𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum malam tanbayana shi
ne ina da miji yanzu a haka 'ya'yanmu 3 amma baya sallah. Ba yadda ban yi ba
idan ya fara sai ya bari amma sallar juma'a baya wuce shi yanzu a haka
mahaifina yace zai yi kararsa ya sake ni tunda baya Sallah to malam in kashe
auren ne ko yaya?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa rahmatullahi
wa barakatuhu.
Tabbas idan har anyi masa nasiha
amma bai ji ba, to bai halatta ki cigaba da zama amatsayin matarsa ba. Domin
kuwa akwai sashen Malaman Musulunci dake ganin cewa ko da sallah guda ce mutum
ya barta da gangan to ya kafirta, balle kuma shi Mijin naki wanda ba ya yin
dukkan sallolin ma in banda Juma'a.
Abin lura anan shi ne tun ranar
da aka daura aurenku aka damƙa masa amanar ciyar dake da tufatar dake, da kuma
koyar dake addini. To Mutumin da shi kansa ba ya yin sallah, ta yaya zai koyar
dake addini?. Ta yaya zai koya ma 'ya'yanku kulawa da muhimmancin sallah?
Cigaba da zama dashi awannan halin zai iya kaiwa zuwa ga lalacewar taki
tarbiyyar ma. Kuma zai wahala bai lalata tarbiyyar yaran naku ba.
Manzon Allah ﷺ Ya ce:
"SALLAH ITA CE GINSHIKIN ADDINI. WANDA YA TSAYAR DA ITA, TO HAKIKA YA
TSAYAR DA ADDINI. WANDA KUMA YA RUSHETA TO HAKIKA YA RUSA ADDINI". Kuma ya
faɗa a cikin wani hadisin wanda Muslim ya ruwaito : "TSAKANIN MUTUM DA
TSAKANIN SHIRKA DA KAFIRCI SHI NE BARIN YIN SALLAH".
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Tambaya Da Amsa Abisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐅��𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
Post your comment or ask a question.