𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mallam ga tambayata kamar haka ya
ya hukuncin matan aurenda take barin tsiraicinta karara amma a gidanta sai
tawuni takwana baruwanta idan miji ya yi magana sai tace itada gidanta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله وحده.
Asali shi ne ya halatta mace
tasanya tufafi agaban mijinta wanda zai bayyanar da al'aurarta gareshi, haka
shima ya halatta ya yi shigar dazata bayyanar da al'aurarsa agaban matarsa,
domin umarnin kiyaye al'aura baya shiga cikin bayyanar da al'aurar ma'aurata ga
junansu atsakaninsu, da abun da damansu tamallaka (kuyanginsu)
Daka mu'awiya bin haidata
Alkushairi ya ce: nace ya manzan Allah Al'aurarmu meya kamata mubayyanar kuma
meya kamata mu kiyayi bayyanar dashi? ya ce: (ka kiyaye al'aurarka saifa ga
matayenka ko kuyanginka) sai ya ce: sai na ce; ya manzan Allah idan kuma
mutanen sashi daya suke fa maza zallah ko mata zallah? sai ya ce: (In za ka iya
kada ka sake kowa yaga Al'aurarka, to ka yi hakan kada ka sake wani yagani) sai
ya ce: sai na ce; ya manzan Allah idan dayanmu yakasance akeɓancefa shi kaɗai? sai
ya ce: Allah shi ne yafi cancanta aji kunyarsa, sama da mutane)
Turmuzi ya ruwaito shi (2794) da
Abu dauda (4017) da ibnu majah (1920) Albani ya ingantashi a cikin sahihul
turmuzi.
Saboda haka abun da take aikatawa
haramun ne idan tana takama gidan tane to ai Allah shi ya fi cancantar aji
kunyarsa sama da mutane kamar yanda ingantaccen hadisi ya nuna dan haka wajibi
ne mijinta ya tsawatar mata ya tashi sosai a kanta har sai tagyara wannan
mummunar al'ada, dan muddin yadauki abun sako sako hakan zai yi tasiri sosai
wajan gurbacewar tarbiyyar 'ya'yansa dama rashin albarka a cikin gidansa, kuma
Shaiɗanu za su yawaita a gidan daman barin al'aura da kazanta a gida da rashin
jin kunyar Allah suke baiwa Shaiɗanu gindin zama a cikin gidan mutum gidan ya
rikice kullum babu kwanciyar hankali.
Amma duk dahaka wannna hadisi
yana nuna mana halaccin wasu ababe kamar haka, yahalatta mace tasanya kananun
kaya ga mijinta, da kuma shara shara waɗanda suke bayyana al'aurarta, da
matsatstsun kayan dasuke bayyana duk wani tudu da loko najikinta ga mijinta,
saboda ya halatta atsakaninsu suga juna tsirara, babu wata hujjah tahana
ma'aurata sanya matsatstsun kayawa junansu damasu shara shara da kananu, saboda
yahalatta suga juna tsirara.
An tambayi malaman lajnatul
da'ima na saudiyya, shin sanya matsatstsun kaya damasu shara shara haram ne ko
halal saboda mace tanayi da nufin yiwa mijinta ado dashi?
Sai suka amsa: Idan mace
takasance tanayin haka ne kawai awajan mijinta yahalatta, idan ba mijinta kawai
take bayyanawa wannan shigar ba bai halatta ba, saboda abun da ke cikin hakan
nabayyana surar jiki, da bayyanar da guraren da ake fitinuwa da mace, Fatawa
lajnatul da'imah (24/34)
Yazo a cikin mausu'a fiƙhiyyah (6/136)
Bai halatta sanya matsatstsun
kaya ba ko shara shara idan yana bayyana al'aura, ta yanda za a iya gane launin
fatar mutum jah ce ko baka ko kasa kasa, da maza da mata duk hukuncin ɗaya ne,
mace ko da a gidan tane bai halatta ta sanya
irin waɗannan kayan ba, idan akwai wanda zai iya ganinta wanda ba mijin taba,
saboda dalilai da suka zo akan hakan, waɗanda suke da alaƙa dahakan, da kuma abun
da ke ciki na zub da mutunci, dakuma saɓawa tafarkin magabata nakwarai, bai
halatta yin sallah da irin wadanan tufafin ba, amma yahalatta mace tasanya shi
idan babu wanda zai gani sai mijinta.
shaik salih Alfauzan hafizahullah
ya ce: bai halatta ga mace tasanya irin wadannan tufafi matsatstsu da masu
bayyanar da surar jiki ko shara shara agaban 'ya'yanta ba, ko muharramanta
saidai abun da al'ada ta gudana akai na yaye abun da babu fitina a cikinsa,
zata sanya sune kaɗai ga mijinta, fatawa shaik salih alfauzaan (3/170).
Duk da haka bai halatta mace tasa
tufafin da maza kaɗai suka keɓanta dasanya suba, ko wanda ya yi kama da yanda
kafirai suke shigarsu.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Tambaya Da Amsa Abisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.