Kamaye

    Yakasai, S. A. & Sani, A-U. (2021). Diwanin WaÆ™oÆ™in Aminu Ladan Abubakar (ALA)Kaduna: Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. ISBN: 978-978-57624-9-0.

    Ado mai Kano mai martaba,

    Ado É—an Bayero mai martaba,

    Na taya murna mai martaba,

    Ka yi naÉ—in sardauna kamai.

     

    Sarki Allah ƙara martaba

    Mai Kano Allah kau da ja’iba,

    ÆŠan Abdu karimi shugaba,

    San kano Sarki mai martaba,

    Ado madubin Shugaba,

    Sadauki marar fargaba,

    Jimrau sa gabanka kai gaba,

    Masallata limamu na gaba,

    Mamu a shige sahun gaba,

    Mai mota direba na gaba,

    Fasinja ba a jira ka ba,

    Ado in da duk ka sa gaba,

    Masoyi ba zai ƙi bin ka ba,

    Na taya murna mai martaba

    Yayi naÉ—in Sardauna kamai

    Mallam Sardauna kamai.

     

    Allah Shi ka aram ma bawa mulki san da ya so Ubangiji,

    San da ya so wanda ya so ga wanda ya so ba wani agaji,

    Kullu Amrullahi Ƙadirun Maƙadurin kun ji ingiji,

    Don haka wannan babu hassada wanda ya ja to zai karairaya.

     

    Ka ƙara salati da amintaka ga Annabi bawan ka Balarabe,

    Mahe Mahmudu Mahe wanda ya sa ƙarya mukarrabe,

    Arabiyyun Ajamiyyun da Inyamuraru da Bayerabe,

    Wanda da zakkowarsa duniya katangun kisra suka rairaye.

     

     

     

     

    Taka sannu da kyau lafiya,

    Ya ÆŠan Bayero mai martaba.

     

    Duƙa sannu da kyau da lafiya,

    Ya É—an mai asali da martaba.

     

    Zauna sannu dakyau da lafiya,

    Ya ɗan mai haƙuri da martaba.

     

    Juya dama da kyau da lafiya,

    Juya haunu ba sa tararka ba.

     

    Ka zama sanɓargon sarakuna,

    In dai ga ka ba za a gan su ba.

     

    Kogi ka cinye kududdufa,

    Ka wuce shinge mai datsar gaba.

     

    Mallam in ka ji doka tambura,

    Ko ka ji kakaki matso gaba.

     

    Taso ga giwar sarakuna,

     Ado Bayero mai martaba.

     

    Sarki na juyo da dundufa taya ka bikin murna na zo in yi,

    Ka yi naÉ—in Sardauna kamai ne bisa tsari da kyauta yi,

    An yi naÉ—in Sardauna Iro ne a kan cancanta da kyauta yi,

    Ado Allah ƙara lafiya babbar giwa ko in ce gini.

     

    Alan waƙa ke ta tambari domin ƙauna ba tanguwa,

    Sarki cancantar ka ta isa in yi yabo ba sai da ilwa,

    In yi kirari har da salsala jikan Dabo ba za na iji ba,

    Ado ÆŠan Bayero San Kano in har ga ka fa babu waiwaye.

     

    Ka yi naɗin Sardauna a Kano Allah riƙa Mallam da martaba,

    Sarki kai sara a kan gaɓa ka naɗa mai kishi na ci gaba,

    Ka naɗa Gwarzo mai karisma mai haƙuri ƙauna ta ci gaba,

    Mallam mai halin a kwaikwaya don haka ne na ƙira shi kamai.

     

     

    Sai na tuno Sardauna Ahmadu mai kishin da ba ai kamarsa ba,

    Sa Ahmadu gwani firimiya mulkin Arewa can shugaba,

    Sa Ahmadu abin da kai mana har a naÉ—e ba a mantaka ba,

    Roƙo na Allah Ubangiji halaiyarsa ka baiwa kamai.

     

    Mai haƙuri mai son ci gaba mai kishi na Arewa can ƙasa,

    Jajirtacce jarimin uba su suka samo ‘yancin Æ™asa,

    Sun mutu don kishin ƙasarmu ne an kakkashe mana jarimin ƙasa,

    Fatana Allahu Rabbana Sardaunanmu ka sa shi yammai.

    Mallam limamun San Kano Sardauna mun sallama maka,

    Allah riƙa ma wagga daraja mu ba mu ja mun yaba maka,

    Allah taya ka riƙo da ɗaukaka halayyarka ta sa a kai maka,

    Tafi dai É—oÉ—ar a gwaddabe babu tsayawa babu waiwaye.

     

    Sakayyar ƙauna akai maka ƙara nutsawa babu jirwaye,

    Tarbiyarka face ta ja maka ƙara nutsawa babu kewaye,

    Gogayyarka face ta ja maka ƙara izawa babu tirji,

    Kamewarka da shi ya ja maka ƙara gaba ka dena waiwaye.

     

    ManaÉ—a sarki suna maka bai’a sun ce eh Allah Æ™ara martaba,

    Kingimeka suni nake nufi sun maka bai’a mai martaba,

    ‘Yan majalisar sarkin Kano sun yi mubai’a babu ja’iba,

    Hakimai cikin jahar Kano sun yi mubai’a mai martaba,

    Hakimai na kewayen Kano sun yi mubai’a mai martaba,

    Bayin sarki na cikin gida miƙa wuya dai babu fargaba,

    Fadawa na sarkin Kano sun yi mubai’a mai martaba,

    Sarakunan Arewacin ƙasa sun yaba kyautar mai martaba,

    Don haka ALA ya taƙarƙare yake baitin murnar da ci gaba,

    Kowa ya bi a yankin Kano an naÉ—a Sardaunanmu kamai.

    Daga Diwanin Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (ALA)

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.