Tallafi

    Yakasai, S. A. & Sani, A-U. (2021). Diwanin WaÆ™oÆ™in Aminu Ladan Abubakar (ALA)Kaduna: Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. ISBN: 978-978-57624-9-0.

    Amshi: Shekara nawa kenan batu na tallafin fetur Nijeriya?

    Ga tuni a gare u shuwagabannin ƙasar yankin Nijeriya,

    Shekara nawa kenan batu na tallafin fetur Nijeriya.

     

    Ɗan mabuɗin waƙar a yau ya zo da istigfari,

    Astagfurullah lillahi wahidun ƙahhari,

    Wa atubu ilaika mai sanya ƙaddarar alkairi,

    Share kukanmu an tsunduma mu halin wayyo bai É—aya.

     

    Mulki na mutane kuma fa ƙirƙira ta mutane,

    Don wasu mutane taken da muka rataya ne,

    Sai ga shi mutanen waÉ—anda an ka wa mulkin ne,

    Sun fito har ƙwansu suna ta ɗuga tutar na-ƙi da na-ƙiya.

     

    Ko ana É—aya an kai zuwa bakwai da ba sauyawa,

    Kuma an yi asarar rayuka da ba mai gawa,

    Kuma an yi asarar lokaci da ba zai zo ba,

    Ba ta sake zani ba sai É—an karen wuya da aka sha tin jiya.

     

    Ashirin ga Janairu Juma’a da ban manta ba,

    Shekara ta dubu biyu da sha biyu da ban yi kure ba,

    Da gari fa ya waye sai Kaduna ban manta ba,

    In da za mu Abuja da zang- zanga dai ta lumanar gaskiya.

     

    Wai ina da wakilai da mun ka dangwalan kuri’armu,

    Wai ina da wakilai da mun ka ce su je madadinmu,

    Wai ina sanatoci cikinmu har da dattijanmu,

    Yan support on motion sun sai da martabarmu idanun duniya.

     

    Muna ta’ajibi muna taraddadi kan haka,

    Ashirin fa ga wata Juma’a da yamma i haka,

    Ina harama ta in je Kaduna babu mushakka,

    Sai na ga hayaƙi garin Kano ya koma duk ya gauraya.

     

     

    Da na dubi sama’i yanayinta ya sauyawa,

    Hargitsi ya gudana ta ko’ina da ka zagawa,

    Go silo ya yawaita kowa yana nufin tserewa,

    Sai na kaÉ—a kaina garin Kano cikin yanayi na Somaliya.

     

    Daga wannan rana sai tattalinmu dukka ya karye,

    Daga wannan rana sai lamarinmu duk suka karye,

    Kasuwa a garinmu middle clerk duka suka karye,

    Tsoro ya shige mu sai fargaba ta aure mu ga tirjiya.

     

    Ko’ina a arewa an kewaye tsaro na tsarewa,

    In ka fito tun safe kafin ka kai gari sai fawa,

    In ka fito ba tabbas ba tabbaci na ka komawa,

    Sallama da iyali muke a yau idan har za mu zagaya.

     

    Sai idan ka dawo cikin gida a yi maka barka,

    Dokar ta-ɓaci ta baibaye mu ta mana sarƙa,

    Mu ko ba mu da ‘yanci maza kama da matan É—aka,

    ÆŠimuwa a jikinmu Allah ka kare yankin Nijeriya.

     

    To ashe arziki muke ciki zama na salama,

    Ka fito in ka so ka so a sa’ilin da ka koma,

    Ka yi sabgoginka ka wataya cikin al’umma,

    Yanzu ba mu da yarda ba mu da izinin shewa sharholiya.

     

    Ga bajet da akan yi na jami’ai dake ta tsaronmu,

    Mafi yawa na kuÉ—inmu ana kashe su ne ga tsaronmu,

    Babu kayan aiki da za su taimaka a tsaronmu,

    Dubi matan Cibok an kwakwashe su bana É“oyen tsinkaya.

     

    Ya Mudabbiru Allah Ubangiji ka kare ƙasarmu,

    Ya Musawwiru Allah ka sauya masu zaluntar mu,

    Yau ruwa ya ci mu ba ma kamar arewa garinmu,

    Addu’a fa nake yi Allah arziÆ™i namu zauna lafiya.

     

     

     

    Duk abin da ake yi kai ne mafi sanin sirrinsu,

    Zahiri da fakenmu Allahu kai ka san motsinsu,

    Dukka masu nufaƙa kai ne mafi sanin kaidinsu,

    Ya masharin kuka ka share dukka matsalar Nijeriya.

    Daga Diwanin Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (ALA)

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.