🔸Babu wasu kwanaki a duniya da suka kai falalar kwanaki goma na farkon watan Dhul Hijja, in ban da dararen goman karshe na watan Ramadhan, kamar yadda wasu malamai suka ce.
🔸Aikin alheri a cikin su ya fi soyuwa, falala da girman
lada a wurin Allah سبحانه وتعالى. Saboda haka su ne kwanakin da suka fi
dukkanin kwanakin shekara falala
🔸 Annabi صلى الله عليه وسلم ya yi umarni a yawaita yin
kabbara (Allahu Akbar) da Hailala (Là'ilàha illallah) da Hamdala
(Alhamdulillah) a cikin wadannan kwanaki masu albarka.
🔸 Ana so a fara yin kabbara tun daga ranar farko na watan
Dhul Hijja. Ana so a dinga yi a masallatai, a cikin gida, a kasuwanni, a kan
hanya, a kitchen da sauran su. Ana so a yi shi a ko da yaushe. Ana so kuma a yi
shi a bayyane.
🔸 Wadannan kwanaki goma masu albarka suna da girma a wajen
Allah سبحانه وتعالى ya kamata mu yi farin ciki da zuwan su, mu ribaci alkhairan
da suke cikin su, mu rayasu da nau'ikan ibada, mu tuba, mu koma ga Allah سبحانه
وتعالى.
🔸 Aikin alheri ya ƙunshi duk abin da Allah سبحانه وتعالى
yake so kuma ya yarda da shi. Saboda haka mu fuskanci wadannan kwanaki da
yawaita yin nafilfili, azumi, karatun Alqur'ani, zikiri da sauran su.
🔸 Kada mu manta cewa shigar da farin ciki a zuciyar
musulmi yana cikin mafi soyuwar aiki a wurin Allah سبحانه وتعالى balle a cikin
wadannan kwanaki masu alfarma.
Allah سبحانه وتعالى
ya nufe mu da aikata abin da yake so, kuma ya yarda da shi. Allah سبحانه وتعالى
ya sa kuma ya zama karbabbe a wajensa cikin rahmarsa.
Copied.
Hukuncin
Azumi Goma A Farkon Zul-Hijja
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalam alaikum Dan Allah mlm mene ne ingancin
azumi Guda goma da ake a watan zulhijja?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumassalam, Hadisi ya tabbata a Sunan
Annasa'i: Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kasance yana azumtar kwanaki
tara na farkon Zul-hijja. Ba a azumtar rana ta goma saboda ita ce ranar sallah,
Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya haramta azumtar ranar sallah a hadisin
da babban sahabi Umar ya rawaito.
Allah ne mafi sani.
Amsawa: Dr Jamilu Zarewa.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
HUKUNCIN
RAMUWA AZUMIN RAMADAN A GOMAN FARKON WATAN ZUL-HIJJA:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Shin ko zan iya yin azumin ramuwa
acikin kwanaki goman farko na watan zulhajji?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam warahmatallahi wabarakatuh
Toh aidama shi wanda ake binsa azumin ramadan cewa
akayi ya ramasu a wasu kwanaki na daban wanda kuma kwanaki goman farkon
zulhijja suma suna cikin jerin kwanaki na daban sannan kuma dama ai cewa akayi
araya waɗannan kwanakin dayin ayyukan alheri toh seki duba kiga
shin rama azumin naki aikin alherine kokuwa sharrine? Idan alherine toh ya
halasta ki rama sannan kuma kuskurenema babba ga wadda ake binta bashin azumin
taje kuma tana raya kwanakin dayin wasu azumin nafila wannan kuskurene babba,
abunda yafi dacewa shi ne a yi azumin ramuwar abaryin nafila ɗin.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.