Ticker

6/recent/ticker-posts

Yaya Ake Sallar Idi?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum malam yaya ake Sallar idi kamar yadda Annabi (S.A.W) ya koyar?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Siffar Sallar idi shine liman yazo ya limanci mutane sallah raka'a biyu. Umar Allah yaqara masa yarda ya ce: Sallar idin qaramar Sallah raka'a biyuce haka Sallar idin babbar Sallah, Ba'a mata Qasaru Abisa harshen Annabinku wanda ya qir-qiri qarya ya jinginata ga Allah da Manzansa ya taɓe.

Nisa'i (1420) da Ibnu kuzaima suka ruwaito Albani ya ingantashi acikin Sahihu Nisa'i.

Daka Abiy Sa'idin Ya ce: Manzan Allah Sallallahu Alaihi wasallam ya kasance yana fita ranar idin qaramar Sallah da babba izuwa wajan Sallah farkon Abunda yake farawa dashi shine Sallah.

Bukhari (956).

A raka'ar farko yana yin kabbarar harama, sannan bayanta yayi kabbara bakwai ko shida, kamar yanda Aisha Allah yaqara yarda da ita ta ruwaito, a idin qaramar Sallah da babba raka'ar farko yana yin kabbara bakwai, araka'a ta biyu kuma yana yin kabbara biyar, banda kabar-barin ruku'u.

Abu dauda ya ruwaito Albani ya ingantashi acikin Irwa'ul galeel (639).

Sannan saiya karanta fatiha ya karanta Suratul "Qaaf" a raka'a ta biyu zai miqe yana mai kabbara idan ya gama miqewa sai yayi kabbara biyar, ya karanta fatiha da Suratul "Iqtarabatissa'ah" waɗannan surori ya kasance yana karantasu a idi biyu, idan ya ga dama kuma a raka'ar farko saiya karanta "Sabbi" a ta biyu " Hal ataka"

Abunda ya Kamata ga liman shine raya Sunnar karanta waɗannan Surori har musulmai su sansu kada suyi inkarinsu idan suka faru Wataran.

Bayan Sallah liman zaiyi khuduba, abunda yafi dacewa shine yake bance wani Abu acikin khudubarsa dazai kebanci mata dashi ya umarcesu da Abunda zasu tsayar dashi na haqqin mazajensu dake kansu, ya hanasu abunda ya kamata su gujeshi kamar yanda Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya Aikata.

Duba Fatawa Arkanul Islma na Shaik Uthaimeen shafi na (398-) da fatawa lajnah (8/300- 316).

Daka cikin Hukunce-hukuncen idi akwai "Sallah kafin Khuduba" saboda hadisin jabir bin Abdullahi ya ce: Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya fito ranar idin qaramar Sallah ya fara yin Sallah kafin khuduba.

Bukhari (958) da Muslim (885) Suka ruwaito.

Wannan shine yanda ake Sallar idi ataqaice.

WALLAHU A'ALAM.

Ga Masu Buqatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗiﺇِﻟَﻴْﻚ

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/CQ9TMXMrWDx1y7sYye2znU

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments