𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam yaya ake Sallar idi kamar yadda
Annabi (S.A.W) ya koyar?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Siffar Sallar idi shine liman yazo ya limanci mutane
sallah raka'a biyu. Umar Allah yaqara masa yarda ya ce: Sallar idin qaramar
Sallah raka'a biyuce haka Sallar idin babbar Sallah, Ba'a mata Qasaru Abisa
harshen Annabinku wanda ya qir-qiri qarya ya jinginata ga Allah da Manzansa ya
taɓe.
Nisa'i (1420) da Ibnu kuzaima suka ruwaito Albani ya
ingantashi acikin Sahihu Nisa'i.
Daka Abiy Sa'idin Ya ce: Manzan Allah Sallallahu Alaihi
wasallam ya kasance yana fita ranar idin qaramar Sallah da babba izuwa wajan
Sallah farkon Abunda yake farawa dashi shine Sallah.
Bukhari (956).
A raka'ar farko yana yin kabbarar harama, sannan bayanta
yayi kabbara bakwai ko shida, kamar yanda Aisha Allah yaqara yarda da ita ta
ruwaito, a idin qaramar Sallah da babba raka'ar farko yana yin kabbara bakwai,
araka'a ta biyu kuma yana yin kabbara biyar, banda kabar-barin ruku'u.
Abu dauda ya ruwaito Albani ya ingantashi acikin Irwa'ul
galeel (639).
Sannan saiya karanta fatiha ya karanta Suratul
"Qaaf" a raka'a ta biyu zai miqe yana mai kabbara idan ya gama miqewa
sai yayi kabbara biyar, ya karanta fatiha da Suratul
"Iqtarabatissa'ah" waɗannan surori ya kasance yana karantasu a idi
biyu, idan ya ga dama kuma a raka'ar farko saiya karanta "Sabbi" a ta
biyu " Hal ataka"
Abunda ya Kamata ga liman shine raya Sunnar karanta waɗannan
Surori har musulmai su sansu kada suyi inkarinsu idan suka faru Wataran.
Bayan Sallah liman zaiyi khuduba, abunda yafi dacewa
shine yake bance wani Abu acikin khudubarsa dazai kebanci mata dashi ya
umarcesu da Abunda zasu tsayar dashi na haqqin mazajensu dake kansu, ya hanasu
abunda ya kamata su gujeshi kamar yanda Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya
Aikata.
Duba Fatawa Arkanul Islma na Shaik Uthaimeen shafi na
(398-) da fatawa lajnah (8/300- 316).
Daka cikin Hukunce-hukuncen idi akwai "Sallah kafin
Khuduba" saboda hadisin jabir bin Abdullahi ya ce: Annabi Sallallahu
Alaihi wasallam ya fito ranar idin qaramar Sallah ya fara yin Sallah kafin
khuduba.
Bukhari (958) da Muslim (885) Suka ruwaito.
Wannan shine yanda ake Sallar idi ataqaice.
WALLAHU A'ALAM.
Ga Masu Buqatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗiﺇِﻟَﻴْﻚ
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/CQ9TMXMrWDx1y7sYye2znU
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.