𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam ina da tambaya ni ce tun bayan dana haihu na gama jini ban kuma yin jini ba Sai jiya kuma ban gan shi kamar yanda na saba gani ba, to abin tambayar shi ne zan iya daukan azumi ko kuwa? Na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Eh ya wajaba ki dauki azumi Domin kamar yadda tambayarki ta nuna ba jinin
haila kika gani ba Shi kuma azumi da sallah ba'a dena su har sai idan asalin
jinin hailar ne yazo sabida hukuncin dakatar da ibada yana ratayuwa ne da ganin
jinin haila ba kowane jinine idan mace tagan shi yake zama na haila ba musamman
Idan ba a cikin kwanakin hailar yazo ba, Sabida haka idan mace taga jini kuma
ya canza daga asalin jinin hailarta to matukar dai ba a tsakiyar hailarta ko ƙarshen hailar tagan shi ba, Bazata daukeshi a matsayin
haila ba.
WALLAHU A'ALAM
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwa a
Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.