Ticker

6/recent/ticker-posts

Tafiya Ta Kama Ni A Tsakiyar Yini, Ko Zan Iya Karya Azumina?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Mutum ne zai je Umara cikin Azumi, sai ya zama jirginsu zai tashi ƙarfe biyu na ranar, shin zai kame baki ne daga safe zuwa lokacin tashin ko kuwa ba zai yi Azumi ba kwata-kwata a ranar?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikum assalam. Zancen mafi yawan Malaman Hanafiyya da Malikiyya da Shafi'iyya shi ne: Idan mutum ya yi tafiya a tsakiyar yini, to ba zai ci abinci ba, sai dai idan ya shiga wahalar da ba zai iya jurewa ba. Amma a wajan Malaman Hanabila ya halatta, saboda Allah ya halattawa matafiyi cin abinci a suratul Baƙara kuma bai bambanta tsakanin wanda ya yi tafiya a farkon yini ba da wanda ya yi a tsakiya.

Don neman ƙarin bayani duba: Al'insaf, 3/205

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwa  a Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/IƘUc0RxgCwA3JFiEKl8j5E

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments