USMAN IBRAHIM BULANGU
09064862386
BISMILLAHIR RAHMANIR-RAHIM
01. Da sannu-sannu na zo na fara dai ku ji,
Na dake na dage babu mai mini agaji,
Shi sha'iranci ba a yi masa kwaf-ɗaya
02. Ni na kasance mai yawan yin bincike,
Ilimi nake nema kamar me dunduke,
Don kad da dai kaina ya zam na Ƙififiya
03. Ni Shehina Malam Ƙani shi ne ya san,
Kishi na
harshe na ya ce kai dai ka san,
Harshenka ya wuce yadda-shi-ɗauko-haya
04. Nukuɗa da dama sai ya
feffeɗe mini,
Asali na kalmomi tsatsaf ya gaya mini,
Har ma da tarihin Bahaushe ɗan jiya
05. Ƙa'ida ta waƙa duk ya suranta mini,
Taza-da-tsifa duk a kanta ya yi mini,
Waƙa ta Hausa har da ma ta Arabiya
06. Na ɗauki niyyar yi
da gaske a hankali,
Jifa da Kansakali na sa yo Kwalkwali,
Ɗamara ta waƙa nas saka ƙololiya
07. Dukufa na yi nazari nake na tsabbace,
Wallafar mazan jiya bi-da-bi na taskace,
Domin na dace kar na yo kandarariya
08. Abokanai ko waɗansu in suka ganni sai,
Su ɓuge da kyarata
kamar Ƙwaron masai,
Wai ga Mawaƙi wassu nai mini zolaya
09. Daga na yi honƙoron na ma wai kare kai,
Sai su barni wofi kai su ma dai kauda kai,
Sun ga mai sana'a o'e wofantacciya
10. Da kaɗan idan na yo
suke yin marmari,
Haka nan ta zaga kan tudu har ma kwari,
Na fitar da Diwanin Madubin Duniya
11. In na yi sai in kaiwa malumma su ji,
Har ma Furofesa na kai masa dan gwaji,
Don dai su sa ni a godaben bin gaskiya
12. Na Gusau Furofesa ya ce waƙar da kai,
Tsaf ta yi daɗi ba ko wai dan dai da kai,
Yi faɗi na sunana,
kawai dan gaskiya
13. Dakta Gabari ya ce kaje maza kai ta yi,
Domin ko
jari ce watan-wata-rana yi,
Kar kai sake kan mauhibar ka ka jiya
14. Af! na yi waƙoƙi akwai Masa'uliyya,
Nai ta
Manzo na yi har da Matashiya,
Ga nan ta Alƙalami da Ƙalwaiwainiya
15. Da diri na ɗango har da ma dai yan ɗiya,
Da ado na harshe har da ma dai ƙafiya,
Na kanannaɗe su a wallafa
ta Ƙarangiya
16. Sau sassaƙar saƙar ka sauƙe sassaƙe,
Saƙon saƙaƙa saƙe-saƙe su sarƙaƙe,
Sarƙarsa sunƙuru siƙe surƙuƙƙiya
17. Gorin ki Kaska gun su Babe kan jini,
Ina ko ke
ki ka samu naki gaya mini,
Kin huda kanki garin ki feɗe wutsiya
18. Kura ko wane za ya baki riƙon gari?
Su Kare ki ja su ki kai ki sa su a haɗari,
Tumuna a ce an bawa Kura tsangaya
19. Na yo Salatai gun Rasulu abin biya,
Har Alihi na gidansa dukka a gauraya,
As'habu tare da su akai ta ɗawainiya
20. Hamdan kasiran ɗayyiban ya Rabbana,
A gare Ka ni Usman Bulangu ga ko ana,
Tutur! a kowasshe inai ma Ka godiya.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.