𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum mallam, Ina mura Na sha magani kuma Ina
da niyyan daukar azumi, sakamakon maganin I wake up late 5:00 daidai na falka,
sai na yi amfani da 5 minites na ci abinci, wato 5:05 ke nan mallam ya matsayin
azumina?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam, ƴar uwa matuƙar lokacin da mutum ya ci abincin sahur Alfijir na
gaskiya ya keto koda da minti ɗaya ne, to ba shi da azumi, sai ya rama wannan azumin.
Amma idan daidai ƙarfe biyar ɗin nan Alfijir na
gaskiya bai riga ya keto ba, to azuminki ya inganta, in kuwa Alfijir na gaskiya
ya riga ya bayyana ko da kuwa da minti ɗaya ne, to lallai ba ki da azumin wannan yinin.
Allah S.W.T ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare
Da Fadakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Bvk6LLvY9evDZHXFMZCzeU
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.