Ticker

6/recent/ticker-posts

Mene ne hukuncin wanda ya je sallar tahajjud bai samu sallar asuba ba?

 𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Malam tambayata ita ce, miye hukuncin wanda ya je sallar tahajjud bai samu sallar asuba ba?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

To wannan kuma idan dagewa tsayuwar dare da rasa sallar asubahi shi ne dabi'arsa to lallai yakamata a jajanta masa domin kuwa yana yin babbar hasara sabida nassoshi ingantattu sun tabbatar cewa Duk wanda ya samu Sallar asubahi a cikin jam'i To kamar ya kwana yana sallah a wannan daren ne. Sayyadina umar Allah ya kara masa yarda cewa yayi: ya halarci sallar asubahi a cikin jam'i shi ne ya fi masa soyuwa ya kwana yana sallar dare.

Sabida haka sallar dare idan ka cire sallar farillah babu sallar da tafi ta kuma yana daga mafi soyuwar ayyukan manzon Allah sabida haka tana da matukar muhimmanci kwarai dagaske. Amma kuma idan mutum ya mayar da dabi'arsa tsayuwar dare Amma kuma baya samun sallar asubahi cikin jim'i to wannan kuma yana sakaci sabida gwara a ce ya kwana yana bacci Amma kuma ya samu sallar asubahi a cikin jam'i

WALLAHU A'ALAM

Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwa a Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Bvk6LLvY9evDZHXFMZCzeU

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments