Ticker

6/recent/ticker-posts

Mene Ne Khul'i A Musulunci?

 Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Ma'anar Khul'i shi ne mace ta fanshi kanta daga gurin mijinta, ta ba shi sadakinsa da ya biya a lokacin da ya aure ta.

 Kamar yadda hakan ya zo a hadisi wanda hakan ya taɓa faruwa a tsakanin ɗaya daga cikin Sahababan Manzon ALLAH {s.a.w} da matarsa.

 Ya halatta a musulunci mace ta biya mijinta sadakinsa daya ba ta a lokacin daya aureta idan har bazata iya zama da shi ba, ko ba ta sonshi, ko yana mata wasu abubuwa da bataso anyi sulhun anyi sulhu amma bai daina ba, to ya halatta ta yi masa Khul'i kamar yadda ya zo a cikin Suratul Bakarah ayata 229.

 Sannan khul'i yana daukar hukuncin saki ɗaya ne tak, sannan kuma idan anyishi ba'ayin kome sai dai tsohon mijin nata ya sake biyan sabon sadaki sannan sai a ɗaura musu sabon aure.

ALLAH shi ne mafi sani.

ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

Post a Comment

0 Comments