Ticker

6/recent/ticker-posts

Ramuwar Azumin Farilla A Shari'a

 Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Salam shin ya alatta mutum ya ringa skipping ya yin yin rankon azummi? Misali kana yin shi Litinin da alhamis kuma ranko ne?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumussalaam Wa Rahmatullahi Wa Barakaatuh.

Babu laifi a kan hakan shi ne abin da mafi yawancin mallamai suka tafi a kai wanda yake da ramuwa na azumin Ramadan ya yin da zai rama su, ba dole sai ya yi su a jere ba, saboda faɗin Allah (SWT):

(فمن كان منكم مريضا أو على سفر فعدة من أيام أخر)

Wanda ya kasance daga cikin ku bashi da lafiya ko a hali na tafiya to sai ya biya adadin a cikin wasu kwanuka na dabam.

 

-Haka an ruwaito daga Aisha Allah Ya kara mata yadda tace da an saukar da àyar

 

(فعدة من أيام أخر متتابعات)

 

Sai aka goge kalmar (متتابعات)

 

-Haka an ruwaito hadisi daga Abdullahi binu Umar (RTA) Ya ce manzon Allah(SAW) yace:

 

(أن النبي صلى الله عليه وسلم قال في قضاء رمضان إن شاء فرق وإن تابع)سنن الدارقطني.

 

Manzon Allah(SAW) ya ce: Wanda yake da ramuwa na azumi idan ya so ya yi su a jere idan ya so ya yi su a rarrabe.

 

والله تعالى أعلم.

 

DR, NASIR YAHYA ABUBAKAR BIRNIN GWARI

 

Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwa  a Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/BJikpGm7VXV1vEVVGcNH5J

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Post a Comment

0 Comments