Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Sanya Turare Ga Mace A Addinin Musulunci

Daga Ubaidu ya ce:

Lallai Abu Hurairata (R.A) Ya haɗu da wata mata wacce ta sanya Turare, sai Ya ce Mata:

 Ina kike son zuwa ne haka baiwar ALLAH?

Sai matar ta ce: Masallaci zanje.

Sai ya ce:

Saboda za ki je masallacin ne kika sanya turare?

 Sai matar ta ce: eh.

Sai Abu Huraira (R.A) ya ce:

 Lallai ni na ji Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce:

 Duk matar da ta sanya turare ta fita da nufin zuwa masallaci, to ALLAH TA'ALAH ba zai karɓi sallarta ba har sai ta dawo ta yi wanka Irin wankan Janaba.

[Ibn majah 4002].

 Ɗaya daga cikin malaman musulunci ya ce:

 Idan har sanya turare saboda zuwa masallaci ya zama haramun ga mace, to ya ake tunanin hukuncinsa zai kasance a kan wacce ta sanya shi domin…

************************************** 

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments