𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum wa rahmatullah ina ma mallam fatan alheri, mallam Tambaya kamar aka, ya dace magidanci ya bar matansa da ya'yansa suna yawo da gyele. Mallam shin bashi da laifi idan ya kasance shi ya ƙoƙarin bin sunnah aman su bai hana su saka gyale ba sobada ba a ko da yaushe suke fita da gyale ba shin hakan ya dace? jazakumullahu khair
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuh.
Alhamdu lillahi rabbil alamin wassalatu wassalamu ala rasulillah wa ala alihi
wa sahbihi ajma'in.
Gaskiya bai dace ga magidanci ya zamo kan shiriya,
sunnah, amma iyalinsa da yaransa a kan bidi'a da saɓon Allah, domin amana ne
Allah ya damƙa a hannunsa kuma ya ce ya
kula da su ya tseratar da su daga wuta. Ba an ce ya yi ta kansa ba ne shi kaɗai, bar saura ko oho.
(یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ قُوۤا۟ أَنفُسَكُمۡ وَأَهۡلِیكُمۡ نَارࣰا وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُ عَلَیۡهَا مَلَـٰۤىِٕكَةٌ غِلَاظࣱ شِدَادࣱ لَّا یَعۡصُونَ ٱللَّهَ مَاۤ أَمَرَهُمۡ وَیَفۡعَلُونَ مَا یُؤۡمَرُونَ)
[Surah At-Tahrim 6]
Ya sani cewa gobe ƙiyamah ba zai kuɓuta a gaban Allah ba, sai ya
yi bayani kan amanar da aka bashi. Allah ya ce mu umarce iyalan mu da su yi sallah,
Annabi ya ce a duke su idan ba su yi sallah ba a shekara goma. Allah ya ce
(وَأۡمُرۡ أَهۡلَكَ بِٱلصَّلَوٰةِ وَٱصۡطَبِرۡ عَلَیۡهَاۖ لَا نَسۡـَٔلُكَ رِزۡقࣰاۖ نَّحۡنُ نَرۡزُقُكَۗ وَٱلۡعَـٰقِبَةُ لِلتَّقۡوَىٰ)
[Surah Ta-Ha 132]
Annabi sallallahu alaihi wa sallama Ya ce
5866 - «مروا أبا بكر فليصل بالناس».
(صحيح) [حم ق ت هـ] عن عائشة... [ق] عن أبي موسى... [خ] عن ابن عمر... [هـ] عن ابن عباس وسالم بن عبيد. فقه السيرة 499، الإرواء 541.
Bayan haka, Annabi ya ce mai rashin kishin iyali, yara
mata, ko yan'uwa mata, ba zai shiga aljanna ba, Annabi ya ce mutane uku
ba su shiga aljanna, mai saɓa ma iyaye, daiyus da macen
da ke kama da maza
3063 - «ثلاثة لا يدخلون الجنة: العاق لوالديه والديوث ورجلة النساء».
(صحيح)... [ك هب] عن ابن عمر. حجاب المرأة المسلمة ص 67: حم، الضياء.
A nan nake so na jawo hankalin mata musulmi, su gane
cewa, hijabi, addini ne, ibadah ce, Allah ne ya umarce su da shi. Allah ya fara
da Annabi ne sannan aka zo ga sauran muminai, Allah Ya ce
(یَـٰۤأَیُّهَا ٱلنَّبِیُّ قُل لِّأَزۡوَ ٰجِكَ وَبَنَاتِكَ وَنِسَاۤءِ ٱلۡمُؤۡمِنِینَ یُدۡنِینَ عَلَیۡهِنَّ مِن جَلَـٰبِیبِهِنَّۚ ذَ ٰلِكَ أَدۡنَىٰۤ أَن یُعۡرَفۡنَ فَلَا یُؤۡذَیۡنَۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورࣰا رَّحِیمࣰا)
[Surah Al-Ahzab 59]
Daga ƙarshe saka gyale ba laifi ba
ne idan zai rufe dukkan jiki, yana da kauri, babu ado, bai kama da na kafirai
ba, ba mai ɗaukar ido ba, ma'ana dai idan ya cika sharuɗɗan hijabi.
Wallahu ta'aala a'alam.
Amsawa:
Malam Aliyu Abubakar Masanawa
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Eub2uLrV18T4vHJcƙRDkPZ
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.