𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Aslm Alaikum Mlm na kasance ina yin Azumin litinin da Alhamis duk sati. Jiya litinin bayan na sha ruwa sai yarinyata take cemin wai ba kyau yin Azumi idan Ramadan ya kusa sai na ce mata har na Nafila sai ta ce min wai eh. Dan Allah meye gaskiyar wannan maganar. Bissalam ALLAH ya taimaki mlm.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salaam Warahmatallahi Wabarkatahu
Manzon Allah S.A.W Ya ce: "Kada Dayan ku ya yi
Azumin Kwana Ɗaya Ko Biyu, Idan Ya zama
Daf Da Ramadana, Sai dai Idan Mutum Ya Saba Yana Yin Wani Azimin sa, To Shi Ya
Halatta ya yi.
Bukhari.
➡️Ma'ana Sai Idan Ya Dace Da Wani Azumi Mutum Ya Saba
Yi, Kamar Azumin Nafila, Ko Litinin Da Alhamis Da Azumin Annabi Dawud, ka yi Yau,
Gobe Ka Huta, Ko Azim Kwana 3 A Kowanne Wata, Dan Haka Hanin Ya Shafi Wanda Ba
Ya Yin Waɗannan Ne.
WALLAHU A'ALAM
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BD0aB20SWTB9hgHahFHb9M
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.