Rubutun Novels ya kasu gida uku:
1• Akwai wanda yake haram ne gaba ɗayansa, saboda irin saƙonnin da ke cikinsa sun saɓawa Alƙur'ani da sunnah.
Kamar littafin da yake ƙunshe da kalmomi na shirka da kuma da suke raba kan musulmi dama al'ummar baki ɗaya.
Kuma suna kimsa
rasahin zaman lafiya a tsakanin ma'aurata ko suke raba kishiyoyi suna kuma raba
iyaye da yaransu, harma wasu suna nuni da yadda ake bin malaman tsubbu da
bokaye da sauransu, to irin wannan littafin kwata-kwata haramun ne.
2• Akwai wanda yake ɗauke wani sashinsa akwai ɓarna wani sashin kuma yana
amfanarwa, kamar litattafan da ke ƙunshe da bayanai a kan mene
ne aure da kuma zaman aure da kuma wasu hanyoyi da za abi domin kyautata
zamantakewa a tsakanin miji da matarsa harma da abokiyar zamanta.
Amma kuma wani
sashin nasa yana ɗauke da kalmomi na batsa wanda hakan yana jefa mai
karatu a cikin damuwa musamman idan waɗanda basuda aure suna
karantawa sai su sami kansu cikin motsawar sha'awa wanda hakan yana kai ga wasu
su fara istimina'i wasu kuma su afkawa zina ko maɗigo.
To irin wannan
littafin akwai buƙatar ya zama antaceshi aya
yin rubutu, kuma mai rubutun ya kiyaye Haƙƙoƙin ALLAH a cikin rubutunsa, kada ya rubuta abin da zai jawo
masa zunubi a gaban ALLAH.
3• Akwai littafin da yake dukkansa halal ne, kamar
irin wanda ke ƙunshe da bayanai wanda
wasunsu an cirosu ne daga Alƙur'ani da Hadisai
ingantattu.
Wasu bayanan
kuma suna ƙunshe da hikima da nasiha da
kuma labarai na magaba ta na ƙwarai domin a koyi darussa
daga irin rayuwarsu kuma a koyar da masu zuwa a bayan-baya.
Sannan kuma
suna koyar da yadda mutum zai rayu cikin aminci suna nuni da illolin ha'intar
miji ko ƙawa ko aboki ko wanin haka.
Suna kuma nuni
da sakamakon mai aikata wani aiki mara kyau da yadda ƙarshensa ke ƙarewa, wanda kuma ya yi haƙuri ya bi ALLAH da Manzon ALLAH {s.a.w} yakan sami
sakamakonsa mai kyau dadai sauransu.
Saboda haka
ire-iren waɗannan littattafan suna da kyau, domin ta hanyarsu ana
samun al'umma na gyaruwa, sannan kuma akwaisu a cikin yare iri-iri, kamar
Larabci ko ingilishi ko Faransanci ko Hausa.
Mafi kyawun
littafi mai ɗauke da gaskiyar zance shi ne Alkur'ani da Hadisan
Manzon ALLAH {s.a.w} sai dai muna wani zamani wanda ba kowa ke iya buɗe Alkur'ani ko Hadisi ya
bibiyi hukuncin ALLAH a cikinsu ba,
Amma kuma
mutane na iyabxaman karanta Novels, shi ya sa idan aka ciro bayanan aka saka a
cikin littattafan Novels aka faɗaɗa bayanai, kuma aka yisu
cikin harshen da mai karatu zai fahimci saƙon da ke cikinsu, to mai
karatu zai zauna ya yita bibiyar abin da ke cikin wannan littafi ba tare da
gajiya ba, kuma maribucinsa zai sami lada, mace ko namiji.
ALLAH TA'ALAH ka sa mu dace, ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
Rubuta tsokaci.