Ticker

6/recent/ticker-posts

Amarya Wai Ba Ta Iya Bacci Ita Kaɗai A Daki

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Tambayoyi Da Amsoshi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Aslmk mal Allah ya kara lfy, mal mutum ne ya yi amarya to sai ta zo da wani salo wai ita ba ta iya bacci ita kaɗai sai da mutum a dakin, sai ta yi ihu wai tana firgita saidai azo falo a zauna indai ba ranar kwananta ba ne, to shi ne mijin ya yanke shawara cewa dukkansu za su ringa kwana a dakin, shi kawai Amma za a kashe wuta kar wata ta ga tsaraicin wata malam hakan ya hallarta.

𝐀𝐌𝐒𝐀👇

Wa'alaikumus salam Warahmatallahi Wabarkatahu

 Da a ce shi ne ya Nemi Shawara sai Ince masa. Abin da ya Kamata shi ne, ya Samar Mata Wadda za ta ke taya ta Kwana Idan ba a dakinta yake ba. Amma idan a dakinki yake bai kamata a yi haka ba. Sabida babu Nutsuwa gaskiya. Ma'ana idan yana dakinta za su kwanta tare, Sabida ta sami Wanda za su Kwana tare. Mijinta ke nan. Idan kuma yana dakinki sai ta zo Ku kwana tare a dakinsa. Sabida na san Nan Gaba za su zo Miki da Wannan Tsarin. Idan har Sun Latsa sun ga Ta kai Musu. Amma duk da Haka Ki Bashi Shawara ya Samar mata wadda zatake taya ta Kwana. Ko da yarinyarki ce tana taya ta Kwana. Ko kuma daga Makotanku ne ko wata Yar'uwarsa ko kuma Yar'uwarta. Amma Rabon Kwana Wajibi ne ga wanda yake da Macen da ta Wuce guda daya.

 

Allah shi ne Masani.

 

Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/BD0aB20SWTB9hgHahFHb9M

 

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Post a Comment

0 Comments