𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne Hukuncin Cinye Naman Layya Duka, Ko Sadaka Da shi Gaba Ɗaya?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Nassoshi Na shari'a sun yi nuni a kan wajabcin yin sadaka da Wani abu na naman layyah, koda kaɗan ne, Allah maɗaukakin sarki ya ce: (Kuci daka naman layyarku, ku ciyar da Talakan daya kame bai roqa ba, da talakan daya roqa saboda buqata, saboda haka Allah ya Yassare muku ita danku zama masu godiya) Suraul Hajji aya ta (36).
Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: ( Kuci naman layya, ku ajiye, kuyi sadaka) Muslim (1971).
Malaman da Suka ce yin sadaka da Naman layya wajibine sune: Shafi'iyyah da Hanabila, Itace sahihiyar Magana Azahirin nassosin shari'a.
Wajibine sadaka da wani abu na naman wanda sunan sadaka zai gaskatu akansa, domin manufa shine yalwatawa miskinai,
Abisa Wannan idan mutum ya cinye naman layyar sa, duka wajibine ya siya yayi sadakar,
Rauzatul dhalibeen da Umdatul mufteen (3/223).
Kamar yanda Marudy ya faɗa acikin "Al'insaaf (6/491).
Kamar yanda Buhty yafada acikin kashshaful Qina'i (7/444).
Kamar Yanda Shaik Usaimeen ya bayyana acikin Maj-mu'u fatawa dinsa (25/132)
Malamai Sunyi Saɓani akan wajabcin cin wani abu daga cikin Naman layya, Jamhur ɗin malamai suna ganin cin wani Abu na naman layya mustahabbine, ba dole bane, wannan shine fatawar Manyan Mazhabobinnan guda huɗu.
Wasu sun tafi akan wajabcin cin wani Abu daka cikin naman layya koda kaɗan ne, saboda zahirin nassosin shari'a da sukayi Umarni akai.
Nawawi ya ce: Cin naman layya mustahabbine ba dole bane, shine mazhabar mu da Malamai gaba ɗaya, sai Abunda aka hakaito daka wasu magabata na wajabcin cin naman, saboda zahirin hadisin dayayi Umarni aci wani abu daga layya, da faɗin Allah maɗaukakin Sarki ( Kuci daka naman layya) Jamhur ɗin malamai sun dora wannan umarni akan halacci da Mustahabbanci,
Sharhin Sahihu Muslim (13/131).
Ibnu qudama ya ce: da Mutum zaiyi sadaka da naman layya gaba ɗaya, ko mafi yawan naman, ya halatta.
Al-mugni (13/380).
Idan ka yanka raguna da yawa, ko wanne saika debi wani abu daka namansa kayi Sadaka da shi.
da Zaka yanka raguna goma ko akuyoyi ko tumaki, ko wanne daka cikinsu saika debi namansa kayi Sadaka da shi, mustahabbine kowacce dabba kaci wani Abu na naman dukkan dabbobin daka yanka.
Domin kowacce layya cin gashin kanta take..
Shi yasa da Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya soke abun hadayarsa sai yayi umarni a debo masa wani kaso daka naman kowacce raquma.
Jabir ɗan Abdullahi Allah ya qara musu yarda ya ce: Sai muka nufi Abbatuwa Annabi ya Soke raquma talatin da Uku da hannunsa, sai ya bawa Aliyu ya yanka Abunda yayi Saura.
Sannan yayi Umarni akawo masa daka naman kowacce sai aka sanya atukunya aka dafa masa yaci namansu, yasha romonsu.
Mualim (1218).
Wannan yana nuna kowacce dabbar layya da'aka yanka tana da hukunci nata ita kaɗai.
saboda hakane yayi Umarni akawo masa wani Abu daka kowacce taguwa.
Nawawi ya ce: acikin wannan akwai mustahabbancin cin hadayar nafila, da layyya.
Malamai Suka ce: cin naman kowacce dabba daka yanka sunnah ne, cin yanka ɗaya na kowacce dabba akwai wadatarwa, ka sanya atukunya don kowacce ya zama akwai romon nata naman.
Sharhin Muslim (8/192).
Wallahu A'alamu.
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan kwarai.
HUKUNCIN
WANDA YA CINYE NAMAN LAYYA DUKA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam. Mene ne Hukuncin Cinye
Naman Layya Duka, Ko Sadaka Dashi Gaba Ɗaya?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam warahmatallahi wabarakatuh.
Nassoshi Na shari'a sun yi nuni akan wajabcin yin
sadaka da Wani abu na naman layyah, koda kaɗan ne, Allah maɗaukakin sarki ya
ce:
...فَكُلُوا مِنْهَا وَأَطْعِمُوا الْقَانِعَ وَالْمُعْتَرَّ كَذَٰلِكَ
سَخَّرْنَاهَا لَكُمْ لَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ
Kuci daka naman layyarku, ku ciyar da Talakan daya
kame bai roqa ba, da talakan daya roqa saboda buqata, saboda haka Allah ya
Yassare muku ita danku zama masu godiya. (Suratul Hajji aya ta 36).
Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: ( Kuci
naman layya, ku ajiye, kuyi sadaka) Muslim (1971).
Malaman da Sukace yin sadaka da Naman layya wajibi
ne sune: Shafi'iyyah da Hanabila, Ita ce sahihiyar Magana Azahirin nassosin
shari'a.
Wajibi ne sadaka da wani abu na naman wanda sunan
sadaka zai gaskatu akansa, domin manufa shi ne yalwatawa miskinai.
Abisa Wannan idan mutum ya cinye naman layyarsa
duka wajibi ne ya siya yayi sadakar, Rauzatul dhalibeen da Umdatul mufteen
(3/223).
Kamar yanda Marudy ya faɗa acikin "Al'insaaf (6/491).
Kamar yanda Buhty yafada acikin kashshaful Qina'i
(7/444).
Kamar Yanda Shaik Usaimeen ya bayyana acikin
Maj-mu'u fatawa dinsa (25/132).
Malamai Sun yi Saɓani akan wajabcin cin wani abu daga cikin Naman layya,
Jamhur ɗin malamai suna ganin cin wani Abu na naman layya
mustahabbine, ba dole bane, wannan shi ne fatawar Manyan Mazhabobinnan guda huɗu.
Wasu sun ta fi akan wajabcin cin wani Abu daka
cikin naman layya koda kaɗan ne, saboda
zahirin nassosin shari'a da sukayi Umarni akai.
Nawawi ya ce: Cin naman layya mustahabbine ba dole
bane, shi ne mazhabar mu da Malamai gaba ɗaya, sai Abunda
aka hakaito daka wasu magabata na wajabcin cin naman, saboda zahirin hadisin
dayayi Umarni aci wani abu daga layya, da faɗin Allah maɗaukakin Sarki (
Kuci daka naman layya) Jamhur ɗin malamai sun
dora wannan umarni akan halacci da Mustahabbanci, Sharhin Sahihu Muslim
(13/131).
Ibnu qudama ya ce: da Mutum zaiyi sadaka da naman
layya gaba ɗaya, ko mafi yawan
naman, ya halatta. Al-mugni (13/380).
Idan ka yanka raguna da yawa, ko wanne saika ɗebi wani abu daka namansa kayi Sadaka dashi.
da zaka yanka raguna goma ko akuyoyi ko tumaki, ko
wanne daka cikinsu saika ɗebi namansa kayi
Sadaka dashi, mustahabbine kowacce dabba kaci wani Abu na naman dukkan dabbobin
daka yanka.
Domin kowacce layya cin gashin kanta take.
Shi yasa da Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya
soke abun hadayarsa sai yayi umarni a ɗebo masa wani
kaso daka naman kowacce raquma.
Jabir ɗan Abdullahi
Allah ya qara musu yarda ya ce: Sai muka nufi Abbatuwa Annabi (Sallallahu
alaihi Wasallam) ya Soke raquma talatin da Uku da hannunsa, sai ya bawa Aliyu
ya yanka Abunda yayi Saura. Sannan yayi Umarni akawo masa daka naman kowacce
sai aka sanya atukunya aka dafa masa yaci namansu, yasha romonsu. Mualim
(1218).
Wannan yana nuna kowacce dabbar layya da'aka yanka
tana da hukunci nata ita kaɗai.
saboda hakane yayi Umarni akawo masa wani Abu daka
kowacce taguwa.
Nawawi ya ce: acikin wannan akwai mustahabbancin
cin hadayar nafila, da layyya.
Malamai Sukace: cin naman kowacce dabba daka yanka
sunnah ne, cin yanka ɗaya na kowacce
dabba akwai wadatarwa, ka sanya atukunya don kowacce ya zama akwai romon nata
naman. Sharhin Muslim (8/192).
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.