𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam matata ta yi rashin lafiya, da aka gwada ta, sai aka ce tana da cutar aids, ni kuma an gwada ni amma an ce ba ni da ita, Sannan an gwada ragowar matana, suma an samu ba su da ita, gaskiya malam ina so zan sake ta, saboda kar ta shafe mu, amma ina neman shawara?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
To dan’uwa
cutar aids tana daga cikin cututtuka sababbi, waɗanda
ba a tattauna su ba a manyan kundayen musulunci, sai dai idan muka duba manufar
da ta sa aka shar’anta saki wato tunkude cuta da matsala, daga daya daga cikin
ma’aurata ko su duka, za muga ta tabbata a wannan cuta, tun da ilimin likitanci
ya tabbatar da cewa cuta ce mai haɗari
kuma ana daukarta, don haka ya halatta ka sake ta, saboda wannan dalilin, tun
da malaman Fikhu sun halatta raba aure saboda cutar kuturta, kamar yadda hakan
ya zo a Minahul Jalil Sharhu Muktasarul Khalil: 6\478 Cutar Sida kuma tafi
kuturta tsanani. Sannan ba za a kalli cutuwar da za ta yi ba, bayan an saketa,
domin yana daga cikin ka’idojin Sharia: kau da kai daga tunkude cutar da za ta
shafi wani saboda cutar da za ta game, Cigaba da zama da ita zai jawo ka dauki
cutar, kuma iyalanka su dauka, wannan ya sa ba za a waiga zuwa damuwarta ba a
nan wurin.
Allah ne mafi
sani.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBƙfaiPwf28l
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.