Ticker

6/recent/ticker-posts

Ta Yaya Zan Gyara Zuciyata Daga Nufin Aikata Zunubai?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu aleikm malam, ina yini, malam ina so dan ALLAH ku yi min bayani idan mutun ya ga zuciyarsa ta zama da duhu, ma'ana ta fi son saɓa ma ALLAH a kan biyayya a gare shi wace hanya ya kamata ya bi don samun haske na zuci?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus salam, duk zuciyar da ta fi son karkata wurin saɓon Allah fiye da yi masa biyayya, to wannan zuciya tabbas ta gurɓace, kuma alama ce da ke nuna mai wannan zuciya yana cikin waɗanda Allah bai yarda da abin da suke yi ba, muna fatan Allah Ta'ala ya kare mu da aikata mummuna, ya ba mu ikon bin umurninsa.

Daga cikin hanyoyin da mutum zai bi don kyautata zuciyarsa ta zamo mai son Allah da yi masa biyayya sun haɗa da:

1. Komawa zuwa ga Allah Maɗaukakin Sarki ta hanyar yawan roƙonsa a kan ya karkatar da zuciyarsa daga aikata saɓo.

2. Mutum ya yaƙi zuciyarsa, ya cire mata shakku, da matsa mata wajen ganin ta yi wa Allah biyayya (wato ya tsarkake zuciyarsa kenan).

3. Yawan tunawa da tsananin azabar da Allah ya tattalar ma da wanda ya aikata saɓon Allah.

4. Mutum ya riƙa tuna cewa duk abin da yake yi Allah na kallonsa a duk inda yake, kuma ba abun da zai ɓuya wa Allah game da shi.

5. Tuna cewa mutuwa za ta iya riskar mutum a daidai lokacin da yake aikata wannan saɓo, to mai zai ce wa Allah idan haka ta faru?

6. Yawan tuna kyakkyawar sakamakon da Allah ya tattalar ma da mutanen kirki da suka yi masa biyayya, wanda masu saɓo ba za su sami wannan ba.

7. Mutum ya yawaita zama tare da mutanen kirki, masu yawaita biyayya ga Allah. Da nisantar mutanen banza, da kiyaye yawan kaɗaita a inda mutanen kirki ba sa ganinsa.

Da ikon Allah Allah zai sa zuciyar bawa ta gyaru idan ya zamo mai kamanta waɗannan abubuwa. Allah ya shiryar da mu.

Allah S.W.T ne mafi sani.

Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8ƙu9GT

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Questions and Answers

Post a Comment

0 Comments