Waƙoƙin bara waƙoƙi ne da ko dai mabarata ke shiryawa ko kuma suke amfani da su wajen bararsu. Wasu mabarata kan shirya ‘yan waƙe-waƙe na begen Annabi (SAW) da kuma wasu waƙoƙin da ke tattare da gargaɗi da karantarwa domin rerawa ga jama’a. Babu wani lokaci takamamme da suka keɓe domin yin bara. Sukan yi bara kowane lokaci wato safe da rana da yamma, kai har ma a cikin dare (Sarkin Gulbi 2007: 49-50).
Salon Hira A Waƙoƙin Bara: Nazari Daga Wasu Waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau
Abdullahi Mujaheed
mujaheedabdullahi@gmail.com
+2348069299109, +2348156747550
Jami’ar Jihar Kaduna
Rabiu Bashir
+2348035932183, +2348022261880
Jami’ar Jihar Kaduna
1.0 Gabatarwa
Nazarin salo gona ce
babba mai kunyakai da yawa; shi ya sa kowane manazarci sai dai ya ɗebi iya kadadar da
zai iya nomewa daidai da manufar nazarinsa. Masana irinsu Mukhtar (2004) da
Yahya (2001) da Garba (2012) da sauransu sun sha rubdugu kan wannan fage na
salo a mabambantan lokuta cikin ayyukansu. Daga ayyukan ire-iren waɗannan masana, an gano
cewa ba komai ba ne salo illa dabara ta isar da saƙo. Shi ya sa salo ke
taka muhimmiyar rawa wajen isar da saƙo a cikin aikin
adabi; walau a waƙa ko a zube ko kuma a wasan kwaikwayo. Saboda haka mawaƙa suke amfani da salo
wajen ƙawata waƙa domin isar da saƙo cikin dabara da
azanci mai armashi. Har ila yau, duk da kasancewar Salisu Sa’in Makafin Zazzau
mabaraci, amma ya kasance ma’abocin sarrafa salo a cikin waƙoƙinsa na bara domin
isar da saƙonninsa cikin armashi. Har ila yau, an lura cewa salon
hira yana sahun gaba cikin irin salailan da yake amfani da su a waƙoƙinsa. Saboda haka, alƙiblar wannan takarda
ita ce nazarin salon hira a waƙoƙin bara na Salisu
Sa’in Makafin Zazzau. Sai dai kafin nan, za a yi tsokaci game da salo da waƙoƙin bara. Sai kuma
tarihin Sa’in Makafin Zazzau a taƙaice. Daga bisani
kuma a ƙwanƙwance salon hira a waƙoƙin Sa’in Makafin
Zazzau.
2.0 Salo a taƙaice
Salo
muhimmin al’amari ne a Hausa, don haka a yayin da (Yahya, A. B. 2001:1-3) yake
nazarin salo ya riƙa kawo misalai da wasu zantukan Hausawa game da salon
inda sukan ce, “salon magana” idan an yi wata magana daban da yadda aka saba
yin ta yau-da-kullum. Haka kuma manazarcin ya ƙara da cewa, Hausawa
kan ce, “sabon salo” wanda ke nufin sabuwar hanya ta daban da yadda aka saba da
wani al’amari. Sannan kuma “sabon rawa” a Hausa yana nufin wata dabara ko
hanyar yin rawa. Yahya ya ci gaba da cewa idan Bahaushe ya ce, “sabulun salo”
yana nufin sabulun da aka bi wata hanya ta daban wajen yin sa. A ƙarshe ya bayyana salo
da cewa dabara ko hanya ko wayo. Ko kuma kwalliyar magana ce mai tasiri a kan
mai jin ta. Haka kuma salo shi yake bayyana saƙo, shi ke kai saƙo inda aka nufa da
shi. Salo dabara ce ko hanya mai yin kwalliya ga abu domin abin ya kwarzanta ko
ya bayyana. Duka-duka dai,
Salo
yana nufin duk wata dabara ko hanya a cikin waƙa wadda aka bi domin
isar da saƙo. Ita wannan dabara ko hanya tana yi wa waƙa kwalliya ta yadda
saƙon
zai isa ga mai saurare ko karatun waƙar (Yahya, 2001:3)
Salo
a waƙoƙin baka wata hanya ce da makaɗi ke kyautata zaren
tunaninsa cikin azanci domin ya cin ma burinsa na isar da saƙo a waƙa. salo a waƙoƙin baka abu ne wanda
yake daɗa fito da ainihin
kyansu ko muninsu, ta haka za a iya gane waƙoƙi masu karsashi, masu
hikima da balaga da kuma waƙoƙi marasa ma’ana,
marasa inganci. Salo ke nan ma’auni ne na rarrabe zaƙin waƙa ko ɗacinta. Salo kuma hanya ce ta sarrafa harshe a
jujjuya shi ta yadda za a iya taƙaita manufa ko a
sakaya ma’ana ko kuma a kaifafa tunani. Za a iya karkasa salon sarrafa harshe
zuwa gidaje guda biyu wato adon harshe da kuma aiwatar da shi. (Gusau, S.M.
20003:53-54).
Salo
yana da wuyar ganewa duk da yake dai ana iya gane wasu sigoginsa. “salo shi ne hanyoyi ko dabarun isar da saƙo”. Kuma salo ya ƙunshi zaɓi a cikin rubutu ko
lafazi sannan kuma daɗi ko armashin zance
da ingancinsa ya dogara ne game da yadda mai magana ya zaɓo kuma ya saƙa kalmominsa a kan
kyakkyawan tsari wajen isar da saƙonsa (Ɗangambo, A. 2008:34).
Don haka salo azanci da basirar fasihai ne
wajen ƙulla tunani, salo kan takure ma’anar abin da ake magana
cikin ‘yan kalmomi. Salo yakan bayar da hoton abu ko al’amari cikin bayani,
yakan ƙunshi kwalliya ko tamka ko alamci ko mutuntawa ko dabbantarwa
ko ƙarangiya
ko kinaya ko jerin sarƙe ko ɗinkin baiti ko salo-rakwacam da sauran azancin magana, waɗanda sukan ɗarsu a zuciyar mai
saurare ko karatu ya yi zurfin tunani a kansu. Salo shi ne yadda harshen
fasihai ke bayyana hoton zuciyarsu. Salo na iya zama duk wani abin da ya
kyautata magana, ya ƙawata ta a zuciyar mai sauraro. Sannan kuma sauƙi ko tsaurin salo ya
danganci lokacin da fasihai suka yi ƙirƙira, ƙwarewar mai sauraro
game da harshe ma yakan taimaka a fahimci salo.
3.0 Waƙoƙin Bara
Waƙoƙin bara waƙoƙi ne da ko dai mabarata ke shiryawa ko kuma suke amfani da su wajen bararsu. Wasu mabarata kan
shirya ‘yan waƙe-waƙe na begen Annabi (SAW) da kuma wasu waƙoƙin da ke tattare da gargaɗi da karantarwa domin rerawa ga jama’a. Babu wani lokaci takamamme da
suka keɓe domin yin bara. Sukan yi bara kowane lokaci wato safe da rana da
yamma, kai har ma a cikin dare (Sarkin Gulbi 2007: 49-50). Shi ya sa Muhammad
(1983), ya ce ta hanyar bara, Namangi ya fara shirya waƙoƙinsa waɗanda galibi jigoginsu na addini ne. Wasu mabaratan kuwa sukan ɗauki waƙoƙi ne da wasu mawaƙan suka wallafa su riƙa amfani da su wajen jawo hankalin mutane su ba su sadaka. Da irin
wannan tunani ne Bunguɗu (2015:104-105) ya bayyana waƙar bara a matsayin waƙar da
mabaraci/mabarata ke amfani da ita yayin da yake/suke aiwatar da baransa/su.
Ana kiran su waƙoƙin bara domin amfani da ake yi da su wajen aiwatar da bara. Waƙoƙin da ake bara da su sukan
kasance na baka ko rubutattu. Na bakan su ne waɗanda tun a
wajen samar da su an ƙudurci tsara su ne saboda a yi
bara da su, mafi yawa domin almajirai. Akan kuma sami wasu waɗanda ba almajirai ba ne sai dai domin sauran mabarata manya, amma haka
bai hana su ma wasu almajirai su yi amfani da su wajen bara ba.
Kamar dai yadda Ampah da Babajo, (2009), suka nuna cewa waƙoƙin bara na almajirai suna
sanya tausayi ga zukatan masu saurare har su ba su sadaka. Haka kuma Almajirai
suna zagayawa yawon bararsu ne gida-gida; da safe ko da maraice domin neman
abinci. Suna yin haka ne ta hanyar yawo da kwanukan cin abincinsu, suna rera
wasu waƙoƙi. Saboda haka, waƙoƙin bara waƙoƙi ne da suka ƙunshi jawo hankalin masu saurarensu domin su rinjayu da saƙon da mabaratan/almajiran suke isar masu, (Ampah da Babajo, 2009).
Daga abin da ya gabata, za a iya cewa waƙar bara da waƙoƙin mabarata abubuwa biyu ne masu yi wa juna shigar giza-gizai, domin
kuwa duk waƙar da ake amfani da ita yayin
da ake gudanar da bara ta kasance waƙar bara, ko da kuwa ba mabaracin ne maƙirƙirinta na asali ba. Sa’annan
kuma akwai waƙoƙin da mabarata ke tsarawa da ba na barar ba, hasali ma waƙoƙi ne masu mabambantan jigo
kamar na sauran mawaƙa gama-gari. Salisu Sa’in
Makafin Zazzau ɗaya ne daga cikin irin waɗannan mabarata, waɗanda suka rikiɗe mawaƙa daga bisani. A cikin waƙoƙinsa akwai waƙoƙin bara kamar ‘Barar Zamani’
da ‘Waƙar Yabo’ da sauransu. Akwai
kuma waƙoƙinsa a matsayinsa na mabaraci waɗanda ba barar ce
manufarsu ba, ba kuma saƙon barar ne a cikinsu ba,
misali,‘Waƙar Rajista’ da ‘Gargaɗi ga Masu Shanƙwaya’ da sauransu, (Mujaheed,
2017).
4.0 Salisu Sa’in Makafin Zazzau Cikin Tarihi
An haifi Sa’in
Makafin Zazzau, cikin shekarar 1933 a ƙasar Daura, daga
bisani kuma shi da iyayensa suka baro ƙasar Daura da ƙuruciyarsa, suka koma
Rafin-Mai-Baka. Cikakken sunansa shi ne Salisu Abdullahi Rafin-Mai-Baka, kuma
iyayensa ba makafi ba ne. Ya sami lalurar makanta ne tun bai wuce kwanaki
arba’in a duniya ba,bayan ya yi fama da
cutar ƙyanda. Duk da haka, ya yi karatun addinin Musulunci
gwargwado a lokacin ƙuruciyarsa, sai dai bai samu yin karatun boko ba
(Mujaheed, 2017).
Cikin shekarun 1960
Sa’in Makafin Zazzau ya koma birinin
Zariya da zama, inda ya zauna wajen maigidansa mai suna Sa’i Ibrahim ɗan Tofa wanda daga
gare shi ne Salisu ya sami sarautar ‘Sa’in Makafi’ bayan rasuwar Sa’i Ibrahim ɗan Tofa. Daga bisani
ya koma garin Kaduna da zama a farkon shekerun 1970. Sa’in Makafin Zazzau ya
kasance ma’abocin hulɗa da gwamnati domin
yana waƙoƙin farfaganda da yaɗa manufofin gwamnati. Shi ya sa bayan shahararsa, kusan kowane
lungu na arewacin ƙasar nan da kudu-maso-yamma babu jihar da bai sanya ƙafarsa ba, ko dai a
karan kansa, ko kuma gayyatar sa ake yi, (Mujaheed, 2017).
Salisu Sa’in Makafin
Zazzau ya yi zaman aure da mata uku lokaci guda, wato Rabi da Amina da Yalwa.
Ko da yake ya auri wasu matan a mabambantan lokuta. Haka kuma ya haifi ’ya’ya
goma sha uku, cikin goma sha ukun nan, goma maza ne, uku mata. Sa’annan cikin
wannan adadi, uku suna raye, goma kuma sun rasu, (Mujaheed, 2017).
Bugu da ƙari, an naɗa Salisu Abdullahi a
matsayin Sa’in Makafin Zazzau a shekarar 1968, lokacin Sarkin Makafi Umaru.
Kafin naɗin, ana kiran sa
‘Wazirin Samari’ ne. A ƙarƙashinsa kuma, akwai yaransa da suke masa amshi waɗanda kowannensu da
sarautarsa, (Mujaheed, 2017).
Dangane da waƙa kuwa, Sa’in Makafin
Zazzau bai gaji waƙa ba, walau ta wajen mahaifi ko mahaifiyarsa, basira ce
Allah (SWT) ya ba shi daga waƙoki na bara, har ya kai ga shahara ga
waƙoƙi na fadaƙarwa da isar da saƙonnin gwamnati ga
al’umma. Ya fara waƙa ne tun yana Kano, musamman a lokacin da yake tare da
ubangidansa Magaji na Ɗambatta, wanda aka ƙaddara shi ne ya koya
masa waƙoƙin baran. Har ila yau, ya daɗe yana ‘yan waƙoƙinsa na bara, kafin
shahararsa a wajajen shekarun 1965/1966 sakamakon rikicin juyin mulkin da ya
kunno kai a lokacin. Wannan ne ya haifar da waƙarsa ta “Soja” wadda
ta shahara sosai kuma ita aka fara sanyawa a gidan rediyo domin fadaƙar da jama’a dangane
da muhimmancin haɗa kan ƙasa, (Mujaheed,
2017).
Daga wannan lokaci,
duk abin da ya tusgo daga manufofin gwamnati da take buƙatar a jawo hankalin
jama’a, ko a gargaɗe su, sai Sa’in
Makafin Zazzau ya shirya waƙa a kan abin, ya riƙa rera ta yayin da
yake bararsa. Idan ‘yan jarida suka ji shi, sai su ɗauka su watsa a
gidajen rediyo. Da abin ya ci gaba, tun yana yi a matsayin sa-kai, har ya
kasance gwamnati ko hukumomin gwamnati musamman Hukumar Watsa Labarai da Gidan
Rediyon Tarayya na Kaduna, suka riƙa neman sa domin ya
tsara waƙoƙi game da wasu manufofin gwamnati, idan sun kunno kai.
Alalmisali, sauyin kuɗi da aka yi a shekarar
1973 Sa’in Makafin Zazzau ya yi waƙar ‘An mana Sabon Launi’ wadda ta yi matuƙar tasiri ga manufar
da ake son cim ma ga al’umma. Haka kuma ya yi waƙa game da sauya tuƙi daga dama zuwa
hagu, duk a waɗannan shekaru. Ta
haka ne yakan sami abin masarufi daga hukumomin da suka ɗauki alhakin waƙokin.Wannan ya haifar
da kyakkyawar dangantaka tsakanin Sa’in Makafin Zazzau da gwamnati, (Mujaheed,
2017).
Wajen shirya waƙoƙinsa, Salisu Sa’in
Makafin Zazzau da yaransa, sukan zauna ne su tsara yadda amshinsu zai kasance,
bayan tattaro bayanai game da abin da kayan cikin waƙokin za su ƙunsa, kafin su rera
kowace waƙa. Daga nan ne, sai su rera a duk lokacin da ake buƙata. A wasu lokutan
kuma, yakan ƙiri waƙa nan take idan buƙatar hakan ta taso.
Dangane da waƙoƙinsa na farfaganda kuwa, gidajen rediyo su ne suke
kasancewa mahaɗa tsakaninsa da
gwamnati. Ta hanyar su ne yake samun bayanai game da abin da duk ake buƙatar ya waƙe, (Mujaheed, 2017).
Kafin rasuwarsa, ya
yi waƙoƙi da dama, kuma ta hanyar waƙoƙin ne, yake samun duk
abin masarufin da yake buƙata a rayuwarsa ta yau da kullum. Haka kuma ta hanyar waƙa ya sadu da jama’a
daban-daban, wanda hakan ya sa ya sami shahara da ɗaukaka a duniya.
Salisu Sa’in Makafin Zazzau ya rasu ne a watan 8, na shekarar 1988, (Mujaheed,
2017).
5.0 Salon Hira A Waƙoƙin
Sa’in Makafin Zazzau
Salon hira ya ƙunshi muryar mai
magana fiye da ɗaya, wato mawaƙi ya ƙadarta cewa da shi da
wani ne ke magana, ko kuwa wasu masu magana biyu ko fiye ne ke wa juna magana.
Salon hira yakan taimaka wa mawaƙi a ƙoƙarinsa na isar da saƙonsa ta hanyar sa mai
saurare ko karatu ya zamo ya ƙara kusantar mawaƙi. Wato, sai mai
saurare ya ji daga bakin waɗanda mawaƙi ke magana a kansu, ba wai daga bakin
mawaƙin ba (Yahya 2001:109).
Shi kuwa Alamuna cewa
ya yi salon hira a waƙa ya ƙunshi jin muryar mai magana fiye da ɗaya ne, wato mawaƙi mawaƙi ya ƙaddara das hi da wani
suke magana, ko kuma wasu masu magana biyu ko fiye ne ke wa juna Magana. Ya ƙara da cewa irin
wannan salo yana daga cikin salailan da mafiya yawan mawaƙan fina-finan Hausa
ke amfani da shi cikin waƙoƙinsu kasancewar mafi yawa waƙoƙi ne na soyayya, inda
a wurin aiwatar da waƙar mawaƙin kan ƙaddara cewa saurayi
da budurwa ne ko mata da miji ke hira kan soyayyarsu.
Idan aka duba bayanan
masana dangane da ko mene ne salon hira a taƙaice, za a iya cewa
wata hanya ce ko dabara ta isar da saƙo a cikin waƙa ta yadda mawaƙi kan ayyana cewa
suna tattaunawa ne da wani a wani mutum guda ɗaya ko wasu mutane da yawa a wani
bigire ko yanayi, don haka maimakon ya kawo wa mai saurare labarin yadda hirar
ta kasance a tsakaninsa da mutumin ko mutanen kawai kai tsaye, sai ya saƙo hirar da yadda ta
kasance a waƙe, inda shi kuma mai saurare zai rinƙa jin hirar da kuma
yadda take gudana a tsakanin mawaƙin da aboki ko abokan
hirar tasa, yana tambaya suna amsa masa ko kuma ana tambayarsa yana amsawa.
Watau dai shi irin wannan salo yana zuwa ne da tsari na tattaunawa a tsakanin
mawaƙi ko fasihi da wani ko wasu mutane a cikin waƙa.
Yawanci makafi mutane
ne da Allah yake halittarsu da hikima da azanci na musamman duk da kasancewar
ba su gani, hakan ya sa suna da yawan son hira da kuma tattaunawa da mutane
domin su ƙara samun wani sabon ilmi ko labari na wani abu ko wani
wuri da ba su iya zuwa ba, don haka ba zai kasance wani abin mamaki ba a sami
irin wannan salo a cikin waƙoƙin bara, waɗanda yawanci waƙoƙi ne da ake aiwata da
su a cikin mutane domin neman abin masarufi. Don haka waƙoƙin Sa’in makafin
Zazzau na cike da irin wannan salo. Misali :
A waƙarsa ta ‘Bayanin
Wulli’, Sa’in Makafin Zazzau ya yi amfani da irin wannan salon yayin da ya je
rumfar wani tela bara, inda a cikin waƙar ya kawo wa mai
saurare abin da ya gudana a waƙe cikin hira. Ga yadda hirar tasu ta
kaya:
Ya ce mini Malam Makaho
Wancan wane ne?
Da dai na kaso kunnena
Sai
na jiyo ƙarar walkinshi
Da na ce Wulli ne
Kan a jima ai tela ya miƙe
Yana
yi ta-kanka Makaho
Kadan
ya zo ni ma zan tsere
Na
tashi na ƙwaƙume tela
Sai yai ƙumaji
"Don
ubaka sake ni Makaho"
"Ba
za in sake ba tela"
Ya
ce, a'a Makaho
Ni
ma na ce a'a tela
Ta ya za kai min wannan?
Ka
san ba za ka iya ba
Ta
ya ka ce in shigo rumfarka?
Ya
kai min zagi
'Yau
ka ga Makahon banza'
Ya
za ka riƙe ni
Kadan
ya taho har ni zai kwaɗe
Na
sau tela na tsinke
(Sa’in makafi Ba ni bayanin wulli)
Abin
lura a nan shi ne, duk da cewa mawaƙin yana labarta yadda
ta kaya tsakaninsa da Wulli ne a rumfar tela, sai ya yi amfani da salon hira,
inda ya kawo yadda tattaunawar ta kasance tsakanin makaho da tela. Da farko ya
nuna cewa tela yake tambayarsa ko wane ne yake tunkaro rumfar tasa? Duk da
kasancewar Sa’in makafi mara gani, sai ya yi amfani da wata hikima wada aka san
makafi da ita, ta wajen saurarawa su ji motsi ko ƙarar wani abu su iya
tantance shi, wadda irin wanna hikimar ce ta ba shi dama har ya gene wanda ya
tunkaro su ta hanyar jin motsin walkinsa. Bayan Makaho ya gaya wa tele cewa
Wulli ne ya tunkaro rumfar sai fa tela ya nuna masa ya yi ta kansa, domin shi
ma ba zai zauna ba, daga nan sai makaho ya ƙanƙame tela sai kuma taƙaddama ta kaure hard
a zagi, amma duk da haka dai makaho bai saki tela ba. Duk waɗannan abubuwan da
suka faru tsakanin tela da makaho da yadda suka yi ta ja-in-ja cikin zance,
Sa’in makafi ya kawo shi ne a waƙe, wanda hakan ne zai
ba mai saurare dama ya ji wa kunnuwansa yadda hirar ta kaya tsakanin makaho da
tela.
A cikin
waƙar
‘Idi Wanzami’ ma, Sa’in Makafin
Zazzau ya yawaita amfani da irin wannan salon cikin zantawarsa da mutanen garin
Gagawa da kuma Wanzamin da ke masa aski. Misali wurin da ya ce:
Na ce; “Idi Wanzami,
Ka sayi turmin alawayyo,
Ko an yi rashi a gidanka?”
Sai ya ce mani a’a.
Na ce; “Idi Wanzami,
Na Tashar Gagawa,
Ga ƙato saba’in a gabanka,
Ga ƙatti saba’in a gabanka,
‘Yan gayyar noma ne,
Ko kuwa ‘yan ɗaurin aure ne?”
Sai ya ce mani a’a.
Na ce; “Idi Wanzami,
Na Tashar Gagawa,
Subhanallahi!
Na ji ka kira limami,
Wai aure zai ɗaura,
Ko kuma zai huɗubar suna ne?
Ko ko zai yi ma hujja’u?”
Sai ya ce mani a’a.
Ya ce; “kai tsaya makaho,
Tambayarka ta fa ishe ni,’
Bari dai za na ba ka amsa,
Ka ga hatsin da na bayar,
Hatsin gumbar sadaka ne,
Turmin alawayyo,
Wannan turmin likkafani ne,
Ƙato
saba’in kuma,
Wannan ‘yan ɗaukar gawa ne,
Shi ko limami,
Shi ne zai maka sallah.”
Wannan misali ne na
salon hira, wanda yake nuna irin tattaunawar da ta wanzu tsakanin makaho da
kuma Idi wanzami, wadda duk wannan hirar ta kasance ne a tsakaninsu kafin a
fara yi wa makaho aski. Mawaƙin ya kwararo wa mai saurare ne yadda
hirara ta kasance, inda ya fara da kawo tambayar da ya yi wa wanzamin lokacin
da ya gan shi da turmin alawayyo, ko shin an yi rashi ne a gidansa, amma sai
wanzami ya amsa masa da cewa a’a. Daga nan kuma sai ya tambaye shi su kuma waɗannan ƙartin har mutane
saba’in me za su yi? Shin noma za su yi masa? Ko ɗaurin aure za su je? A nan ma sai
wanzami ya amsa wa makaho da babu ko ɗaya. Makaho bai haƙura ba sai kuma ya
sake tambayar wanzami cewa ya ji yana kiran Limami ne, shin aure zai ɗaura ko kuma huɗubar suna zai yi, ko
kuma wata tambayr wanzami zai yi masa? A nan ma sai wanzami ya amsa masa da
babu ko ɗaya. Daga ƙarshe dai wanzami ya
yi fushi ya nuna cewa tambayoyin fad a makaho yake yi masa sun fara yi masa
yawa, don haka sai ya amsa masa da cewa, ya fa sani hatsin day a aika da shi na
sadaka ne za a yi, sannan turmin alawayyo likkafani za a yi masa da shi, su
kuma waɗannan ƙarti guda saba’in su
ne za su ɗauki gawar makahon, a
yayin das hi kuma Liman shi ne zai yi masa sallah. Idan aka duba za fahimci
cewa Sa’in makafi ya zaɓi ya yi amfani da
wannan salo ne na hira domin ya kawo wa mai saurare irin bahallatsar da ta faru
tsakaninsa da Idi wanzami, wanda ya je rumfarsa domin ya yi masa aski, amma sai
ya ga wasu baƙin abubuwa da wanzamin ken aiwatarwa don haka bai yi ƙasa a gwiwa ba ya
fara tambaya shi kuma wanzamin na amsa masa. Wanda yin hakan ne ya ba mai
saurare damar jin tattaunawar da ta gudana tsakanin wanzamin da kuma makaho.
A cikin waƙar ‘Direba Makaho’, a nan ma Sa’in Makafi ya yi amfani da wannan
salo na hira, inda ya ba mai saurare dama ya saurari hirar da ta wakana
tsakaninsa da masu mota. Misali inda y ace:
Da zuwana Legas,
Da
ni da abokan aiki,
Yaya muka ƙare?
Sai na je wajen Hausawa,
Na ce; “Salamu alaikum,
Hausawan Legas,
Ga baƙo na makaho,
Amma fa ina da jawabi,
Ni ina da jawabi,
So nake na kama sana’a,
Ni fa barar nan ta dame ni.”
Sai suka ce; “To malam,
Yanzu nan wane aiki za kai?”
Subhanallahi!
(Sa’in Makafi: Direba Makaho)
Idan aka duba wannan ɗan waƙar, Sa’in Makafi ya
kawo wa mai saurare hirar da ta gudana ne a tsakanisa da wasu Hausawa a garin
Legas a lokacin da ya tafi neman sana’a kasancewar ya gaji da bara . Sa’in
Makafi ya kawo hirar ne ta hanyar nuna yadda ya je ya samu waɗannan Hausawa suna
zaune a wurin kasuwancinsu, amma bai faɗa musu kai tsaye ba sai day a yi musu
sallama, wadda it ace al’adar duk wani baƙo na kirki kamar
yadda Hausawa suka tabbatar cewa “baƙo babu sallama mugu
ne”. Bayan makaho ya yi sallama ne sai kuma ya gaya wa mutanen dalilin zuwansa
garesu, wato ya zo ne domin ya bayyana musu cewa shi fa barar da yake yi ta
dame sa kuma bai ɗauke ta a matsayin
sana’a ba, don haka ya yanke hukuncin zai fara wata sana’a. bayan Hausawn Legas
sun saurari jawabin makaho sai kuma suka amsa masa ta hanyar tambayarsa da cewa
to shi a nasa tunanin wane irin aiki zai yi a matsayin sana’a kasancewarsa
makaho? Duk wannan tattaunawar da ta gudana tsakanin makaho da Hausawan Legas
Sa’in makafi ya kawo ta ne a waƙe ta yadda mai saurare zai ji yadda
hirar ke gudana tsakanin mutanen da kunnuwansa, wanda dalilin sarrafa salon
hira ne a cikin waƙar.
Haka dai mawaƙin ya ci gaba da
sarrafa irin wannan salo na hira a cikin waƙar tasa ta ‘direba
Makaho’ domin ganin ya kawo wa mai saurare irin irin yadda hirar tasu ta ƙare da waɗannan mutane da ya
samu da nufin su samar masa da aikin da zai rinƙa yi domin neman na
abinci a maimakon bara da yake yi. Inda ya ce:
Na ce; “Hausawan Legas,
Ku saya mani moto,
Mu je mu cika ta da lodi,
Mu je mu ɗau fasinja,
Karen motanmu makaho,
Ɗan
kamashonmu makaho,
Kwandastan namu makaho,
Akawun namu makaho,
Duk babu mai ido a cikinmu.”
Sai suka ce; “ kai malam,”
Daga nan babbansu ya miƙe,
Ya ce; “Kai tsaya makaho,
Ka san mu nan,
Ka san mu Hausawa ne,
A cikin nan namu,
Wa zai yarda ya ɗauki asara?
A saya maka mota,
In ka saka ta a rami,
Ai a yi ba uwa ba riba,
Na ce; “Allah zai kare,”
Sai suka ce; “Kai malam,
Mu mun yarda da Allah,
Amma wajenmu ba mu da mota.”
A nan Sa’in Makafi ya
ci gaba da kawo wa mai saurare yadda tattaunawarsu da Hausawan Legas ta wakana
ne ta hanyar sarrafa salon hira, inda ya jiyar da shi yadda yake roƙon Hausawan da su
saya masa mota domin ya zaɓi tuƙi ne a matsayin sana’ar da za ta maye
gurbin barar da yake yi. Ya gaya masu cewa shi ne dai zai tuƙa motar a matsayin
direba duk da kasancewarsa makaho, haka kuma da yaron motar da ɗan kamashon da zai yi
musu lodi da akawun motar duk makafi ne. Bayan Hausawan Legas sun saurari
jawabin makaho sai suka amsa masa ta bakin babbansu wanda ya bayyana masa cewa,
su fa Hausawa ne, don haka babu wani wanda zai iya yin wannan kasadar a cikinsu
domin gudun asarar da za ta faɗa masa yana ji yana gani ya ɗauki kuɗi ya sayi mota
sannan ya hannantata ga makaho, wanda a ƙarshe tana iya yin haɗari. Duk da jawabin
waɗannan mutane makaho
bai haƙura ba sai ya ci gaba da ƙoƙarin lallashinsu ta
hanyar nuna masu ƙaddara da Allah, tare da ƙarfafa musu gwiwa
cewa Allah zai iya kare su tare da motar, sai dai a ƙarshe dai haƙarsa ba ta cim ma
ruwa ba, domin haka suka gaya masa cewa sun fa yarda da Allah da kuma ƙaddara, amma duk da
haka ba su da motar da za sub a shi ya tuƙa. Mawaƙin ya sarrafa wanna
salo ne na hira saboda mai saurare ya ji irin yadda tattaunawar ta gudana
tsakanin makaho da Hausawan Legas a waƙe.
6.0 Kammalawa
Muhimmancin salo a waƙa ba ya misaltuwa,
saboda salon ne ke kwarzanta mawaƙin da waƙar, kuma shi ne yake
rayar da harshe, ya kuma kaifafa tunanin mai ji ko mai sauraro kuma ya sarrafa
shi tare da bayyana shi cikin irin fahimtar da ake buƙata. A wannan aikin,
an nazarci salon hira ne a waƙoƙin Salisu Sa’in
Makafin Zazzau, waɗanda galibinsu waƙoƙin bara ne. Saboda
haka, an kawo bayani kan salo da waƙoƙin bara da kuma taƙaitaccen Tarihin mawaƙin. Daga ƙarshe aka fayyace
fasalin salon hira a waƙoƙinsa. An gano cewa salon hira yana kan gaba cikin salon
da mawaƙin yake amfanin da shi wajen gabatar da waƙoƙinsa.
7.0 Manazarta
Tuntuɓi masu takarda.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.