Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu Jami’ar Tarayya Gusau.
Tsafe–Tsafen Maguzawa: Nazari A Kan Bukukuwan Maguzawan Kwatarkwashi (5)
NA
ABDURRAHMAN LAWALI
BABI NA HUƊU
BUKUKUWAN AL’ADUN
MAGUZAWAN KWATARKWASHI
4.0 GABATAWA
A babin da ya gabata na yi tsokaci a kan yadda taƙaitaccen tarihin ƙasar Kwatarkwashi,
dangantakar Maguzawan Kwatarkwashi da da Maguzanci, Tsarin shugabancin
Maguzawan Kwatarkwashi, Al’adun Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi da sana’o’in
maguzawan Kwatarkwashi.
A wannan babin zan yi
bayani
a kan ire – iren bukuwan Maguzawa da al’adunsu da
hanyoyin mallakar macce a Maguzance.
4.1 BUKIN
CIKA SHEKARAR MAGUZAWAN KWATARKWASHI
Kamar yadda muka sani ɗan – Adam mutum ne wanda Allah ya nufa da son jin daɗin rayuwa, sai dai idan bai samu ba, ya yi haƙuri. Kamar haka su ma Maguzawa suna da lokaci da suke
keɓe wa irin wannan buki ko shagulgula, wato bukin cika shekara.
Irin wannan bukin ana
gudanar da shi ne bayan an gama aikin gona, kuma amfanin gona ya zo gida. Kamar
dai yadda Maguzawa kan inganta sauran bukukuwa irin su aure, bukin zanen suna,
bukin kaciya da sauransu, haka shi ma wannan bukin cika shekara suke gudanar da
shi. Inda za su aika da goron gayyata zuwa duk inda wasu ‘yan uwansu suke domin
gudanar da wannan buki.
Maguzawan Kwatarkwashi
suna amfani da wannan aljani na tsafinsu wanda suke kira Kyauka domin gudanar
da wannan buki na cika shekara. Bayan ranar gayyata ta zo, Maguzawa kan tafi
gidan shi wannan aljanin Kyauka domin rarrashin sa da ya amince su zo da shi
domin gudanar da wannan wasa ko buki. Amma kafin a tafi wurin dole ne a tanadi tulunan giya, baƙaƙen bunsura kamar guda hamsin (50) da
jajayen zakaru kamar guda ɗari biyu (200) waɗan da za a yanka masa ya sha jini domin neman
amincewarsa.
Bayan ya amince za a biyo
hanya zuwa gari, za a kirawo gwanaye don aljani Kyauka masu ɗaukar kayansa waɗanda da ma an riga an tanade su don irin wannan buki. Sannan su sa ma shi Kyauka wannan suturar. Irin kayan kuwa su ne:- Baƙaƙen tufafi na saƙi da suka haɗa da riguna, zannuwa da sauransu. Sannan zai yi ta yin
wasanni iri – iri, ana kaɗe – kaɗe yana rawa, yana fitar da abubuwa
na ban tsoro daga jikinsa. Kuma shi wannan buki na
cika shekara kan iya ɗaukar kwana goma sha huɗu ana gudanar da shi.
Kuma ana zuwa ga sarakuna irin su sarkin tsafi da
sauransu.
Kamar yadda aka sani cewa
ba a kallon wasar Kyauka da fararen tufafi, haka nan Bahillace ba ya zuwa kallon wasan Kyauka domin a nasa gani, wai ba duk
kowane Bahillace ba ne ɗan halak ga ubansa. Don haka, mai farar sutura da Bahillace ba su zuwa
kallon wannan wasan. Idan kuwa suka kuskura suka tafi, tasu ta ƙare. Saboda haka, kafin
wannan wasan ta Kyauka ta soma, sarakuna sukan aikawa talakkawansu da cewa su
san irin waɗannan ƙa’idoji, idan suna son zuwa kallon
wannan wasan.
Wannan wasa na Kyauka wasa
ne wanda ke ƙara fitar da darajar Maguzawa, kuma wanda yake a dole ne a ji tsoron
su.Domin idan ka ga yadda Kyauka ke wasa, lalle ka ga abin tsoro. Domin kuwa ita wannan wasa ana fara ta ne da misalin ƙarfe goma sha biyu na dare. Amma da
zarar ya fara wannan wasan, ko ina zai haske kamar rana. Wani
lokaci ka ga wuta ta kama ta yi sama kamar tafiya rabin kilomita ɗaya wadda kai kanka ba za ka iya tabbatar da iyakacin
tsawonta ba. Kuma wani lokaci za ka ji ya yi gumza wadda za ka ji ƙasa na motsi kamar za ta
tsage, sai ka ga kowane mutum da dabba sun firgita baki ɗaya. Amma abin mamaki sai ka ga Maguzawa ba su ko damu
ba, sai dai ba shi magana kawai suke yi suna yi masa kirari suna cewa;- “Mun
tuba, Baba ɗiyanka, Baba ka ga ta kowa, taka ta
yi wuyar gani, Ubangiji mabiyanka aiki ba da kai ba a fasa” Haka dai za ka ji
suna ta faɗi kuma suna watsa masa turare da
giya. Sannan sai ka ji ya yi shiru kuma ya ci gaba da wasanni iri – iri waɗan da ɗan – Adam bai taɓa gani ba a cikin rayuwarsa na ban tsoro ba. Wanda idan ya yi su za ka ji
kamar duniya za ta tashi.Domin kuwa ita kanta ƙasa za ka ji tana motsi, itatuwa
kamar za su faɗi domin tsananin iska. Haka Kyauka
ke gudanar da irin wannan wasansa har ranar da sarki ya sallame su. Inda zai ba su babbaƙun shanu da bunsura da zakaru da sauransu. Sa’annan su koma gida. Daga ƙarshe su sallami shi
Kyauka su mayar da shi gidansa, sai kuma wata shekara dai – dai
wannan lokaci.
4.2 BUKIN WASAN BAURA DON NUNA JARUNTAKA
Wasan baura ana gudanar da
shi sau ɗaya a shekara, a lokacin kaka bayan
an cire kayan gona an kawo gida. Ranar kasuwar garin ake gudanar da ita. Tana
cikin bukin wasanninsu na shekara da ake aiwatarwa na al’adun gargajiya da suka
gada tun kaka da kakanni a Maguzance. A ƙofar gidan magajin garin nan ne ake gudanar da ita. Kamar yadda aka saba a Maguzance, ana wannan wasa domin nuna jaruntakar Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi a fili don ana yin ta kamar wasan
“Dambe”.
Sai dai tafi kama da wasan kokowa wadda muka sani. Ita wannan wasa ta baura idan za a gudanar da ita ana share fili tare da yi
masa zobe da ‘yan kallo na ko’ina da suka zo. Su ko a bisa al’ada sai kowanensu ya je wurin bautar tsafin Magiro na
Magajin dutse domin neman sa’a. Sa’annan a shigo da guda – guda, ana yi masu
kuwa da kirari tare da ihu gaba ɗaya. In an zo za a yi kirari ga ɗai – ɗansu, sai su sa wasu zobba masu
bala’in kaifin gaske kamar reza. Da su ne ake bugun mutum a duk inda aka samu, ko a fuska ko a kunne ko a kunci da dai sauran sassan jiki. A nan ake bugewa har a kai wani ƙasa kwance galala a cikin jini baje – baje. Amma akwai
maganin da suke sawa idan an bugi mutum har fata ta yanke. Suna haɗa kashin shanu a kwaɓa da wani magani, sai a shafa wurin, shi kenan zai tsaya,
ya koma shafewa kamar ba a yi yankan ba.
Masu wasar da ‘yan kallo
duk suna gaf ne da bakin duwatsun tsafi, wanda ake bi ta ƙarƙashinsa a hau samansa. A nan kusa da wurin akwai kogunan duwatsu daban – daban da manya da ƙanana ana ce masu, “komo”.
Ana haɗa waɗanda ba su taɓa sanin juna ba, wanda yake kowanensu ana ji da shi a garinsu a kan jaruntakarsa ta wannan wasan
Baura ƙwarai.
Akwai mutumin da ya fi
fice ƙwarai a wannan wasa ta Baura, ana ce masa “KALAGU” don shi ne ma
magajin tsafin Magiro ya ba shugaban wasan Baura na ƙasar Kwatarkwashi don ya riƙa gudanar da ita yadda
ya kamata. Kuma ga garuruwan da suka fi yin fice a ƙasar kamar su: Hujrin
giya, Samawa da Sankalawa, su ne manyan garuruwa. Ana son ko wane ɗan wasa ya zo da makiɗansa don ya yi masa kiɗa domin ya yi zafin nama da jaruntaka, tare da nuna ƙwazonsa a fili. A wurin haɗuwarsu makiɗan suna faɗin haka a cikin kiɗa da kirarin ‘yan wasa:
“Ga ka nan tafe!
Ga ka nan tafe baƙo!
Ga ka nan tafe baƙo, ba a san halinka ba!”
Duk ‘yan wasan suna ciccika suna hurji, har sai an gwada tsakaninsu sa’annan a san na ƙwarai wanda shi ne
jarumi.
4.3 BUKIN WASAN TASHEN MAGIRON MAGAJI
Wannan wasar tashe ana
gudanar da ita ne a shekara idan aka dawo daga wasan
tsafin bautar Magiro na magajin dutse. A bisa ga al’adar
tasu sai an gama bautar shekara sa’an nan a aiwatar da ita. Ga yadda ake
aiwatar
da ita:
Da kaka ake gudanar da
tashen bayan an gama ɗebe kayan gona sarai ba sauran komi sai karan gona ko su ko an fara adana su saboda dabbobi. Don tashen murnar kewayowar shekarar
bautar tsafin Magiro na magajin duwatsun Kwatarkwashi da gama bautar lafiya,
tare da murnar samun amfanin gona na wannan shekara mai yawa. Akan haka ne
yaran Maguzawa ke gudanar da al’adunsu da suka iske tun daga kaka da kakanni ta
gudanar da wannan wasa ta raha da annashawa da nishaɗi da ban dariya ga jama’a na gida – gida ko na kan
dandali masu fira a waje. Wannan wasa ta tashe ana gudanar da ita a tsakanin
mazansu da matansu, wato ‘yan mata da samarinsu da ke zaune a dandali suna hira
barka da samun kewayowar wannan shekara. Sai su mutanen su ce barka kadai,
tsafin su ya maimaita.
Su matansu suna tafiyarsu
daban ne, suna gudanar da yadda ake aikace – aikace nasu a gidajensu cikin raha
tare da ban dariya. Su samari nasu daban suke yi kuma ba sukan shiga gidajen ba
sai na ‘yan uwansu.
Amma babban abu gare su shi
ne su gudanar da wannan tashe a mazaunin mutane na
dandalin hira, a inda dattijai iyayensu suke zama. Ana kwaikwayon ayyukan gargajiya
ne na gado kamar ƙira, noma, wanzanci da sauransu. Su yara ƙanana su ke haɗewa mazansu da matansu. To Maguzawa sun
yarda da haka don su ma su gudanar da nasu daban har su iya a hankali. Bayan
haka, ana samun manyan mutane suna
gudanar da wannan wasa na tashe matsakaita, masu aure, nasu yakan zo ne daga ƙarshen watan da suke yi,
don kamar kowane rukunin jama’a suna da nasu lokacin yin tashe.
Da haka ne ake gudanar da
wannan wasan tashe na tsafin bautar Magiro na magajin duwatsu, har akai ƙarshensa a cikin raha da
annashawa da ban dariya ga jama’a don shi ne watan farin cikinsu.
4.4 AL’ADUN DA SUKA SHAFI RAYUWAR MAGUZAWA
Al’adun Maguzawa suna
nufin sababbiyar hanyar rayuwarsu. Don haka, al’ada ita ce hanyoyin gudanar da
rayuwa ta yau da kullum da ke faruwa ga rukunin jama’a masu zama wuri ɗaya ko yankin gari, ko ƙasar baki ɗaya. Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi sun samu kansu a wannan
yanki tun kaka da kakanni. Masu salsalar asali waɗanda suka fara zama a wannan wuri, su ne suka samar da al’adun rayuwa a tsakaninsu. Don haka suke gudanar da komai nasu a bisa wannan tsari na yau da kullum.
Sun kuma ƙunshi matakan rayuwarsu na tun daga haihuwarsu har zuwa mutuwarsu. Akwai yadda ake gudanar
da abubuwan da suka shafi tsarin rayuwarsu tun daga al’amurransu na kasuwanci
har zuwa abin da ya shafi shugabanci da sauran ƙananan bukukuwan wasanni da suke
gudanarwa daban – daban.
Ga su kamar haka, bi da bi
a tsare, tare da bayanansu da yadda ake gudanar da bukukuwan kamar haka a jihar Zamfara.
a.
Auren Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi
b.
Haihuwa a Maguzance
c.
Mutuwa a Maguzance
d.
Sauran fannoni na
al’adun Maguzawa
4.5
NEMAN AUREN MAGUZAWAN ƘASAR KWATARKWASHI
Aure hanya ce ta ƙulla zama tare tsakanin jinsi biyu na mace da namiji ba tare da an iyakance
adadin zamansu ba. Sai idan mutuwa ta yi halinta.Ana yin aure bisa ga samun
yardar da amncewa a tsakanin saurayi da budurwa. Da kuma samun amincewar iyayensu da kakanninsu domin gudanar da shi, kamar
yadda al’adarsu ta zo da shi.
Al’adun Maguzawa sukan
fara la’akari da shekarun waɗanda za a yi ma aure tsakanin saurayi da budurwa ko mace da namiji.Sai dai
an fi duba na mace in ta kai shekara goma sha bakwai zuwa sha takwas (17 – 18).
Daga nan ake yi masu aure da namiji da ya kai shekaru goma sha takwas zuwa
ashirin (18 – 20). Kafin a kai ga aure, suna gudanar da soyayya a tsakaninsu
tun daga haɗuwarsu da suke yi a ranar cin
kasuwar garin, musamman ma in lokacin kaka ta yi (lokacin da aka gama aikin
gona). Saboda mata suna zuwa cin kasuwa a ƙauyuka da garuruwan da ke kewaye da duwatsun. Don haka,
su ma maza ba a bar su a baya ba. Samari suna zuwa cin kasuwa don ba wani sauran
aikin gona da ya rage a daji. Samari da ‘yan mata suna haɗuwa a ƙauyukan da garuruwan don gudanar da kasuwancinsu tare da
gudanar da samartaka da ‘yan matanci a tsakaninsu da marece bayan rana ta yi
sanyi.
Bayan ‘yan kasuwa sun fara
watsewa, irin dattijai maza da tsofaffin mata da sauran waɗan da bai kamata su tsaya ba. Daga nan ne sai makiɗa su fara aikinsu na kiran ‘yan mata duk inda suke a lungun kasuwar. Idan
suka
ji wannan ƙarar kalangun,to sai su zo ko sun sayar da abin da suke
talla, ko ba
su sayar ba. Sai bayan sun taru sosai har sun fara
gudanar da rawa.
Bayan an taru sai su fara rawa ta ɗai – ɗaiku don jawo hankalin samari da ‘yan kallo mazansu da
matansu. Ana taruwa ƙwarai da gaske a yi ta kiɗa. Wasu daga cikin ‘yan matan da samarin sun riga sun gana da junansu a
wurin kasuwanci.
Wasu ko ba su samu dama ba sai a dandalin taron kiɗa ne za su yi nasu zaɓe ta hanyar nuna soyayya da ƙaunar juna. Sai tana cikin gudanar
da rawa ya shiga ya taya ta kuma ya yi mata kari sosai. Haka za a yi ta yi har lokacin
tashi ya yi.
Kowa ya koma ƙauyensu da garuruwansu sai kuma wata ranar kasuwa ta gewayo. Bayan sun gama rawa tare, ya gama zuba mata karin kuɗi, sai su fito don wasu su shiga, su ko suna gefe don yin zance ko hira a tsakaninsu saboda soyayya ta shiga
kenan. Shi zai faɗa mata ƙauyensu ko garin da ya fito, idan ba
daga gari ɗaya suke ba. Ita ma haka za ta yi
mashi kuma za ta gayyace shi zuwa
garinsu ko gidansu don ya ga iyayenta.Ko kuma shi ya gayyace ta zuwa garinsu a
gidansu don iyayensa su san cewa ga wadda yake so ta zo. Wannan gayyata da ake
yi tsakanin saurayi da budurwa na zuwa garuruwansu shi ne ake ce ma “Tsarance”.
Bayan sun zama jiki
tsakaninsu yana haɗuwa da ita a duk ranar kasuwa ko ta garinsu ko ta wani gari don yin zance,
sai ya fara zuwa garinsu wajen zance. Ita kuma idan bai zo ba ko in ta samu
hali ita
ma sai ta je garinsu don tayi zance da shi. Za ta gayyace
shi ya je garinsu don wasar da ake gudanarwa a duk shekara a tsakanin ‘yan mata
da samari.
Inda ‘yan mata daban – daban suke taruwa su ɓarje guminsu don yin rawa iri – iri a tsakaninsu don
samarinsu su
ga abin da ya ba su sha’awa da
gwanintar da suke nunawa. Samarin za su riƙa yi masu kari har a tashi
wasan.Wannan ita ce hanyar rayuwar da Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi ke bi wajen neman
aure a tsakanin saurayi da budurwa. Kafin gudanar da aure akwai matakai kamar
haka:
1.
Haɗuwarsu a kasuwa da wurin wasan kiɗan kalangu
2.
Tsarance a tsakanin
budurwa da saurayi
3.
Shigowar iyayensu
4.
Hawan duwatsu don kamo
maiki daga sama zuwa ƙasan duwatsun.
4.5.1
SOYAYYAR TSARANCE TSAKANIN SAURAYI DA BUDURWA
Wannan tana faruwa ne
tsakanin saurayi da budurwa bayan sun haɗu a kasuwa sun yi zance sai ta umurce shi da ya kwana a gidansu kamar yadda
al’adarsu ta nuna. Galibi a kan ba su ɗaki ne su yi hira har dare ya yi ba tare da sun sani ba.Idan ya gane dare
ya yi zai fito, sai ta faɗo wa iyayenta cewa zai tafi. Sai a samu tsofaffi a
gidan su zo su yi masa maganar cewa ya kwana a nan ɗakin mana. Idan dai da gaske yake yana sonta. Ita za a yi
mata magana duk abinda ya dace tayi mashi na so da ƙauna, ka da ta yarda ranshi ya ɓaci. Kuma za su ji abun da ya
gudana tsakaninsu daga tsafin gida. Idan tsafinsu ya kai su
gobe. Shi ke nan sai a rufe su a ɗaki ɗaya su kwana tare har gobe. Amma shi namijin ba zai yarda ya kusance ta ba saboda amincewa da ke
tsakaninsu na so da ƙauna a kan aure, tare da nisanta ga kauce ma abin bautar su bisa ga
dokokinshi. Za su kwanta tare har safiya ta waye ba zai
kula da ita ba, baya ga hirar da za su yi ta yi har barci ya ɗauke su.
Safiya ta waye sannan a buɗe su. Kafin ma su ga ɗiyar tasu, ta faɗa masu abin da ya faru za su iya yanke hukuncin abun da ya faru a
tsakaninsu tun daga jiya zuwa wayewar safiyar yau.
4.5.2 BUKIN WASAN KALANKUWA
Ana gudanar da shi ta hanyar gayyatar juna a tsakanin saurayi da
budurwarsa. Ita ke fara aiko masa da goron gayyata tana mai cewa ya zo wasan kalankuwa a garinsu. Wato babban birnin
ƙasar, nan garin Kwatarwashi don a nan ake gudanar da ita tsakanin ‘yan mata da samarinsu. Za a taru sosai ana ta kiɗan kalangu yana tashi ko’ina a garin
da kewayen shi, kowa zai aika mata da damen hatsi. A ranar da zai zo za a yi
masa gagarumin tarba tare da kayayyakin abinci iri – iri da na sha, a cikin ɗakin da zai kwana a nan gidansu yarinyar. Farko zai gaisa
da ita yarinyar tashi, sai a haɗa shi da yaro don ya gaisa da iyayenta mazansu da matansu. Sa’annan ya dawo masaukin da aka yi masa su ci gaba da hira ko zance da
budurwar tasa. Bayan sun gama zance sai ta koma can cikin gida wurin iyayenta
ta kwana. Shi kuma ya kwana a nan ɗakin, ba za su sake haɗuwa da yarinyar ba, sai idan ya ji ƙarar kalangu yana tashi. Zai tashi ya nufi can dandalin wasan kalankuwa don ya ga mi ke faruwa ne a can. A lokacin da zai je can an riga an taru ƙwarai tsakanin ‘yan mata
da samarinsu, da yara da manya da ‘yan kallo, maƙil a filin. Ita kafin ta je wurin
wasan kalankuwan sai an yi dafe – dafen abinci iri – iri da shaye – shaye,kamar
su tuwo da naman kaji, da na agwagi da zabbi, ga masu hali har da naman ‘yan
kuikuyo da ‘yan awaki, ga fura da nono, ga kuma tulunan giya daban – daban.
Za a raba biyu ne, ɗaya a kaishi can wurin wasar, ɗaya kuma a bar shi nan gidansu yarinyar.Saboda idan ta dawo daga wurin
wasar ita da abokaninta za su taru tare da matan maƙwabtansu a cinye abincin sarai na
murna da wannan buki. Shi ko bayan an tashi taro sai su koma gefe ɗaya daga wurin dandalin wasan kalankuwan su fara hidimar cin abincin. Amma
kafin nan zai isa filin wasan, ya kuma tarar da ana kiɗa, ‘yan matansu suna ta sheƙa rawa. Da zarar an ga samarinsu
tafe, to sai a canza kiɗa da cewa su rinƙa shigowa da ɗai – ɗai. Idan sun fara, duk wanda ya ga budurwarsa ta shiga
rawa zai natsu ya ga shin me zai faru. Tana cikin yi a lokacin da ta ba shi sha’awa a kan gwanintar ta da tayi ta rawa. Sai shi ma ya shiga tare da abokansa suna
rawa, sun kewaye ta. Sai ita ko ta zauna bisa wata kujera da ke nan tsakiyar filin taron, sai ‘yan kallo su riƙa kuwwa da kirari da ihu tare da guɗa.
Bayan sun tafi sai shi ya ci gaba a hankali, ita kuma ta tashi da rawa
sosai har ya tsima, ya fara yi mata kari har sai an zo an jaye shi da ita cikin
filin don wasu su shigo su ma. Ana yin haka don a
tabbatar da cewa fa lalle wance ta samu masoyinta sai jiran lokacin aure kurun.
Amma kafin nan sai uwaye sun shigo kuma an nuna jaruntakar hawan duwatsun don ɗauko maiki daga sama zuwa ƙasan duwatsun magajin Magiro.
4.5.3 SHIGOWAR IYAYE GA SHA’ANIN AUREN MAGUZAWA
Bayan an gama wasan bukin kalankuwa na tsakanin ‘yan mata da samari, duk
uwayensu suna sane da soyayyar da ke gudana tsakaninsu, sai saurayin ya aika a
faɗa gida, wato ga iyayensa game da
abunda ke faruwa tsakaninshi da wance. Ko kuma shi ya je wurin iyayensa da
kansa amma tare da abokansa don ya faɗi cewa shi ya ga ‘yar gidan wane, kuma yana sonta da aure. Maguzawa suna
yin haka ne saboda nuna tarbiyya a tsakaninsu da ɗiyansu saboda akwai kunya.
Zai ce ya ga yarinya ‘yar gari kaza ko ‘yar gida kaza ko kuma gidansu wane
sai a samu tabbatar magana tare da samun yardar junansu. Shi ke nan sai uwaye su taru da na gidansu yarinyar da na saurayin don su tattauna maganar ‘ya‘yansu. Daga nan sai a ba da shedar aure ko kuma kuɗin aure.
Za a kuma kawo kaya a gidansu yarinyar daga gidan su saurayin, sai su yi masu maganar aure don a ba su izini su shigo. Shi ke nan sai shekara ta dawo zuwa hawan duwatsun
tsafin Magiro na magaji don nuna jaruntakar ɗauko maiki daga saman duwatsun zuwa ƙasa.
4.5.4 BUKIN HAWAN DUWATSU DON ƊAUKO MAIKI
Shi ɗauko maiki a ɗauro ma jarumawan samari domin nuna bajinta kan aure, ana
taruwa ne a ƙofar mai garin a ranar da kasuwar
garin take ci. Bayan an taru mazansu da matansu da yara mata da maza da
tsofaffi masu sauran ƙarfi a jika waɗan
da suka san yadda ake gudanar da bukin da aka gada tun
kaka da kakanni. Jarumawan magajin Magiro suna gaba ana biye da su, ana tafe
ana kiɗe – kiɗe da raye – raye da ihu da kuma guɗa tare da kirari da ake yi wa masu son nuna gwanintar a
kan ɗauko tsuntsun nan na maiki daga
saman duwatsun zuwa ƙasansu. Akan ɗaura gashin maikin a kafaɗa tun gida don nuna su ne jarumawan bana.
Bayan jarumawan magaji sun haye sai a ba su umurni da cewa duk samarin su
haye kan duwatsun. Bayan an haye a ɗauro masu maikin a bayansu dukkansu, sa’anan ace kuma su
koma ƙasan duwatsun. Duk wanda ya kai na shi ƙasa to shi ya isa aure, wanda ko bai
samu kaiwa ba sai wata shekara ke nan. A wurin hawa
ana samun mutane masu mutuwa ko kakkarewa idan sun faɗo daga saman duwatsun a wurin hawa ko sauka. Kafin su zo
nan sai an ci an sha ƙwarai, kuma ba za a fara hawa ba sai an yanka ma tsafin Magiro na magaji baƙaƙen bunsura ko ‘yan kuikuyo don ya
sha jini ya sheda. Sai a
je da naman gida a dafe kowa ma ya ci.
Kuma yadda aka je wurin bautar haka za a koma gida da raye – raye da kiɗe – kiɗe da sauransu, har a kai cikin gari. ‘Yan kallo duk suna sheda abun da aka
yi a wurin ɗauko maiki.Tsafin ya yarda wasu su
yi aure, wasunsu ko bai yarda ba sai shekara ta dawo. Daga wannan sai ranar
baiko za a raba goro ga ‘yan uwa da maƙwabta da abokan arziki na anguwanni da ƙauyuka da na garuruwa su
zo don baikon wane da wance. Za a raba goro a ranar za a zo da tabarma biyu daga gidan ango da garin rogo da hura da nono da gishiri.
Ana zuwa da ɗan akuya daga iyayen ango da sauran
kayan ciye – ciye da shaye – shaye da na tanɗe – tanɗe da lashe – lashe da makamantansu.
4.5.5 RANAR ƊAURA AUREN MAGUZAWA
A ranar ɗaurin aure, ga yadda al’adar
Maguzawa take tun kaka da kakanni. Ranar aure galibi akan
sa ranar cin kasuwar garin. Kafin a ɗaura aure ana sa amarya lalle, a yi mata tirgeza a saman turmi. Iyayen ango
mazansu da matansu za su haɗu su ɗunguma zuwa gidan iyayen amarya. ‘Yan uwa da abokan arziki za su wuce wurin
ɗaurin aure a gidan amarya. Suna isa su ma za su ɗunguma dukkansu su fito wajen ɗaura auren wance da wane.
Sai dai wurin zamansu duk ya bambanta da na kowa daga cikinsu, na tsofaffi
daban yake, wurin mata daban, wurin samari da ‘yan mata duk daban suke. Sa’an
nan ƙananan yara nasu wuri daban ne. Sannan ɓangaren ango daban na amarya daban. Kowanensu da
mutanensa daban – daban. Za a kawo tulunan giya
da na hura da nono a cikin tukwane da goruna da ƙwaryayyaki na tuwo daban
– daban. Ga nama iri – iri daga na kaza da zabbi, da agwagi da akuyoyi da na
bunsurra daban – daban, da soyayye da dafaffe da gasashshe da sauran kayayyakin
bukin aure.
Bayan an gama sai a gayyaci kowane ɓangare na ango da na amarya, a samu dattijo ɗaya – ɗaya don su zo a ɗaura aure.
Sai kowanensu ya taso su haɗu a innuwa ɗaya don su
yi barkwancin auren. Za a samu dattijo ɗaya wanda yafi kowa iya barkwanci daga gidan amarya ya
fito da lafuzzan da zai ce, shi ne “Daram” na ɗaura auren wance da wane, in ga masu abu kazar uwa! Ko
uba! Da zai raba! Wurin furta wannan lafazi akwai ɓota da barandami da mashi, sai ya buga su a ƙasa tare yana yin
kirarin tsafin garin zuwa na ƙasa. Shi kenan sai kuwwa da ihu da guɗa tare da kiɗe – kiɗe da raye – raye da sauran abubuwan
jin daɗi.Wasu ma har da zage – zage tare da
wasanni iri – iri.
Bayan haka ana samun wani daga wancan dangin, shi ma ya tashi ya yi ihu ana
cikin raha sai ya
ce shi ne wane ya raba! Wato ya rama zagin da aka yi wa
sashensu saiya kawo nasa dalilan ya zauna. A kawo wani abun kunya da wani dangi
suka taɓa yi, sai a yi ihu a taɓa, tare da kekkewa gabaɗayansu.Sai a koma a yi ihu a
ce shi ke nan. Misali, sata ce ko maita ce, ko kwartanci
ko wani abun kunya ne
na daban. Yana gamawa sai duk taro a ce “i”, to shi ke nan an raba. Ana raba aure nan wurin ɗaura shi idan akwai wani ƙazafi a tsakanin dangin ko amarya da
ango ko wani dalili mai ƙarfi na daban, da sauransu.
Idan an gama za a yi wa amarya wanka a kaita gidan ango. Kafin haka, a
wurin wankan ana yi mata tsirara ne tana bisa turmi, a nan sama ake yi mata
wankan.Ana gabatar da wasu abubuwa da suka shafi tsafi ta samun jajayen zakaru
guda biyu, ɗaya a riƙa kewaya mata a bisa kanta tare da
faɗin
tsafin nasu, ana yi mata ado ne ana sa mata gashin maiki a kanta. Ana
aza ta kan goɗiya ko asa mayaƙan tsafi, jarumawa masu ƙarfi su ɗauke ta su zagaya da ita, in har wurin tsafin gari za a
shigar da ita cikin wani kogo ne na duwatsun garin Kwatarkwashi. Ana ce ma wurin “Kwaman Magiro”. Yana da tsawo ƙwarai, daga nan garin an fita garin
Kura. Masana tarihin garin sun ce “Akwai takobi da mashi da barandami irin na
da, masu nauyi sosai kamar babban dutsi, tare da kwari da baka duk a nan ciki. In ba ƙato, jarumi, majiyi ƙarfi to ba mai iya tallabasu ko ɗaukar ɗaya daga cikinsu. Sai an taru kamar mutum biyar zuwa
goma sannan a ɗauki ɗaya daga cikinsu”.
Wasu kayayyakin ƙasar na tarihi har yanzu wasu na nan cikin “Kwaman
duwatsun”. A cikinshi ne ake gudanar da tsafin aure tsakanin ango da amarya da
kuma na mutuwa. Idan mutum ya mutu sai an kawo shi nan cikin kogo don tsafi ya
shaida mutuwarsa, tare da roƙar mashi zaman shi kaɗai a cikin rami ga tsafinsu na ƙasa baki ɗaya. An ce wani yana ɗaukar aƙalla mutum ashirin (20), a nan ake binciken sirrin amarya, ko wani ya taɓa saninta kafin mijinta. To idan ta taɓa aikata wani abu wanda yake da muni sai a shirya su
tsakaninta da mijinta. In yana sonta sai a rage kuɗin aurenta ta mayar masa da rabi a ɗaura aure. Idan ba ta taɓa sanin wani ba sai ta rantse da tsafinsu na Magiro na
magajin duwatsun Kwatarkwashi. Za a aza ta bisa turmin
tsafin ayi mata surƙullensu tare da yadi guda uku, baƙaƙe da ɗan akuya. Ana kuma ɗaura mata gashin maiki don adon amarya ta shiga bukin
aure.
Za a nemi ƙatta majiya ƙarfi, jarumai, su uku, don su zo da ɗan akuyan nan wanda za a yi tsafin auren da shi.Za a aza shi bisa turmi, ɗaya yana riƙe da ƙafafu biyu da na gaba da na baya, ɗaya zai ɗauko takobin nan na tsafin ko mashin ko barandamin nan domin a sare ko a
kashe ɗan akuyan nan don tsafin ya sha
jini. Idan ya aikata haka amma turmin bai rabu ba to sai ya sake sau ukku in ya
sare, to tsafin ya ci idan ko bai aikata haka ba to lallai ne tsafin nasu bai
yarda da auren ba sai wani lokaci.Idan ya amince to lalle sun zama amarya da
ango ke nan, sai zaman aure.
Bayan wannan gaba ɗaya tsakanin amarya da ango, sai tsafin kai amarya. Bayan anyi na ango, ana
gabatar da shi a washe gari da daddare, za a je a kai ɗan akuya da zakara da tulun giya duk can za a baro su
cikin “Koman dutse”, a koma tun da sassafe, idan an iske an shanye giyar, su ko
zakaran ko ɗan akuyan duk sun mutu to lalle
tsafin ya yarda da auren. Idan ko ba a shanye giyar ba kuma ba su mutu ba, to lalle tsafin bai yarda da auren ba. Sai bayan wata ɗaya ranar kasuuwar garin a sake komawa wurin tsafin.
4.5.6 ZAMAN AUREN MAGUZAWA
Ga al’adar zaman aure na Maguzawa kusan komai mace tana yi a gidan da aikin
daji, da noma, da renon yaran gidan. Ita ke samo ma yaranta abun da za su ci a gidan, ga gyaran abinci kafin a kai ga cin shi. Mazansu ko akwai
shan giya, ga biɗar aure duk shekara har dai ace
kayan gona sun yi kyau ƙwarai, ga su da gudun mutuwa. Yana raba kayan gona kashi biyu ne, ɗaya a kai gida asa rumbu na ruhewa don ci da shayarwa ga
iyalansa. Sauran kuma zai sayar don bukukuwan dangi da yin zawarci domin neman aure.
Matar abun da ta noma ne za ta ciyar da ‘ya‘yanta tare da yin hidimomin yaran
idan ta tashi. Za ta yo itace na sanwa, ta ɗauko ruwa a rafi tare da sauran ayyukan gidan.
Idan miji zai sake yin wata amarya, to duk hidimomin gidan
da ɗawainiyar bukin duk suna ga
uwargida. Za ta yi daɓen ɗaki da ba da nata gudunmuwa na zuwan
amarya. Amarya za ta yi wata biyu ba ta aikin komai. Sai uwargida, tana sa wa ana yi mata aikin
gayya a gonarta.
Shi ke nan sai in zai sake wani aure ita ta biyun za ta yi
wa amarya hidimar ban da uwar gidan. Ga al’adar Bamaguje
bai da iyakar mata sai ya yi ta yi saboda a samu zuri’a masu yawa, ya yi
alfahari ko tinƙaho da cewa yana da yawan mutane kaza.
4.6 BUKIN SUNAN MAGUZAWAN KWATARKWASHI
Maguzawa a wancan lokacin
suna gudanar da al’adunsu na ba su zuwa goyon ciki gidajen iyayensu sai bayan
an yi suna bayan sati ɗaya, wato kwana bakwai kenan, sa’annan mace ta je gidan iyayenta don goyon
jariri.
Za a iya tura mata wata
tsohuwa a lokacin da take can gidan mijin don a kula da ita saboda lafiyarta da
samun sauƙin naƙudar haihuwa. Bayan an haihu lafiya tsohuwar ta wanke jariri da ita mai
jegon a yi mata wanka da ruwan zafi, sai a yanke wa jaririn cibi. Ita kuma uwar
tana shan kunun jego tun daga ranar haihuwa har zuwa wata uku tana yi ba fashi,
don samun lafiyar jikinta da na jaririn ta.
Zuwa wata biyar (5) ta
samu lafiya, idan abin da aka haifa namiji ne ana kashe
masa bunsuru ne a matsayin naman ƙauri don rarraba wa mutane. Ita ma mai jego ta yi shagalinta don ta samu ƙarfin jikinta. Idan mace
aka haifa ana kashe mata ɗan akuya ne don ya zama naman ƙauri na mai haihuwa. Mai jego ba za ta fito waje ba, a
kodayasuhe tana nan a ɗakinta har sai ranar sunan jinjirin ne za ta fara fitowa daga ɗakinta.
A ranar ana yin asubanci
tun da sauran dare a je wurin tsafin garin na wakilin Magiro ko shi tsafin
Magiron cikin kogon duwatsun. A nan za a gudanar da
tsafin jaririn a sa masa gashin maiki a rufe shi ana yanke dabbobi kamar yadda
ake gudanarwa na auren don tsafin ya sha jini ya shaidar da an samu ƙaruwa.
Ita uwar ana roƙa mata lafiya ne tare da
abun da ta haifa a can wurin tsafin. Bayan an gama sai a dawo gida domin a ci
gaba da shugulgulan bukin suna.
A al’ada ba za a faɗi sunan jariri ba, ba wanda ya sani
sai kakanninsa, kuma ba za su faɗa ba sai ya girma ya kai ga aure ko a ranar da za a ɗaura masa aure. A lokacin za a faɗa masa sunansa na ƙwarai. Duk wancan lokacin sunansa na laƙani ne ake kiransa da
irin nasu na kakanni. Haka bukin suna yake gudana a Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi da ke
cikin ƙasar Zamfara.
4.7 BUKIN KACIYAR MAGUZAWAN KWATARKWASHI
Kamar yadda muka sani cewa
dole ne kowace al’umma da irin nata hanyar bukin kaciya. Haka nan Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi suna
da nasu. Suna yi wa ‘ya‘yansu kaciya ko kuidu tun suna da shekara bakwai zuwa
goma (7 – 10). Ana yanka masu bunsuru ko ɗan kuikuyo, daga nan sai a ci gaba da ba shi zabbi da kaji ana kuma sa masu
magungunan gargajiya don ya samu sauƙi ya warke rauninsa da wuri. A al’adance lokacin sanyi
ake yin kaciyar, ba a yi wa yaro wanka sai bayan
bakwai uku, ya warke sosai. Maguzawan Kwatarkwashi na gudanar da tasu kaciyar
kamar haka:
Kyauka wani wasa ne da ake
yi a cikin daji a lokacin da ake yi wa yara kaciya. Kamar yadda Muhammadu Kalgo
(2002) ya ce “Shi dai Kyauka wani aljani ne wanda ake kai wa yara maza idan
lokacin kaciya ya yi domin ya yi masu kaciyar”.
“Rankaratu” da Wudiga su ma wasu gumaka ne waɗan da ake fara kaiwa waɗan nan yara kafin a kai su wurin da za a yi masu
kaciyar ta Kyauka. Kuma Malam Muhammad Kalgo (2002), ya ce “Ana kuma kiran
wannan aljani da ‘yan Kyauka ke tsafi da shi da suna “Mai diyaku”. Lokacin yin
wannan kaciya ne, tun daga lokacin da yaro ya kai shekara tara (9) kuma har sai
adadin yaran da za a yiwa wannan kaciyar ya kai ɗari (100) ko fiye da haka.Kuma ko da yaro zai kai shekara
talatin (30) idan har ba su kai wannan adadin ba, to ba za a yi masa kaciyar
ba.
Za a ɗauki dukkan waɗan da za a yi wa kaciyar zuwa wani daji inda za a yi wa kowannensu bukka,
wanda zai riƙa zama har sai ya warke kafin ya dawo gida. Ranar kaciya za a gayyaci duk
‘yan uwa na nesa da na kusa domin halartar wannan buki na kaciya. Kuma kowa zai
bayar da tasa gudunmawa.Wani bunsuru baƙi, wani jan zakara, kai ga dai su nan. Wasu giya, wasu abinci iri – iri. Bayan an gama kaciyar za a ci gaba da
shagulgula a cikin daji wanda za a ɗauki kwana da kwanaki ana gudanarwa.
Haka kuma, duk wanda zai
tafi wurin wannan wasa, dole ne ya tanadi baƙaƙen kayan sawa. Idan kuma mutum ya yi karanbanin
zuwa da farar sutura, to shi sai dai uwarsa ta haifi wani, domin kuwa nan take
zai faɗi ya mutu. Babu wanda zai san
lokacin da za a
yi wannan kaciya. Gari na wayewa za a ga yaran duk da
kaciyarsu, kuma idan aka tambaye su, su kansu yaran cewa, wa ya yi masu kaciya?
Za
su ce su ma ba su sani ba, sun ganta ne kawai.
Kuma bayan kwanakin da
yara za su yi a cikin daji, wato kwana goma sha huɗu (14), idan lokaci ya yi iyayensu kan tafi domin dawowa
da su gida. Wasu za a tarar sun mutu, kuma iyayen daga zuwansu za a miƙo masu kayan yaran da
suka mutu.
Da zaran an miƙo maka waɗannan tufafi kasan cewa ɗanka ya mutu kenan. Kuma wannan aljani wanda ya yi masu kaciya, wato Kyauka, shi ne ke tsaronsu, abincinsu da abin shansu
duk suna hannunsa.
Lokacin da iyayen waɗannan yaran suka tafi domin su dawo da su gida, za su
shaida wa Kyauka cewa yau za mu tafi da ‘ya‘yanmu gida. Shi kuma zai ce “a’a” bai yarda ba sai fa idan an yi alƙawarin ba shi ɗaya a matsayin ladar aikinsa. A nan ne za a ƙulla alƙawali da iyayen waɗannan yara, su ce za su ba shi, amma sai sun kai
bakin garinsu.
Shi zai amince kuma ya bi su har bakin garin inda zai tambayi alƙawalinsa. A nan ne fa ake jani – in
– jaka sai sun kai ga jifarsa da duwatsu har zuwa nesa da gari, kana ya koma
yana mai cewa “ba haka muka yi da ku ba. Amma tun da kun yi mani haka, to Wudiga ya saka da alheri (wato maimakon Allah ya
saka da alheri)”. Kamar dai yadda aka riga aka ambata cewa Wudiga gunki ne na
tsafin Maguzawa.
Idan sun isa gida, wanda
ke da mata a cikin su ‘yan kaciyar zai tafi ɗakin matarsa, wanda ba shi da mata ya yi ɗakin uwarsa. A nan kuma za a sake ɓarkewa da shagulgula na murnar ganin ‘yan kaciya sun dawo
lafiya.A yi ta dafe – dafe da ciye – ciye da shaye – shaye da makamantansu.
4.8 BUKIN MUTUWAR MAGUZAWAN KWATARKWASHI
Maguzawa suna da hanyoyin
al’adunsu na rayuwa bisa ga tsarin bautar tsafin Magiro. Akwai bukukuwan mutuwa
wanda Maguzawan Kwatarkwashi ke gudanarwa, idan mutum ya mutu ga yadda suke
gudanar da bukin kamar yadda suka gada tun daga kakanninsu:
Idan mutuwa ta kama su, ta
hanyar rashin lafiya ne ko wani haɗari ko ta hanyar faɗa ne ya mutu, in ya bar iyali da yawa to lalle za a yi masa shagulgulan
bukin mutuwarsa tare da yin kiɗe – kiɗe da raye – raye. A samu taruwa
wurin bukin tun daga kakanni da iyaye da matan da ‘yan uwa da ɗiyansa da jikoki da maƙwabta, tare da abokan arziki duk sun
hallara a bukin mutuwarsa.
A lokacin da yake rashin
lafiya ana sa masa wani dattijo ya dinga diba shi don jinya tare da ba shi
magungunan warkewa. Idan bai samu warkewa ba ya kai ga
mutuwa, shi zai shafe masa idanunsa da ruwan magani a kuma yi masa wanka da su don
kada ya ruɓe zuwa kwana uku kafin a je wurin
rufe shi.
Ba za a gayawa kowa ba sai bayan kwana uku, a lokacin za a gaya wa mutane
cewa wane fa ya mutu, ya zama babu.Wato wane, ya riga mu, wane ya yi kasala bai
jure ba. Za a ɗauko gawarsa zuwa wurin tsafin
Magiron don ya shaidar da cewa lalle ya mutu ne. An samu ragowa ne, don haka sai a kashe ko a yanka masa daga cikin dabbobin
da za a yi bukin mutuwa da su. Ana zuwa da tsofaffi da matsakaita da masu ji da
kansu da ƙarfi ƙwarai wato jarummai samari. Za a kai shi cikin kogon duwatsun ne wasu na
kuka, wasu na ihu da shewa da kyakkewa, tare da guɗa, ana tafi da baƙaƙen bunsura da kuikuyo da kaji duk uku – uku, waɗan da za a kashe wa tsafin don ya sha jini, tare da
tulunan giya da hura da nono da sauran kayan bukin mutuwa.
Bayan an dawo daga wurin
tsafin ana tafe da kaɗe – kaɗe da raye – raye da bushe – bushe za
a je can bayan gari wurin rufe shi ana ta ihu da kuka da kyakyewa, ana tafi ana
zuba masa ruwan giya. Za a ajiye shi a ƙasa a gina inda za a sa shi ciki. Ana bulbula masa giya a bakinsa da jikinsa. Bayan an sa shi, kafin a rufe
shi za a yi masa gargaɗi kamar yadda suka saba kamar haka:
“In ka je
ka ce kai kaɗai ka rage!
Kai kaɗai ne ba sauran kowa!
Babu sauran
kowa a sararin ƙasa!
Kuma ga ka nan
ka taho!
Babu kowa duk
sun ƙare!
Babu kowa ne?
Duk sun koma!
Bayan an gama sai mutane su ce:
A she wane ya
yi kasala!
Wane bai jure
ba, ya yi kasala!
Ai wane bai
jure ba!
Bai jure ba!
Ya kasa!
Bayan an dawo da kaɗe – kaɗe da raye – raye da sauran shagulgulan da ake yi na ciye – ciye da shaye –
shaye da sauran hidimomin bukin mutuwa da aka gudanar,za a ci gaba har kwana
bakwai. Ranar da za a yi bukin sati ɗaya bayan na kwana uku da aka yi sai a jira na kwana arba’in (40).
Bayan kwana arba’in (40)
ana sake gudanar da bukin mutuwa, za a sake taruwa kamar yadda aka yi na farko
a yi shaye – shaye da kaɗe – kaɗe da raye – raye ga kuma shagulgulan
abinci irin su tuwo da nama, sai dai ba za a shiga ɗakin mamacin ba sai ya kwashe shekara a kwance. Bayan an
je an dawo sa’annan a fara shigarsa, ana iya ba wani cikin danginsa ɗakin ya zauna.
Bayan bukin kwana arba’in
sai na juya kafaɗar gawar don cika shekara ɗaya da mutuwa.Akan yi shi ne idan ya shekara ɗaya, amma idan mutum ba ya da hali yana iya bari har ya
samu sannan a yi.Wato a bisu bashin bukin mutuwar kenan. Wannan shi ne bukin
gawa na ƙarshe wanda daga gareshi ba wani sauran bukin mutuwa. Don haka ga masu arziƙi za su ɗebe kunya ga ‘yan uwansu, za a taru kamar yadda aka saba taruwa har wannan
taron ma sai ya fi sauran domin wannan shi ne babban bukin mutuwa. Za a gayyaci mutane tun daga unguwanni, da ƙauyuka, da garuruwan ƙasar Kwatarkwashi masu bautar tsafin
Magiro magajin duwatsun.
Za a yanka duk dabbobi nan
a cikin raminsa, bayan an fito da su kafin a ajiye su ana faɗin waɗan da suka kawo mishi kayan bukin mutuwa, ana kwara wa raminsa giya, daga nan sai kirari kamar haka:
“Tsoho ka
kwanta lafiya!
Mun gode ma!
Mun gode ma
arzikin ka!
Mun gode ma
tsafin Magiro!
Mun gode ma
kwanan Magiro ta magaji!”
Bayan haka sai shugaban
tsafin ƙasar Kwaarkwashi ya ce magaji jikan Magiro ya amsa!
“Kwanta lafiya
in ji Magiron magaji!”
Daga nan sai a dawo gida a
ci gaba da shagulgulan mutuwa har zuwa kwana uku ana yin bukin. Sai a kira matan mamacin ko su nawa ne don su yi rawa ta al’adar mutuwa, ana
yi masu kiɗa da kirari. Daga nan sai a raba su
zuwa ga manyan abokansa, don su matan ba su da gadon komai na dukiyar da ya
bari, sai ɗiyansu ke da wannan gado.
4.9 HANYOYIN GARGAJIYA NA MALLAKAR MACCE A MAGUZANCE
Akwai hanyoyi masu yawa da
Maguzawan ƙasar Kwatarkwashi ke mallakar macce kafin a ɗaura masu aure da ita kamar haka:
i.
Neman Aure: A na
mallakar mace ta hanyar neman aurenta bias ga yarjejeniya ta magabatan miji da
mata.
ii.
Yaƙi: A na mallakar mata ta hanyar yin yaƙe – yaƙe tsakanin wani gari da wani, ko wata nahiya da wata,
idan wani ya ci wani gari da yaƙI sai auratayya ta shiga tsakani.
iii. Samame: A na
mallakar mace ta hanyar samame. Wannan wata dabara ce ta mallakar mace ta hanyar kawo ma gari samame lokacin da masu garin suna
gonaki ko kuma a yi samako.
iv.
Hari: A na mallakar mace ta hanyar kawo hari a cikin gari, wanda shi wannan hari
yana kasancewa a taso ma gari kai tsaye.
v.
Tsintuwa: A na mallakar mace ta hanyar tsintuwa sai ta zama matar mutum.
vi.
Bashi: A na mallakar mace ta hanyar bashi tsakaninta da mijinta ta hanyar
yarjejeniya.
vii.Saye: A na mallakar mace ta hanyar saye a wancan lokacin da
akwai bayi. Sai mutum ya tafi ya sawo baiwa ta zauna a matsayin matarsa.
viii.
Kyauta: A na mallakar mace kyauta ta hanyar uwayenta su ba da ita ga wani
sadaka, a matsayin aure gare shi.
ix.
Kwartanci: A na mallakar mace ta hanyar kwartanci, ko shige, ko tsallaka katanga.
Wanda zai iya kasancewa da yardar mace ko kuma babu.
4.10 LALACEWAR MAGUZANCI A KWATARWASHI
Lalacewar Maguzanci a ƙasar Kwatarwashi ta faru ne ta dalilan:
·
Zuwan Turawa
·
Shigowar baƙin haure
·
Samuwar ilimin boko da
tsarin yankuna
Mutanen garin Kwatarwashi yaransu da manyansu sun taka rawa wurin biɗar ilimin addinin Musulunci ƙwarai da gaske. Ba don komi ba sai don su gane addinin gaskiya. Su bar bautar tsafi a yankinsu. Saboda zaman shi
addinin gado tun daga kakanninsu aka fara shi zuwa lokacin da suka bar shi zuwa
ga addinin gaskiya. A kan haka ne kuwa aka samu karkato mutanen da su dawo ga
kaɗaita Allah tare da yarda da Annabin
Allah wanda Allah, ya aiko masa da manzanci shi ne Annabi Muhammad (S.A.W). Tare da neman gafarar Ubanhiji Maɗaukakin Sarki Allah bisa abun da suka aikata na bautar tsafin Magiro.
Duk da haka har yau akwai masu bin bautar tsafin Magiro na magaji, sai dai
sun ragu ƙwarai don ‘yan kaɗan ne suka rage. Daga baya masu zuwa wurin bautar tsafin Magiron su ma duk
sun matsa can cikin daji. Sai dai suna zuwa a duk shekara in ta
yi don zuwa bautarsu na aure ko haihuwa ko na mutuwa.
Bayan haka, addinin Musulunci ya ci gaba da yaɗuwa ƙwarai har aka kai ga samun maluman addinin Musulunci don
su yaɗa ilimin bauta ma Allah sosai. Ga kuma masallatai a cikin garin da kewayen garuruwan ƙasar Kwatarkwashi. A sanadiyyar haka
ne aka samu ɓalɓalcewa ko lalacewar bautar tsafin Magiro a garin
Kwatarkwashi, daular ƙasar Zamfara a shekara ta (1804/05) a ƙarni na sha tara.
4.10.1 ZUWAN TURAWA GA MASU BAUTAR MAGIRO
Bayan jihadin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ya zama abu na farko wurin ɓalɓalcewar bautar tsafin Magiro ga Maguzawan Kwatarwashi a shekara – shekara;
sai wasu suke komawa ga wancan bautar tsafin Magiro na addinin gargajiya na
gado. Ana cikin haka, sai ga Turawan mulkin mallaka sun ɓullo ƙasar Zamfara bayan hijirar sarkin musulmi Attahiru na ɗaya, a sanadiyyar
yaƙe – yaƙen da ya yi na musulunci a kan turawan mulkin mallaka. Masu son kame ƙasar Hausa su mai da ita ga mulkin da ba na Musulunci ba. Don su kauda
mulkin addinin Musulunci suka ɗauro yaƙi tun daga ƙasarsu ta Ingila zuwa nan ƙasar Hausa Daular Usmaniyya. A zuwansu sun ya da zango ne
a garuruwan Hausawa da yawa kafin su iso cibiyar Daular Usmaniyya a garin
Sakkwato. Sun fara aje sansaninsu a garin Zuru da Yauri da Birnin Kebbi da
Kwatarkwashi. A sanadiyyar wannan zaman suka yaɗa nasu addini na Kiristanci don suna taimaka masu ta
hanyar abinci da sha da sutura da kuma kula da lafiyarsu da warkar da kutare,
da makafi, da guragu da masu ciwon inna, musamman ma na garin Kwatarkwashi.
Bayan sun gama yaƙin daular Usmaniyya, sai suka koma wuraren da suka fara zama don sun gano
ba su da addini sai na gargajiya suke bi. Masu tasiri musamman ma ga garuruwan
da ke kewaye da duwatsun sun yi masu gine – ginen gidaje da wurin bautarsu
“chochi”. Turawa sun ci gaba da ba mutanen garin kuɗi tare da kayan sana’o’i a kan noma da kiwo da sauran ƙere – ƙere na gargajiya. Da haka suka yi sanyi ga addininsu na gargajiya. Sai dai mabiya addinin gaskiya suna nan cikin Musuluncinsu ba ja da baya.
A
kan haka addinin Kiristanci ya yi tasiri ga wasunsu sosai. Dangane da haka na ce lalle a nan ma saboda samun addini biyu a ƙasar, to fa bautar tsafin ya ɓalɓalce ƙwarai da gaske. Turawa sun shigo yaɗa addinin Kiristanci a ƙasar Hausa ta daular Usmaniyya tun daga kudanci zuwa
arewacin Nijeriya, don sun zo ne ƙarƙashin su koma ƙasa ɗaya, ƙarƙashin addininsu na Kiristanci a shekara ta (1903) bayan sun samu wurin
zama.
4.10.2 RUSHEWAR BAUTAR MAGIRO
Bayan masu mulkin mallaka Turawa sun ba da nasu gudunmawa ga masu bautar
tsafin Magiro. Sai Allah Maɗaukakin Sarki ya ba su Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato firimiyan jihar
Arewacin Nijeriya mulkin ƙasar nan. Shi ma ya taka rawa sosai don ganin cewa
mutanen Kwatarkwashi masu bin addinin Turawa da na bautar tsafin Magiro na
gargajiya duk sun dawo ga na Musulunci, addinin gaskiya. Don haka, gwamnatin
Sardauna ta taimaka ma mutanen garin ƙwarai da gaske. Daga nan aka samu shigowar baƙin haure da suka shigo a
sanadiyyar aikin jirgin ƙasa daga Zariya zuwa Gusau har wucewa Ƙauran Namoda a shekara
ta (1920 – 1929).
Saboda haka gwamnatin arewacin Nijeriya ta Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato
ta taimaka wajen dawo da martabar addinin Musulunci, musamman ma garin
Kwatarkwashi, a ƙarƙashin Jama’atun Nasarar Islama (J.N.I), ta Nijeriya ta samu ‘yancin kanta
daga Turawan mulkin mallaka na Ingila a shekara ta (1960). To nan ma tsafin
Magiro da Kiristanci duk sun rage ƙarfi sosai, amma bautar tsafin Magiro shi kan ya watse
saboda gaskiya ta bayyana “ƙarya ko dole ta dushe,” sai Musulunci addinin gaskiya.
4.10.3
TASIRIN ILIMIN BOKO GA RUSHEWAR MAGIRO
Samuwar ilimin boko ya yi tasiri ƙwarai a garin Kwatarkwashi don ya taimaka wurin ɓalɓalcewar addininsu na gargajiya wato “Bautar Tsafin Magiro”. Turawan Ingila
da suka zo yankin ƙasar sun gane cewa ba su da wani addini sai na gado, wanda ya yi tasiri ga wasun su a shekara ta (1960 zuwa 1968). A kan haka suka taro
mutanensu don son yaɗa addinin Kiristanci sai suka zauna a gefen gari suka ba da abinci iri –
iri da tufafi da kuɗi tare da taimaka masu a fannin kiwon lafiyarsu ta hanyar ba su magunguna
da gidajen zama da asibiti da chochinsu ta addinin Kiristanci.
Ba a an karo ba sai mutanen ƙauyukka da garuruwan Kwatarkwashi suka yi ta komawa
addinin Turawa, amma ban da babban birnin garin. Shi kam yana nan cike da masu
bin addinin Musulunci sosai. Sai dai duk da haka masu zuwa yin bautar tsafin
Magiro ‘yan kaɗan ne, har lokacin mulkin Alhaji
Shehu Aliyu Shagari, Turakin Sakkwato a shekara ta (1979 zuwa 1983). Bayan
janar Olushegun Obasanjo ya ba shi mulki har zuwa juyin mulkin da aka yi masu
wanda janar Muhammadu Buhari Daura ya yi, a shekara ta (1983 - 1985). A wannan lokaci da Burgediya Garba ke
gwamnan jihar Sakkwato aka sa doka da ta hanasu zuwa bautar tsafin Magiro na
shekara. Masu zuwa kamo maiki a saman duwatsun don nuna jaruntakar tsafin duk an ce
su bari. Sa’an nan ita ko ƙungiyar Izalatul Bidi’a Wa Iƙamatus – sunna (JIBWIS) ta taimaka ƙwarai wajen yin wa’azi
na Musulunci ga mutanen da aka hana, to da yawa kuwa sun dawo ga Musulunci.
Duk da haka ba su rabu da yi ba sai shekara ta (1987 zuwa 1989), a nan ne
aka sake hana su a lokacin gwamnan mulkin soja na Sakkwato Ahmadu Daku. A
wannan shekara ne fa ta faru ta ƙare, saboda suna cikin yin hidimominsu na bukukuwan aure
da ake hawa duwatsun bautar tsafin. Ga ‘yan kallo sun taru ana kiɗe – kiɗe da bushe – bushe tare da kirari da waƙoƙinsu, ga kayan shaye – shaye nan da
ciye –ciye kamar yadda suka gada. Bayan an fara hawan duwatsun, duk samarin
jarumawa da za a ba sun haye an kuma fara ɗauro masu tsuntsun maiki a bayansu don su sauko da shi ƙasan duwatsun daga saman
su, wasu daga cikinsu sun kai ƙasa, a nan aka samu wani tsuntsun maiki ya farka daga
barci, sai ya tashi da wanda aka ɗaura ma shi a baya, ya yi sama da shi sosai. Aka yi ta kallonshi, bai
yiyuwa a harbe shi tunda tare da mutum yake ɗan uwansu, sai ya dawo saman duwatsun. Shi ke
nan da mutumin da tsuntsun maikin ba a gane namansu duk
sun fashe. Shi ke
nan sai aka bari baki ɗaya, aka bar zuwa bautar tsafin. Ta haka ya lalace babu shi. Sai suka koma Kiristanci a chochi, saboda
zaman Turawa a garin aka fara yin makarantar boko a shekara ta (1940 zuwa 1945).
Kafin yaƙin duniya na biyu da bayanshi a yankin ƙasar Zamfara.
An samu tsarin yankunan jahohi da ƙananan hukumomi a lokacin mulkin soja Janar Yakubu Gawon
a shekara ta (1967 zuwa 1975). Sai Janar Murtala Ramat Muhammad (1975 zuwa 1976), zuwa lokacin Alhaji Shahu Shagari a shekara ta (1979 zuwa 1983). Waɗan nan shuwagabanni su ne suka ƙirƙiro da yankuna da jahohi da ƙananan hukumomi don ba
da ‘yanci da ci gaban hukumomi tare da matsowa da mutane kusa da gwamnati. Daga
waɗancan shekarun zuwa lokacin mulkin
soja na Janar Ibrahim Badamasi Babangida a shekara ta (1991) duk garin
Kwatarkwashi yana ƙarƙashin ƙarmar hukumar Gusau. Sai a wannan shekara aka mai da shi ƙarƙashin ƙaramar hukumar Bunguɗu har zuwa yanzu.
Bayan wannan, a shekara ta (1996), lokacin mulkin Janar Sani Abacha aka ƙirƙiro jihar Zamfara saboda kusantowar
gwamnati ga jama’a, a yankin garin Kwatarkwashi. An yawaita kiraye – kirayen jama’a ta
hanyar wa’azi da hanyoyin addinin Musulunci ke yi ga masu biyar addinin
gargajiya da Kiristanci.
Bayan an yi siyasa, Allah Maɗaukakin Sarki mai Sarauta ya ba Alhaji Ahmadu Sani Yariman Bakura mulkin
jahar Zamfara a matsayin gwamna, a shekara ta (1999 zuwa 2006), ya ƙaddamar da shari’a bayan
ya shekara ɗaya da hawa mulkin. Wannan ƙaddamar da shari’a ta yi
tasiri ƙwarai, musamman ma ga mutanen Kwatarkwashi waɗanda ke zaune a saman duwatsu. A farkon shekara ta
2001(25/1/2001) aka samu mafi yawan garuruwan masu bin addinin Kiristanci tare da
fastocinsu suka koma addinin Musulunci ta hanyar wa’azin gari da gari na jahar Zamfara zuwa lunguna don isar da saƙon Musulunci. Don haka ana iya cewa, Allah Shi ja zamanin
gwamnan jahar Zamfara, Ya ba shi haƙuri da juriya ga ‘yan uwanshi Musulmai, tare da taimaka
masu ci gaban addininsu baki ɗaya.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.