Ticker

6/recent/ticker-posts

Tsafe–Tsafen Maguzawa: Nazari A Kan Bukukuwan Maguzawan Kwatarkwashi (1)

Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu Jami’ar Tarayya Gusau.

Tsafi

Tsafe–Tsafen Maguzawa: Nazari A Kan Bukukuwan Maguzawan Kwatarkwashi (1)

NA

ABDURRAHMAN LAWALI

SADAUKARWA

Na sadaukar da wannan aiki ga mahaifana, Alhaji Lawali Jamalu Rawayya da Hajiya Hassi ‘Yan dotondaji da kuma abokina Jafar Usman Badarawa.

GODIYA

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Maɗaukakin Sarki Mai kowa Mai komai, tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban talikai kuma cikamakon Annabawa, Annabi Muhammad (S.A.W). Cikin ikon Allah da yardarSa da amincewarSa Ya ba ni ikon kammala wannan aikin bincike, domin samun takardar shaidar kammala digiri na farko a sashen koyar da harsuna da al’adu, a Jami’ar tarayya Gusau, jihar Zamfara.

Bayan haka, ina miƙa godiyata ga mahaifana a kan ɗawainiyar da suka yi da ni tun yarantata har zuwa wannan lokaci da na  kammala karatun digirin farko. Allah Ya saka masu da mafificin alherinSa. Haka kuma ina mai nuna godiyata da farin cikina ga malamina wanda ya yi ɗawainiyar duba mani wannan aiki, watau Malam Aliyu Rabi’u Ɗangulbi bisa umurni da shawarwari da ya bayar, Farfesa Balarabe Abdullahi kan irin taimako da shawarwari da ya bayar don ganin na samu nasarar kammala wannan bincike. Allah ya saka masu da mafificin alherinSa.

Har wa yau, Ina miƙa godiya ta musamman ga malamaina Malam Musa Abdullahi Zariya, da Malam Adamu Ibrahim Malumfashi, da Malam Isah S. Fada a kan irin taimako da shawarwari da suka ba ni, domin ganin wannan aiki ya kammala. Allah Ubangiji Ya saka masu da Aljannar Firdausi. Sauran malaman da ba a ambaci sunayensu ba saboda ƙarancin lokaci, ina yi masu godiya bisa taimakon da suka ba da domin cimma nasarar kammala wannan aiki. Har wa yau ina miƙa godiya ta musamman ga Shugaban Sashe, Farfesa Aliyu Muhammad Bunza, da Farfesa Magaji Tsoho Yakawada, da Dr Yakubu Aliyu Gobir da Dr. Abdullahi S. Gulbi da sauran malaman da suka koyar da ni har na kai ga samun nasarar kammala karatuna. Allah Ya saka masu da alherinSa.

Godiya ta musamman ga yayannina Basira Lawal da kuma Bela’u Lawal da ƙannaina Bashar Lawali da Habiba Lawali bisa shawarwari da ɗawainiyar da suka yi da ni har zuwa kammalar wannan karatu nawa.

Bayan haka, ina miƙa godiyata ga abokan da na yi karatu da su kamar su Jafar Usman, da Shafa’atu Salihu Labbo, da Bashiru Haruna, da Aminu Murtala, da Umar Yahaya Dogara, da Bilya Umar, da Sadiya Kabir Sama’ila Aliyu, da  Mukhtar Muhammad da sauransu,waɗan da lokaci bai ba da damar lissafawa ba. Allah Ubangiji Ya sakawa kowa da alherinSa, Ya sa Aljannar Firdausi ta zama makoma a garemu baki ɗaya.

Ba zan manta da Yunusa Aliyu Guraguri ba, wanda ya ɗauki lokaci dare da rana wajen buga wannan aiki cikin na’ura mai ƙwaƙwalwa da kuma sauran mutanen da suka ba da tasu gudunmuwa ta kuɗi ko ta kayan aiki. Ina fatar Allah ya yi wa kowa sakamako na alhairi, ya kuma sa wannan aiki ya zama jagora ga duk wani mai bincike ko nazarin tarihin Maguzawan Kwatarkwashi amin.

Ƙarshe ina miƙa godiya ta musamman ga malam Aliyu Rabi’u Ɗangulbi bisa ga ɓata lokacinsa da ya yi wajen dubawa da kuma gyare – gyare da ya yi na wannan aiki. Allah ya saka masa da alhairinsa, ya albarkanci zuri’arsa amin.

Post a Comment

0 Comments