Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsuna da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.
Ganuwar Gusau Da Kofofinta (4)
NA
UMAR YAHAYA DOGARA
BABI NA UKU
GANUWAR GUSAU
3.0 Shimfiɗa
A babin daya gabata,
watau babi na biyu binciken ya duba ayyukan da suka gabata a wannan fanni,
musamman waɗanda
suke da ganuwa da ƙofofi. Ban samu wani kundin da ya yi bayani akan, ko
nazari gane da ganuwar Gusau da ƙofofinta ba, wannan baba zai yi bayani akan,
ganuwar Gusau, watau tarihin Gusau da kuma tarihin ganuwar Gusau da tasirin
ganuwa a (gari) da nadewa, wato wanna shine maƙasudin wannan babi.
3.1 Tarihin Gusau
Allah Ubangiji ya yi halitta ya
halici jam’a daban-daban, ya kuma zaunar da halittunsa a ƙasashe
daba-daban da kuma wurare, daban-daban, kuma ta haka ne Allah ke azurta bayinsa
kuma ya ni’imtar dasu, da abubuwa da yawa, wanda za su yi amfani da su a
rayuwarsu ta duniya.
Gusau ƙasace mai tarin
albarka kuma Allah ya ni’imta ƙasar da arziki, da jama’a hazikai, tun a
zamanin da har zuwa wanna zamani. Gusau na da sunan da ake mata kiraru dashi
“Gusau ta Malam Sambo Kwazo Gusau abinai ya Gusa” wannan kirarin ƙasar
garin Gusau wanda yana da ɗaɗɗaɗen tarihi, tin kafin
yaƙin
kafa daualar Musulunci, wanda shaihu Usman ɗanfodiyo ya yi. Gusau dai tun a zamanin da ƙasace
mai ɗinbin
tarihi domin ƙasar ta yi fice wurin sha’anin tafiya da mulki da
kasuwanci; da aikin noma da masana addini Musulunci.
Gusau dai ta samo asalinta ne daga
kalmar Hausa watau (Gusau) wanda Hausance ake nufin mutum ya matsa, ko kuma
kamar a ce mutum ya dan ƙara tafiya gaba ko ya matsa a nan, dai ya
danganta ga yadda mutum ya fahimci kalmar Gusau a hausance. (Gusau ta Malam
Sambo 2012).
A shekarar (1811) kimanin shekara (207)
da suka gabata bayan tasow a daga garin “Yandoto” a shekar (1806). Garin Gusau
yana ɗaya
daga cikin manyan garuruwan tsohowar jahar Sakkwato wato, kafin daga bisani ya
zama babban Birnin Jahar Zamfara a shekara (1996). Garin Gusau yana kan titin
Sakkwato zuwa zariya ne, kimanin kilomita (179) kilimita (2010) tsakanin su da
Sakkwato. Daga gabas garin Gusau ya yi iyaka da kasar Katsina da kwatarkwashi,
daga arewa kuma yayi iyaka da Ƙaura-Namoda, a ya yin da ya yi wata iyakar da
garin Bungudu, daga Yamma a aЪan garen kudu kuma ya
yi iyaka da Ɗansau.
Almajirin Shaihu Usman Ɗanfodiyo
ne, watau Malam Sambo ɗan
Ashafa, ya kafa Birnin na garin Gusau wanda yake shi da jama arsa. Wajaje
shekarar (1214H/1799M). Kafuwar wannan garin Gusau ta faru ne a Sakamakon umurnin
da Shaihu Usman Ɗanfodiyo ya bai wa Malam Sambo da jama’ar su, bayan da
“Yandotawa suka bi su da bakar yadiya, har sunka yi yunkurin kasha shi Malam
Sambo inda aka kasha wani maharbi wanda ya bashi kariya. Malam Sambo Ɗan
Ashafa da jama’rsa. Sun rike wanan sabon wurin nasu, matsayin wurin ribadi,
wato cibiyar da zasu ci gaba da neman ilimi da bayar dashi, da kuma
shirye-shiryen yaƙar ‘Yandotawa, domin kuwa hijirar da suka yo daga
‘Yandoto ba ta sa sun tsira daga makircin mutane garin na ‘Yandoto ba, na ƙoƙarin
shafe hasken addini Musulunci a ƙarƙashin jagorancin Shaihu Usman Ɗanfodiyo.
Malam Sambo Dan Ashafa da jama’ar sa sun sami nasarar kammala waɗannan shirye-shirye
na yaƙi a cikin tsawon shekaru bakwai. A shekarar
(1121H/1806M). Allah ya basu nasarar cinye ‘Yandoto da yaki a cikin dan
kankanin lokaci, bayan yaƙin Alwasa (Gusau da Gusau:1984)
Wannan nasara da Malam Sambo, da
jama’ar sa suka samu kan ‘Yandotowa bata basu dammar mike kafa su zauna lafiya
a sabon garin su na gusau ba, domin kuwa ‘Yandotawa da uwayen gidansu da magoya
bayansu basu saki kariba, sai suka ci gaba da ƙoƙarin
yi wasu Malam Sambo kumun kazar kuku, wanda a sakamako haka ta sa, suka zauna a
garuruwa da dama, kamar, sabuwal 1806 zuwa 1807, sanan shekara 1807 suka koma ‘Yar Gusau da garin cideya
1807 zuwa 1811, bungudu 1818-1820 da kiyawa, da Banga 1820-1822, sai kuma suka
koma Birnin Kamani, duk a cikin ƙasar Ƙaura Namoda suka
shekara ɗaya
daga, 1822 zuwa 1823. Daga nan kuwa Malam Sambo Dan Ashafa, ya kafa garin
Wonaka inda ya shekara hudu a Wonaka, sannan Allah kuma ya karЪi rayuwar sa shekara 1827.
Bayan rasuwar Malam Muhammadu Sambo,
sai sarkin Musulmi Muhammadu Bello ya nada babban ɗansa, Malam Abdulƙadir a shekara ta
(1827), duk a Wonaka suka ci gaba da zama garin Wonaka har zuwa (1860) inda
suka bar garin wonaka, suka koma garin Rawayya, suka shekara biyu 1860-11862 da
jama’arsa a Birnin Rawayya, a shekara 1862, suka share wuri suka yi tajadid ‘Yan bukko kinsu da Masallaci , daga
wannan lokaci mutane Gusau suka mike kafa basu sake zuwa ko’ina ba, domin sun a
iya kare kansu daga kowace irin barazana da kuma mugunta.
Bayan kafa garin Gusau da Malam
Muhammadu Sambo Ɗan Ashafa, shine Sarkin na farko, kuma shine ya sara
garin Gusau, daga baya an yi ta yin sarakuna da dama tun daga wannan lokaci har
yau. Bayan rasuwar Malam Sambo Ɗan Ashafa, Ɗan sa Malam Abdulkadir
ya gaji wannan sarautar ta Sarkin Katsinan Gusau, garin Gusau yana ɗaya cikin sababbin
garuruwan da aka kafa waɗanda
suka maye tsofaffin garuruwan da aka samar shekaru da dama da suka shude, kafin
jihadi, kamar Birnin Alkalawa da Kiyawa
da Birnin Samari da Birinin ‘yandoto da suaran su. Almajiran Shaihu Ɗanfodiyo
suka kafa garin Gusau.
3.2 Tarihin Ganuwar Gusau
A lokacin da mutane
Gusau suka sami zama a garin Rawayya, suka ga kuma sun yi ƙarfi
sai suka shirya tsananta wa mutane garin Rawayya suka hana su sakat, harta kai
idan Rashin hakimi Rawayya ya sa ake yi shela, sai su kuma su yi tasu shelar,
su warware abin da mutanen garin Rawayya suka yi shawarar abin da Rashin ya
umarta da aikata. Daga nan sai mutanen garin Rawayya ruka yi shawarar hanyar da
za su bi don su fitar da su daga garin su, wani daga cikin su yace, tun da ba
mu iya cin su da yaƙi, ba abin da zai sa su bar garin an sai gori, A bari sai
Sarkin yakin su ya fita kilisa bayan
gari a rufe kofofi, in ya yi Magana a mayar masa dab aka. Suka shirya da haka,
kowa ya yarda da wannan shawar (Hira da M.M.
da ƙungiyar mutane a 1976 da M.M.W da ƙungiyar
mutane a 1978).
Bayan wannan shawarar
rannan sai sarkin yaƙi Salihu Ɗan Kambo cikin
mutanen Wonaka ya fita kilisa da marece. Ko daya dawo, sai ya tara da an rufe
dukkan ƙofofin kowace ya zagaya, sai ya tarar da ita a kullace.
Daga nan ya koma ƙofar da sarkin ƙofa yake zaune, ya
nemi ya buɗe
masa yaƙi, illa ya ce masa “kai ku gudu ku ba mu wuri na ki bude ma, ai ga kangon uwayenku can kun baro kun zo
nan gari wasu kuna kaba” wannan jawabi na Sarkin ƙofa ya yi wa Salishu Ɗankambo
zafi, sai ya cewa Sarkin ƙofa “ka gaya wa duk wanda ke cikin zuriyarmu
ya isko ni kangon uwayen namu gobe da safe, ni na tafi” Sarkin yaki Salihu Ɗankabo
ya kuma tafiya tar da zagin sa har suka isa tsohon wurin nan nasa na farko,
suka kwana a nan (Hirar da M.A.D ya yi da kungiyar mutane 1976) kuma yana gabin
sun yanke shawara su sanya mutane su dinga yi masu najasa a bakin ƙofofin
bukko kinsu, kuma idan sallah karama ta zo su riga su zuwa idi, idan suka fita
daga baya. A rufe masu ƙofofi haka kuwa ta faru, lokacin da Sallah
karama tayi, sai mutanen garin Rawayya suka shirya tun da wuri, suka fita suka
yo sallar idinsu. Da mutanen Gusau da na Wonaka suka ce masusu fita zuwa idi,
sai suka mayar masu da cewa har sun gamo tasu sallah. Don haka, da jama’ar
Sarkin Kastina Abdulkadir suka fita zuwa idi, sai mutanen garin Rawayya, su ka
rufe kofofin su. Suka nemi a bude masu, aka kiya har ma dai suka yi masu gorin
das u zarce zuwa garinsu na farko daga nas, sarkin yaki Salishu Dankabo ya
daura kayaa sirdin dokinsa, ya jawo ta har zuwa tsahon wurinsu, wato y’ar
Gusau,ya bude hanya ga mutane, amma sai ya gurgusa gaba kadan da ‘yar Gusau ya
zabi wuri. Da mutane suka iso aka ci gaba da gyara wuri, aka kafa wa Sarkin
Katsina Abdulƙadir bukkokin sa, sai kuma na Malam Muhammad Modibbo da Ɗangaladima
Usamatu da shi kansa Salishu Ɗankaboda liman Muhammadu babba da sauransu.
Haka dai mutane Gusau suka dinga tasowa daga zama har suka dawo wannan wuri sai
suna kiran shi da Gusau. Wannan kuwa yafaru ne a shekara ta 1275 zuwa 1862. A
lokacin da aka yi wata wuta wadda ake kira wutar A’isa a garin Rawayya a 1862
ya ƙara karfafa wa mutanen garin Gusau ƙwarin
guiwar barin Rawayya domin mafi yawan garin wuta ta kone shi. Bayan komawar su
Gusau a zama na biyu wato sabon zama ya farune a farkon sarautar Sarkin Musulmi
Amadu Atiku a shekara (1859-1866) Bayan mutane garin Gusau sun koma wurin su na
farko lokacin Sarkin Katsina Abdulƙadir shekara 1827 – 1867. A lokacin ne aka
gina garin Gusau da ganuwa, samin kariya ga mazauna wannan gari domin taken ƙara
jawo masa bunkasa da haЪaka ta hanyoyi da
yawa.
A lokacin da mutanen garin gusau
suka dawo wurin tahanyar kewaye shi da shigen ƙaya. Wannan kuwa ya
auku ne tun zamanin Malam Muhammadu Sambo ɗan Ashafa har zuwa farko da tsakiyar sarautar Sarkin
Katsinan Gusau Abdulƙadir. A zamanin Sarkin Katsina Abdulƙadir,
Sarkin Musulmi Amadu Atiku a shekarar (1859) ya yi wa Sarkin Katsinar a lokacin
daya je yi masa muba’yi’a bayan nada shi Sarkin Musulmi. Alkawarin ya sa a gine
garin Malam Muhammadu Sambo ɗan
Ashafa da ganuwa.
Don haka, ya umurci sarakunan
garuruwan dake makwabtaka da garin Gusau dasu taima ka wajen gine garin na
Gusau da ganuwa. Daga cikin waɗanda
suka taimaka wurin gina ganuwar Gusau, suka turo mutanen su, akwai Sarkin
kiyawa Jibri na Ƙauran Namoda, da Sarkin Fulani Bundgudu Muhammadu da
mutanen Kwatarkwashi, da kuma mutanen Garin rawayya da suaran su, duk sun zo
sun taimaka kwarai wajen wannan aikina gina ganuwa. Wanan shine lokacin na
farko da garin Gusau ta fara samun ganuwa ginanna da ƙasar
wato yambu mai ƙwari tare da yi ma ta ƙofofi guda tara.
Bayan haka, a zamanin Sarkin
Katsinan Gusau, Muhammad modibbo shekarar (1867) aka sake faɗaɗa garin Gusau da
ganuwa a sana diyyar zuwan wasu mutane. Shi wanna ƙari ya haɗa da unguwar da ake
kira Rahaji wadda ta kunshi mutane Abarma da Janyau da wasu Rahazawa. A lokacin
ne aka sami kofar Rahaji haka kuma an daɗa faɗaɗa ganuwar ta bangaren
kudancin garin ya yi da haza da abokin shantali da dan’uwansa Malam Umaru suka
zo Gusau.
A zamani Sarkin Katsinan Gusau Muhamamdu
Tuburi; (1876 – 1887) an ƙara samun bunƙasar, garin da suka
haɗa da shiyar Birnin
ruwa a zama cikin ganuwa. Amman a lokacin sarkin katsinan Gusau, Muhammadu giɗe (1887 – 1900) ne
aka haɗa
Birnin haza da Birnin ruwa suka zama shiyya ɗaya da sunan Birnin haza.
Ganuwar Birnin Gusau ta sake samun
bunkasa da haЪaka a zamanin Sarkin
Katsinan Gusau, Muhammadu Murtala (1900-1916). Ƙarin ya auku ne ta
wajen yamma maso arewa wanda ya sat a hada da makabarta da kuma gandun
Sarki, zuwan wanna lokacin ganuwar
Birnin Gusau ta sami ƙofofi guda tara (9) sune; ƙofar
Rawayya, ƙofar Katsaura, ƙofar Kwatarkwashi, ƙofar
Goje, ƙofar Dogo/dokau, ƙofar Tubani, ƙofar
Jange, ƙofar
Mani da ƙofar
Matsatstsa. Ginin ganuwa watau babbar kariya ce da samun ci gaban gari na son
ya bunƙasa ya samu ci gaba sosai da haЪaka da yawaita mai amfani, to ginin ganuwa yana daga cikin
abubuwan da ke samar da leka. Kuma gina ganuwa yana daga cikin tsarin tafiya da
har kofofin manya dauloli don kariya ta sosai. Kamar Kano da Katsina da Zazzau,
duk sun samar da ganuwa har a yau wasu wurare akwai sauran burburshinta.
Ganuwar garin Gusau dai tun zamanin
Sarkin Katsinan Gusau Malam Muratala bata ƙara samun wane
bunkasa ko kum kari ko habaka daga lokacin ba’a ƙara faɗaɗa garin Gusau da
ganuwa ba.
3.3 TASIRIN GANUWA (A GARI)
Ma’anar tasiri:
Masana daban-daban sun tofa albarkacin bakin su akan wannan kalma ta tasiri,
kamar haka; Ibrahim. M (1985) ya bayana Kalmar tasiri da cewa, al’adar da wani
yakan yi wadda a da can ba’a san da ita ba. Inda ya ƙara da cewa, hakan na
faruwa ne a sanadiyyar zamantakewa da cuɗanya da juna ta fuskar siyasa da addini.
Uwaisu. A (2007) ya
fassara Kalmar Tasiri da cewa asalinta Kalmar larabci aka aro, wadda ke da
sigar kamar haka “Ta’asiri” wadda kuma a larabci a ke nufin mamaye wani abu ko
wata al’ada. A Hausan ce kuma, kalamar na nufin yadda wani abu yake mamaye ko
canza sigar wani abu, ko kuma ya canza al’adar da wani yake yi wadda da can
ba’a san shi da ita ba.
Bashir A. (2001) ya
bayyana Kalmar tasiri da cewa, kalma ce ta larabci da. Hausawa suka yi mata
kwaskwarima ta zama ta su. Basher yace, kalamar tasiri na nufin abu ya kama
mutun har ma ta kasance ya yi ƙarfi a zuciyarsa, haka kuma ya fassara
kalamar tasiri da cewa yadda wani abu daban yake canza ma wani abu yanayi, ko
ya ƙara ma wannan abun kyau da bunƙasa, ko kuma ya
haifar ma da abin naƙasu.
Babu wani abu da wata
al’umma ko wani mutun zai aikata ba tare da makasudin aikata wannan abin ba.
Haka kuma, akwai wata manufa ta musamman wajen aikata wannan abin, sai dai abin
yana iya kasancewa mai kyau ko kuma mummuna, ya danganta yadda abin ya yi
tasiri a zuciyarsa, ko kuma yadda abin ya yi tasiri a ala’adar al’umma ko ƙasa.
Domin haka, wannan
babi zai ci gaba da bayyana irin tasirin ganuwa a gari. Hausawa basu da ganuwa
ga al’adarsu ko adabin su, amma tasirin hulɗa da mutanen shingai na ƙasar mali, da Hausawa
sun kayi a zamanin da sun ko yi yadda ake yin ganuwa, iri daban – daban da kuma
sanin amfanin ganuwa da muhimmancinta. Wanna hulɗa ta faru ne, tun a karni na shida (6), daga lokacin
Hausawa suka fara tunanin gina ganuwa a ƙasar Hausa, kuma sun
samu nasarar gina ganuwa, daga bisani Hausawa sun ci gaba da amfani da ganuwa a
kasashesu da daulolinsu, har zuwa ƙarni na goma sha tara, bayana rushewar daular
Shaihu Usman Ɗanfodiyo.
Ana amfani da abubuwa
da dama, wajen yin ganuwa a ƙasa, kamar dutse ko kuma ƙasar
yumbu, ko kaya, ko kuma ayi rame a zagaye gari da s hi da sauransu. Samun
ganuwa ga kowane irin gari alamace ta samun kariya ga mazauna wannan gari domin
takan ƙara jawo masa bunkasa da haЪaka
ta hanyoyi da yawa. Domin haka yana da kyau mufadi irin matsayin ganuwa da
tasirinta.
Duk tsofaffin birane
a ƙasar
Hausa waɗanda
aka kafa, kafin daulolin da waɗanda
aka kafa bayan kafuwar dauloli ko bayan jihadin Shaihu Usman Ɗanfodiyo
suna da ganuwa. Tsofaffin birane kamar su, Kwatarkwashi da Birnin ‘yadoto da
Birnin Katsina da Zazzau da Daura da Gobir da Kabi da kuma Birnin Kano, da
sauransu. Duk suna da ganuwa.
Tasirin ganuwa a gari
shine, domin a kare gari, daga har-hare da yake-yake da suka yi yawa a zaminin
saboda tarihi ya nuna cewa; Daular Birnin Kano tasha karawa da Daular Katsina
da Zamafara da Zazzau kai har ma dasu Damagaram. Domin haka, sai a gina ganuwa
saboda a kare birane da jama’arsu, daga hari ko yaƙi, ko wani farmaki da
barazana.
A cikin ƙarni
na sha biyu (12) kusan shekara ɗari
tara (900) da suka gabata aka fara gine ganuwa a garuruwa ƙasar
Hausa ya kasance tun kafin ƙarni na goma sha bakwai, har zuwa karnin na
goma sha tara (19), bayan jihadin Shaihu Usman Ɗanfodiyo, kafin zuwan
turawa mulkin mallaka ƙasar Hausa (1903), aka gina ganuwa kuma duk
manyan dauloli sun mallaki ganuwa domin sanin irin tasirinta a zamanin da.
Saboda haka, dole ne
kowani gari ya mallaki ganuwa, domin duk lokacin da ƙaasa bata da ganuwa a
kowane lokaci za a iya shigowa a cisu da yaƙi, kuma a kama mutane
ƙasar
a maida su bayi, kuma a mallake masu dukiya, daga wannan lokacin ana ruguje
wannan daula, kuma za a mallaka wannan ƙasa sakamakon an ci
su da yaƙi.
Amma saboda irin tasirin
da ganuwa take dashi, ba za a shigo ƙasa ba kai tsaye bare a kawoma mutanen gari
farmaki ko yaƙi ba, ko a masu wata barazana ba, har a ci su da yaƙi
ba. Sai dai in yaƙi ya haɗa
wata ƙasa da wata kasa a lokacin sai a yi wasika da yarjejeniya
za a haɗu
domin yin wannan yaƙi, sai a saka rana da lokaci da za a haɗu domin karawa da
gwabzawa a fagen yaƙi.
Har way au; cikin
tasiin ganuwa a gari, dole ne duk wanda zai shiga ƙasa, sai an san shi,
kuma an san ko daga, inda yake, da kuma makasusin baro ƙasar
sa, ta haihuwa. Sabanin a yau da muke a ciki.
3.4 Naɗewa
Waɗannan su ne, abubawa da suka samu a cikin wannan babi na
uku, inda aka fara da shimfida kuma sai aka kawo, tarihin garin Gusau, sai kuma
aka kawo takaitaccen tarihin ganuwar Gusau, sai kuma ƙarshe
aka yi bayanin tasirin ganuwa a (gari) da kuma muhimmancinta.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.