Ticker

6/recent/ticker-posts

Ganuwar Gusau Da Kofofinta (2)

Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsuna da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.

Ganuwar Gusau Da Kofofinta (2)

NA

UMAR YAHAYA DOGARA

Ganuwa

BABI NA ƊAYA

1.0              Shimfiɗa                  

Wannnan Bincike zai yi magana akan ɗaya daga cikin nau’oin al’adu al’umomi da rayuwarsu, har ma da tarihinsu.

Tarihi abu ne wanda yake sanar da ama’a rayuwar al’umomi da suka wuce dangane da halin zamansu, da tattalin arzikinsu, da sana’ar su, da al’adunsu, da ilimin su, da suaran abubuwan da tarihi yake dubawa.

Duk da cewa rubutu a kan tarihin kowane gari abu ne mai wahala da neman dogon binickie, domin gudun rikitarwa da kuma buyar diddigin littattafan da aka, rubuta, domin kokarin tabbatar da hakikanin gaskiyarsu da kawar da shakku ga al’umma.

Wannan bincike da za a gabatar an laƙaba masa sun “Ganuwar Gusau da Ƙofofinta” kuma an rubuta shi da nufin ya ba yarda tarihin ganuwar garin da bunkasar da mutane garin na farko, da kuma Ƙofofin ganuwar Gusau.

1.1 MA’ANAR GANUWA

Sa’idu Muhammad Gusau (2012) da Bello Muhammad (2012) cikin littafin “Gusau ta Malam Sambo” Sun bayyana cewa; Ganuwa wata babbar kariya ce, mai muhimmanci a gari. Sun ƙara da cewa; Ganuwa da ɗaɗɗiyar al’ada ce da aka daɗe ana ginawa tun zamani mai nisa. Ta hanyar ganuwa ake gane faɗin gari da kuma yalwarsa da tattalin arzikinsa da zamantakewa mai nagarta.

Haka zalika, wadannan masana (2012) sun ƙara da cewa; Ganuwa tana taimakawa wajen bunkasar gari, tare da bashi kariya da kuma tsaro. Domin gujewa farmaki ko hare-hare da yaƙe-yaƙe. Gina ganuwa yana ɗaya daga cikin tsarin mulkin manyan daulolin sarakuna kasar Hausa, kamar su: Kano da Katsina da Zazzau da Sakkwato da Zamfara da Sauransu. Duk suna gina ganuwa ne domin samun kariya ta musamman. Daulolin ƙasar Hausa sun jima suna gina ganuwa tu zamanin kaka – da kakakanni.

Munir M. (2017) ya bayyana cewa “ganuwa na nufin kare kowane irin gari ko birni daga cin zarafin was, kuma tana taimakawa wajen samam masu ‘yanci da barrenta daga abokan gaba.

Ishak. M. (2017) Ganuwa na nufin gina wani gin ko alama a gari don samun kariya da hare-haren ko farmaki daga abokan gaba, da kuma gina kofofin cikin ganuwar.

Hashim Gumel M. (1998) ya bayyana cewa, birane a ƙasar Hausa waɗanda aka kafa bayan kahuwar dauloli da bayan jihadi suna da ganuwa. Tsofaffin Birane kamar su: Kwatarkwashi da Birnin ‘yandoto Birnin Daura da Birnin Katsina da Birnin  Zazzau da Birnin Kano da Birnin Wudil, duk suna da ganuwa. A kan gina ganuwar gari ne kuwa domin a kare gari daga har-hare da suka yi yawa a wuncan zamani.

Haka zalika, Hashim Gumel (1998) ya bayyana cewa Birinin Kano ko a ce Daular Kano ta sha Karawa da daular katsina da ta Zamfara da ta Zazzau, kai har ma da su Damagaram, da dai sauransu, ya ƙara da cewa; a na gina ganuwa ne domin a kare Birni da jama’arsa, kuma hasashe ya nuna cewa a cikin ƙarni na sha biyu (12) (kusan shekara 800 da suka wuce) aka  fara gina ganuwar Birnin Kano tun a  wannan karnin zamanain sarkin kano. Gajimusu wanda ya yi zamani a tsakanin shekara 1095 zuwa 1134. An kammalata a zamanin sarkin kano Jusa.

Har ila yau, Hashim Gumel (1998) ya ci gaba da cewa; inda za’a iya nuna muna majigin yadda ganuwowin birane suke a ƙasar Hausa kafin zuwan turawa da an burge mu da kuma mun fahimci cewa kakanninmu wayayyu ne, kuma basira da fasaha ne kudu ba yadda turawa mulki mallaka suka dauki bakar fata a matsayin koma bayan halitta, amma da suka zo ci Kano da yaki sai da suka sarawa kakanninmu tare da girma mawa a gare su.

Bisa dalilan da suka gabata zamu iya fahimtar dalilin gina ganuwar gari, kuma kamar yadda aka fada a baya ba. Birnin Kano ne kawai ke da ganuwa ba. Manyan Biranen ƙasar Hausa kamarsu; Katsina da Zazzau da Sakkwato da Daura da Zamfara duk suna da ganuwa, to amman in anje yau kila sai dai a tara da ƙofofi kawar, babu ganuwa. Kananan garuruwa ne kamar su, Ƙausani da Wudil da ‘Yandoto da Kwatarakwashi sune da ganuwa. Ana kyautata zaton cewa kafin zuwan turawa akwai garuruwa fiye da dari masu ganuwa a ƙasar Hausa, amma yanzu duk sun zama tarihi saboda sakaci da rashin kishin tushen da mutun ya fito.

Haka zalika, akwai wani babban abin lura anan. Wannan abun kuwa shine, duk lokacin da ake yi maganar ganuwa to dole ayi maganar ƙofofinta, domin kowace irin ganuwa a duniya tana da ƙofofi kamar ganuwar Kano tana da Ƙofofi kamar haka; Ƙofar Mazugal da Ƙofar Wambai da Ƙofar Ruwa da Ƙofar Dukawuya da ƙofar Adama da Ƙofar Dan Agundi da Ƙafar Mata da Ƙofar Na’isa da Ƙofar Kansakali da Ƙofar Famfo da sauran su.

Har ila yau (Isma’il Abbas) ya bayyana cewa ganuwar a Zazzau ita ma tana da Ƙofofi kamar haka; Ƙofar Gayan da Ƙofar Kuyan Bana, da Ƙofar Tukur – Tukur da Ƙofar Doka da Kuma Ƙofar Galadima da Ƙofar Kibau da sauran su. Husau (Leadership 2017)

Haka kuma. Farfesa Munir Mamman (2011) ya Bayyana kofofin Katsina da anguwoyinta kuma ya kawo su kamar haka; Ƙofar Doka  da Ƙofar Kwa, da Ƙofar Ƙaura da Ƙofar Sauri da Ƙofar Durbi da Ƙofar Marusa da suaran su.

Bisa ga bayanan da suka gabata, mun fahimci cewa tabbas duk wata ganuwa da take a Ƙasar Hausa dama duniya baki – daya tana da Ƙofofi, domin haka ne, wannan binciken zai yi bayanin ganuwar Gusau da  Ƙofofinta

1.2              Dalilin Bincike

Kamar kowa ne irin bincike da a kan gudanar, akan yi shine domin zakulo wasu muhimman abubuwa da ta yiwu ba a sani bad a farko ko kuma an sani, amma ba’a tara da shiba, ko kuma ba a tsara shi ba, domin masu nazari, hausawa na cewa “Banza bata kai zomo kasuwa” Wannan Magana ta yi dai-dai da nufinta na yin wannan bincike. Shi ya sa naja damara na kuma zage damtse da nufin nazari a kan wannan batu mai taken “Ganuwar Gusau da Ƙofofinta”

Masana da manazarta kamar su; Ferfesa Sa’idu Muhammad Gusau (2012) da kuma Bello Muhammad (2012) da Ferfesa Munir Mamman (2011) da Isma’ila Abba (2017) da Garba Nadama (1972) da Sauran su. Wadannan Masana sun nazarci ganuwa da Ƙofofinta, ta fuskar daban-daban amman basu nazarci ganuwar gusau Da Ƙofofinta ba kaitsaye a matsayin Ƙundin binciken suba. Amma Farfesa Sa’idu Muhammad da Bello (2012)  Sun dan tofa albarkacin bakinsu game da ganuwar Gusau da Ƙofofinta. Dalilin da yasa aka yi wannan nazarin shine domin a dora daga gudummuwar da wadannan manazarta, a gano yadda tarihi ya fayyace ganuwar Gusau da Ƙofofinta.

1.3              Manufa Bincike

A kowani lokaci mutum yayi nufin yin wani abu, to! Lallai babu shakka yana da manufarsa ta yin wannan abu. Kamar yadda Hausawa suke cewa” Kowanne allazi da nasa Amanu” haka ne domin komai baya faruwa sai dai manufa ta yinsa. Saboda haka babu wani bincike da zai faru ba tare da wata manufa ba.

Babbar manufar wannan bincke shine a bayyana ganuwar Gusau da Ƙofofinta, tare da yin tsokaci daga a,l’ada da adabi. Bincike ya Ƙudurin aniya nazartar ganuwar da tasirinta a Ƙasar Hausa, da kuma yadda Bahaushe da adabinsa ke kallon ganuwa a rayuwar Zaman duniya.

1.4              Harshen Bincike

Hausawa sun san me ake kira ganuwa, kuma sun rarrabe tsakani nau’oin ganuwa da muhimmancinta, tare da tasirinta. Domin haka shi yasa wannan bincike yake hasashe abu ne mai yi yuwa a sami, kundi ko mukala ko littafi ko jarida, da suka yi bayani a kan ganuwar Gusau da Ƙofofinta da yanayinta.

 

1.5              Farfajiyar Bincike

Tarinin garin Gusau da Ƙasar Hausa, shi ne farfajiyar wannan bincike, aikin ya taƙaita, a kan Ƙofofin Gusau. Ganuwar Gusau tana cikin farfajiyar wannan binciken, saboda haka nazarin ya taƙaita a kan Gusau da kuma Ƙofofinta.

Bugu da kari, binciken zai yi tsokaci a kan tarihin ganuwar Gusau, da Ƙofofinta cikin garin Gusau, da tsarin sarakunan Gusau, da wasu unguwanin Gusau, da Gusau a ma tsayin babban Birnin Jahar Zamfara da sauran su. Saboda haka ganuwar tana da tasiri mai yawa a cikin gari.

 

1.6              Muhimmancin Bincike

Ana saran wannan bincike ya zama mai muhimmanci wajen fayyace ganuwa ga al’ummar Hausa ta fuskar nazarin ganuwa. Haka kuma, aikin ya zamo mai muhimmanci saboda zai Ƙara fito da alaƙar da ke tsakanin Ƙofa da ganuwa, da kuma al’ada da adabin Hausawa, haka kuma ana saran binciken zai taimaka wa Hausawa su zurfafa tunanin su da ke Ƙunshe a cikin adabin su. Haka zalika wannan bincike zai kara fito da martabar ganuwar hausawa a duniya da ma kasa baki ɗaya.

Daɗin da ɗawa, wannan aiki zai zama hanyata taimako ga wadan da suke son ganin ilimin al’ummar su ya haЪaka ta fannin karatu da rubutu sanna kuma bincike zai zaburar da manazarta al’adun da adabin wajen zurfafa bincike a kan sa wato a fahimci muhimmancin al’ada da kuma adabi harma da falsafar Bahaushe.

1.7              Hanyoyin Bincike

Kowane bincike na ilimi na bukatar ingantattun hanyoyin gudanar da shi, a wannan bincike an yi amfani da amintattun hanyoyin gudanar da bincike. Wato hanyoyin tara bayanai, da kuma hanyoyin ƙwanƙwance bayanai; hanyoyin da aka bi wajen tara bayanai sun hada da; shiga ɗakin karatu inda aka karanta littafai da Maƙalu da ƙundayen bincike da kuma jarida. An tattauna da mutane domin ƙkara samun haske wajen tattara bayanai na wannan bincike. A dunkule wannan ita ce yadda aka ƙwanƙwance bayanai.

1.8              Naɗewa

Wannan babi na ɗaya, babi na ɗaya kunshi da shimfiɗar wannan bincike baki ɗaya, inda aka kawo muhimman abubuwa waɗanda suka haɗa da; gabatarwa da dalilin bincike da farfajiyon bincike da muhimmanci bincike da hanyoyon gudanar da bincike. Haka kuma, a cikin manufar bincike, an nuna cewa manufar wannan bincike it ace zakulo tarihin ganuwar Gusau da kuma ƙofofinta.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsuna da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.

Ganuwar Gusau Da Kofofinta (3)

NA

UMAR YAHAYA DOGARA

BABI NA BIYU

WAIWAYEN AYYUKAN DA SUKA GABATA

2.0 Gabatarwa

            Masu iya Magana na cewa “waiwaye adon tafiya” wasu kuma kance “daga na gaba ake gane Zurfin ruwa” Dangane da wannan zance na hikima daya gabata, yana da matukar muhimmaci kwarai da gaske a dubi wasu ayyukan da masana da manazarta suka gabatar, waɗan da suke da alaƙa da wannan bincike nawa kuma alaƙar zai iya kasancewa ta kusa ko ta nesa.

            Wannan babi a dunƙule ya waiwaya littafai da ƙundaye da muƙalu da sauran bangarorin da suke da alaƙa da wannna bincike mai suna binciken, na ayyukan da suka gabata, shine a fayyace ganuwa da ƙofofinta, tare da tasirinta, kuma binciken ya ƙudiri aniyar nazarin ganuwa da ƙofofinta bakin gwargwado, domin haka wannan binciken zai yi ƙoƙarin zaƙulo waɗansu abubuwa na tarihin garin Gusau da suka shafi ganuwar garin da ƙofofinta, wannan shine makasudin wannan babi.

2.1 Gumel H. (1998) ya bayyana cewa; duk Tsofaffin birane a kasar Hausa waɗanda aka kafa bayan kafuwar dauloli; ko bayan jihadin shaihu Usman Ɗanfodiyo suna da ganuwa. Tsofaffin birane kamar su, Kwatarkwashi da Birnin ‘Yandoto da Birnin Katsina da Kogo da Zazzau da kuma Birnin Kano da Gobir da kuma Birnin Daura, duk suna da ganuwa. Akan gina ganuwar gari ne domin a kare gari daga har-hare da yake-yake da suka yi yawa a zamanin da.

Gumel H. (1980) ya bayyana: Birnin Kano ko a ce daular Birnin Kano ta sha karawa da daular Katsina, da ta Zamfara da ta Zazzau kai har ma dasu Damagaran. A na gina ganuwa domin a kare Birni da Jama’arsa; A cikin ƙarni na sha biyu (12) a shekar 1202 miladiya, kusan shekar dari tara (900) da suka wuce aka fara gina ganuwar Birnin Kano (Gajimasu). Kamar yadda: Tanko (1996) na sashe labaran ƙasa na jami’ar Bayero ya yi bayani, katangar ganuwa kano a zamanin ta kewaye bangaren Dala da Gwauron – dutse ne, har yanzu in aka je wurin ƙofar Mazugal za’a ga Burbushin ta. Daga nan sai ganuwar ta yi arewa tabi ta wajen masallacin juma’a na Birnin, sannan ta yi ta wajen asibitin murtala ta mike ta ƙofar wambai an zagaye Birnin lokacin kenan.

Haka zalika, Gumel H. (1998) ya ƙara da cewa; ƙarni na goma sha biyar, sabida yawan jama’a da habakar harkokin kasuwanci. Birnin Kano ya ƙara haЪaka. A sakamakon haka ne sarkin Kano Muhammadu Runfa, wanda ya ƙara faɗaɗa ganuwar kano. Tanko, (1996) ya ƙara bayyana cewa Sarkin Kano Muhammadu Runfa ya ƙara da’irar ganuwar da kusan kasha hamsin daya (51), kuma ya tayar da gidan masarautar kano ya matso da ita dai-dai inda take a halin yanzu ta yadda ya shiga sabon birnin. Tunda kafin a yi hakan, inda gindan sarki yake a halin yanzu a lokacin wajen badalane.  A wanan karo ne ake sami ƙofofi kamar su, ƙofar Gadon ƙaya da ƙofar Dan Agundi da kuma ƙofa Na’isa har ganuwar ta tarar da ƙofar ƙansakali.

Har ila yau Gumel, H. (1998) ya ci gaba da cewa; lokaci na ƙarshe da aka ƙara faɗaɗa ganuwar Birnin Kano shine, a ƙarni na goma sha bakwai (17) a zamanin Sarkin Kano Muhammad Nazaki Sarkin na Ashirin da takwas (28) Gumel H. (1998) ya   ƙara da cewa; Wambai giwa shine ya’ yi wannan gagarumin aiki a lokacin sarki ya tafi yaki da ƙasar Katsina. Garin cewa shi Wambai giwa bashi da lafiya a lokacin da aka tafi yakin, sai ya yi tunanin mai zai yi ya burge Sarki in ya dawo, An ce a lokacin da aka yi wannan aiki sai da a ka yanka shanu ɗari to ganuwar Birnin Kano da muke gani yanzu, a wannan lokaci ne a ka ginata.  Ba za a ce ba’a ƙara yi mata komai ba, tun daga lokacin har zuwa lokacin jihadi. Babu ko shakka ana yi mata yaЪe sana kuma kyautata. Wannan daliline ya sa harta kawo yau muke ganin sauranta.

Har ila yau Gumel H.  (1998) ya ƙara da cewa; a taron cikar Kano shekara dubu (1000) soma mulki, Tanko, (1996) ya yi tambayar cewa da an ci gaba da faɗaɗa ganuwar Birnin Kano in da ta kai a halin yanzun har yana cewa; ƙila yanzu da ta kai kura.

Haka zalika, Hashim gumel (1998) ya ci gaba da cewa; inda za a iya nuna muna majigin yadda ganuwowi birane suke a ƙasar Hausa kafin zuwan turawa da an burge mu da kuma mun fahimci cew Kakanninmu wayayyune, kuma masu basira da fasaha ne, ku duba yadda Turawan mulkin mallaka suka ɗauki baƙar-fata a matsayin kom-bayan halitta, amma da suka zo cin Birnin kano da yaƙi sai da suka sara wa kakaninmu. Lord Lugard a (1903) da su ka gane da badalar Birnin Kano. “lokacin da dakarun mu suka iso Kano sun iske wata babbar katanga mai matuƙar ƙwari wadda ta kewaye Birnin, Wannan Katagar ta ganuwa, ta kai mil goma shatara da ƙofofi oma sha uku (13) waɗanda take dasu “Wannan daliline na ganuwar Birnin Kano ya hana Turawa mulkin mallaka suka suka shiga cikin garin kano balle har suci daular su da yaƙi. Sai dai suka haɗa kai da ɗiyan sarakuna suka ci kano da yaƙi, da ma wasu garuruwan na ƙasar Hausa.

Bisa dalilin da suka gabata; kowa zia iya fahimtar dalilin gina ganuwar gari, kuma kamar yadda aka faɗa a baya, ba Birnin Kano ne kawai ke da ganuwar ba. Manyan Biranen ƙkasar Hasau Kamar su, Katsina da Zazzau da Sakkwato duk suna da ita, to amman in anje yau ƙila sai dai a tatar da ƙofofi kwai ba ganuwa. ƙanana garuruwa ne kamar su, ƙausani da Wudil da Daura da ‘Yandoto da Kwatarkwashi sune da ganuwa. Ana kyautata zaton cewa kafin zuwanTurawan mulkin Mallak akwai garuruwa fiye da dari (100) masu Ganuwa a ƙasar Hausa, amman yanzu duk sun zama tarihi, saboda sakaci da rashin kishi tushen da mutum ya fito.

Wannan aiki na Hashim Gumel (1998) na da alaƙa ta kusa da wannan aiki da ake gudanarwa ta la’akari da duka ayyukan sun fuskanci gari da ganuwa, har ma da ƙofofin.

Domin binciken Gumel (1998) ya tabbatar da samuwar ganuwa a Kano, da kuma kasar Hausa, ya fito da yadda Hausawa suke kallon ganuwa a matsayin garkuwa ko kariya a gari sannan ya ambaci ƙofofin Kano, da kuma sunayen su.

Tabbas! Wannan aiki yana da dangantaka da alaƙa da kut da Kut da binciken da ake gudanarwa, saboda dukkan su ayyuka ne da suka shafi gari da ganuwa da kuma ƙofofi sai dai ƙofofinta’ Ake gabar dashi.

Abba, (2017) ya gudanar da bincike mai suna “Dangantakar tarihi da waƙar ƙofofin Kano” Nazari daga bakin Ala” Domin haka a wannan binciken ya tofa albarkacin bakinsa akan ganuwa da kuma ƙofofin Kano, ya ce, a cikin sarakunana gidan bagauda ba za a manta da gijemasu ba, domin shi ya halacci jama’ar Kano masu bautawa Tsumbubura har suka yarda suka taimaka masa ya fara gina ganuwar gari. Ya fara daga rariya (A tsakanin ƙofar ɗan gundi da ƙofar Na’isa)yayi yamma zuwa ƙofar adama da ƙofar kansakali. wanda a yanzu ƙofar Adama da ƙofarTuji Babu su duk da dai bincike ya gano cewa ba a gama ginin ba sai a cikin zamanin Usman zamne gawa, wato a cikin ƙarni na sha huɗu 1343 – 1349m.

Lokacin da yake-yake suka fara yawaita sai aka dinga haka kududdufai da fa ganuwa. Dalilin yin haka kuwa domin hana abokan gaba shi ga gari, da Birnin Kano ya faɗaɗa to sai jama’a suka mai da gindin ganuwar wajen ɗibar ƙasar gini. Ta haka aka din ga rushe wannan ganuwar mai daɗaɗɗen tarihi, sai da hukumar kiyaye kayan tarihi wato (National Council for Antiƙuities) ta tsawata kuma ta kawo wadan su gyara daga cikin waɗansu ƙofofin gari.

Haka zalika, Abba (2017) ya jara da cewa; akwai wani abin lura, domin kowa ganuwa da ƙofofinta a koda yaushe a tare suke tamakar ɗan jumma ne da ɗan jummai, dole ne duk lokacin da ake maganar ganuwa a yi maganar ƙofofinta. Haka kuma idan a na maganar ƙofofi a yi maganar ganuwar su.

Bugu da ƙari, Abbas, (2017) ya kawo sunayen ƙofofin Kano na tarihi a bakin Ala, Kamar haka:

1.      Ƙofar Mazugal

2.      Ƙofar Wamabi

3.      Ƙofar Ruwa

4.      Ƙofar Dukawuya

5.      Ƙofar Adama

6.      Ƙofar Ɗan Agundi

7.      Sabuwar Ƙafa

8.      Ƙofar Waika

9.      Ƙofar Mata

10.   Ƙofar Na’isa

11.   Ƙofar Dawanau

12.   Kofar Nasarwa

13.   Ƙofar Gadon-Ƙaya

14.   Ƙafar Kabuga

15.   Ƙofar kansakali

16.   Ƙofar Famfo

Shine Wanna bincike yana da alaƙa da aikin na alaƙar juna ta kut da kut domin kanun aikinsa shine “Dangan taka da waƙar kofofin Kano nazari daga bakin Ala” Domin haka Wannan binciken yana da alaƙa da nawa binciken mai suna “Ganuwar Gusau da ƙofofinta”

Sai’du Gusau (2012) da Bello Muhammad (2012) sun Bayyan cewa; ganuwa wata babbar kariya ce mai muhimmanci a gari da take da matukar tasiri da kuma amfani ga al’ummar gari.

Bugu da kari, masana (2012) sun ƙara da cewa Ganuwa daɗɗar al’ada ce da aka daɗe ana ginawa tun zamani mai nisa. Ta hanyar ganuwa ake gane fadin gari da kuma yalwarsa da tattalin arzikinsa da zamanta kewa mai nagarta.

Haka zalika, waɗannan masana (2012) sun ƙara da cewa; ganuwa tana taimakawa wajen bunkasar gari, tana da bashi kariya da tsaro. Domin gujewa farmaki ko hare-hare da yaƙe-yaƙe. Gina ganuwa yana ɗaya daga cikin tsarin mulkin manyan dauloli Sarakunan ƙasar Hausa, Kamar su, Kano da Katsina da Zazzau da Sakkwato da Zamfara da sauran su. Duk suna gina ganuwa ne domin samun kariya ta musamman daga abokan gaba. Daulolin ƙasar Hausa sun jima suna gina ganuwa tun zamanin kaka da kakakanni.

Wannan littafi na masan, yana da dangantaka ta kusa da binciken da ake gudanarwa, saboda sun yi Magana a kan Gusau, da cewa shi wannan binciken ya karkata ne a kan “Ganuwar Gusau da ƙofofi”

Mamman M. (2011) yayi tsokaci akan ƙofofi katsina da a guwanninta, kuma ya kawo su kamar haka:-

1.      Ƙofar Yan Doka

2.      Ƙofar Ƙwaya

3.      Ƙofar Ƙaura

4.      Ƙofar Sauri

5.      Ƙofar Durbi

6.      Ƙofar Marusa da sauran su.

Haka zalika, Munir (2011) ya ƙara da cewa kasan cewar dole ne duk lokacin da aka yi magan akan ƙofofi dole ne, a yi maganr ganuwar su, kuma ya nuna cewa ganuwar katsina ta samu tun zamanin mai nisa, ko tun lokacin kaka – da kakanni kasancewar har yanzu babu takamammen lokacin da ganuwar daular katsina ta samo ko an ka yi ta, sai dai hasashe.

            Idan aka duba bayanan wannan masani, za a fahimci wannan aiki ne da dangantaka da aikin bincike da ake gabatarwa, shi dai wannan an taƙaita akan ƙofofi da ganuwa ne, shi kuma aikin da ake gudanarwa zai yi bayani ne a kan “Ganuwar Gusau da ƙofofinta”

            A Jaridar Hausa (Leadership 2017) sun bayyana cewa; Ganuwar Zazzau ita ma tana da nata ƙofofi na tarihi tu ƙarnukan da suka gabata.

Haka zalika Jaridar Hausa (leadership 2017) sun kawo jerin sunayen ƙofofin Zazzau Kamar Haka:-

1.      Ƙofar gayen

2.      Ƙofar Tukur – Tukur

3.      Ƙofar Kuyan Bana

4.      Ƙofar Doka

5.      Ƙofar Kibau

6.      Ƙofar Kone

7.      Ƙofar Bai

8.       Ƙofar Jatau

9.      Ƙofar Galadima

Muhammad, (2017) ya yi aiki mai suna “Jiya a yau ƙofofin Zazzau a bakin Ala” kuma a cikin nasa ya waiwayi tarihin Zazzau da ganuwarta da kuma ƙofofinta, kuma cikin binciken nasa, ya bada tarihin kowace ƙofa da ke cikin garin Zazzau, da kuma dalilin yiwa kowace kofa sunan da ake kiranta da shi jiya da yau.

            Haka zalika Muhammad I. (2017) ya zayyano sunayen ƙofofin Zazzau tare da cikakken tarihin su da dalilin gina kowace ƙofa da ke cikin garin Zazzau ga sunayen ƙofofin kamar yadda ya bayyana:

1.      Ƙofar doka

2.      Ƙofat kuyan bana

3.      Ƙofar bai

4.      Ƙofar gayan

5.      Ƙofar galadima

6.      Ƙofar jatau

7.      Ƙofar Tukur – Tukur ko ƙofar kibo

Bugu da ƙari Ishak (2017) ya bada tarihin tun daga lokacin gina waɗannan ƙofofin zuwa yau.

Waɗannan ayyuka na musamman da aka na zarata kan gari da ƙofofin ganuwa na da alaƙa ta kusa da aikin da za a aiwatar, domin sun bada ma’anar ƙofofin da kuma ganuwar su, amma wannan bincike nawa ya ta allaka ne kan “Ganuwar Gusau da ƙofofinta.

            Bello Gusau da Sa’idu Gusau (2012) a cikin littafinsu mai suna “Gusau ta Malam Sambo” sun tofa alabarkacin bakin su, akan garin gusau, kuma sun yi bayani Akan ganuwar Gusau da ƙofofinta da kuma tarihin garin Gusau da ƙofofinta Gusau da wasu unguwoyin Gusau da kuma Gidajen Sarautar Gusau  da tsarin Sarakunan Gusau da a matsayin babban Birnin jahar Zamfara.

            Haka zalika, waɗannan masana (2012) sun bayyana cewa; ganuwar Birnin Gusau ta sake samun bunkasa da haЪaka a zamani Sarkin Katsinan Gusau Muhammadu Murtala (1900-1916). ƙarin ya auku ne ta wajen yamma masu arewa wanda yasa ta hada da makabarta da kuma gandun sarki. (Hararar mu da M. U. A. G Gusau ta samu bunƙasa lokacin ganuwar Gusau ta sami ƙofofi har gusau tara (9) ga sunayen su kamar haka:-

1.      Ƙofar kwatarkwashi

2.      Ƙofar dogo

3.      Ƙofar  goje

4.      Ƙofar tubani

5.      Ƙofar jange

6.      Ƙofar matsattsa

7.      Ƙofar rawayya

8.      Ƙofar Katsaura

Domin Haka, wanna littafi yana da dangantaka da aikin da ake gudanarwa, saboda dukkansu ayyuka ne da suka shafi Gusau, domin haka suna da alaƙa da kuma danganataka ta kusa da wannan bincike mai suna “Ganuwar Gusau da ƙofofinta”.

Bisa ga bayanna da suka gabata, daga ayyuka ne musamman da aka nazarta a kan gari da ganuwa da ƙofofi, na da alaƙa da binciken da ake aiwatarwa mai taken “Ganuwar Gusau da ƙofofinta”.

2.2 Naɗewa  

            Wannan babi ya yi bitar ayyukan da suka gabata a akan ganuwa da ƙofofi, har mada garuruwan ƙasar Hausa masu ganuwa. Babin ya waiwayi wasu ayyukan da suka gudana a kan Gusau da ganuwarta harma da ƙofofinta a dunkule, bitar waɗannan ayyuka ya jagoranci wannan bincike da bayanai masu yawa game da abin da manazarta suka gano a al’adun Hausawa, da kuma ƙasar Hausa, wanda ya nuna akwai alaƙa tsakanin al’umar Hausawa da al’adunsa da kuma tunanain su game da ganuwa da ƙofofinta.

Kamar yadda masu iya Magana kan ce “Komai ya yi farko yana da ƙarshe” domin haka wannan babi na biyu ya kawo ƙarshe bisa ga waiwayar ko bitar da aka yi wanda keda alaƙa da wanna kundi ta nesa da ta kusa, wanda ya shafi ganuwa, da ƙofofi da kuma garuruwan ƙasar Hausa. Wannan babi an waiwayi waɗan su ayyukan da suka gabata waɗanda, keda alaƙa da wannan aiki na kusa da nesa, aikin ya binciki litttafai da kudaye da kuma muƙalu da sauran bangarorin ilimi. 

Post a Comment

0 Comments