Ticker

6/recent/ticker-posts

Musabbabin Taɓarɓarewar Tarbiyya A Ƙasar Hausa

 Sauye-sauyen rayuwa ta yau da kullum sun bayyana a tsakanin al’ummar Hausawa. Irin waɗannan sauye-sauyen sun wanzar da wasu munayen halaye da ɗabi’u, har sun kane-kane a akasarin rayuwar Bahaushe, waɗanda a da can babu alamunsu. Misali, rashin rikon amana da rashin cika alƙawali da ganin ƙyashi da haɗama da rowa da son kai da dogon guri da kwaɗayin tara abin duniya ta kowace irin hanya da yaudara da rashin tausayin na ƙasa ga kuma rashin gaski a cikin zukata. Irin waɗannan munayen halaye su ne suka taru suka zubar da mutuncin al’umma a idon duniya. Kuma aikata su shi ya haifar da lalacewar ƙasarmu tare da al’ummarta. Su kuwa kyawawan ɗabi’unmu da muka gada kaka da kakanni su ma sun fara gushewa, sai labarinsu kawai ake yi. Shin me ya kawo haka? Kuma me ke faruwa ne?Dangane da haka ne, wannan maƙala ta ƙuduri aniyar kawo bayanai game da dalilan taɓarɓarewar tarbiyya a tsakanin al’ummar Hausawa. Da farko maƙalar za ta fayyace ma’anar tarbiyya da abubuwan da suka haifar da taɓarɓarewar tarbiyya a ƙasar Hausa. Abubuwan suna da yawa, sai dai ni a nan zan karkata ne a kan waɗannan dalilai:

·         Cuɗanyar Hausawa da Wasu al’ummomi

·         Yi wa tarbiyyar Gargajiya Rikon sakainar Kashi

·         Kauce wa  tarbiyyar musulunci

·         Gina tarbiyyar ‘ya’ya a kan tsarin Nasara

Daga ƙarshe za a yi tsokaci ne a kan dalilan da suka sa ‘yan bokon farko ke da nagartattun halaye da ɗabi’u nagari, duk da kasancewar  Turawa ne suka koyar da su.

kasar hausa

Musabbabin Taɓarɓarewar Tarbiyya A Ƙasar Hausa

Dr. Adamu rabi’u bakura

arbakura62@gmail.com

08064893336

Gabatarwa

            Matsalolin rayuwar duniya sai ƙara bayyana suke yi kullun garin Allah yaw aye a farfajiyar ƙasar Hausa, sakamakon bayyanar fasahohi da ƙirƙire-ƙirƙiren zamani da ke ƙaruwa. Hanyoyinmu na tarbiyya da ladabtarwa waɗanda muka gada, sai daɗa sukurkucewa su ke, ko ma a ce sun gushe gaba ɗaya. An kuma rungumi wasu baƙin al’adu da ɗabi’un  al’ummomin yammacin ƙas ashen Turai, ba don komai ba sai don da’awar wayewar kai da buɗe ido.

            Daga cikin abubuwan da aka watsar akwai kyawawan hanyoyin  tarbiyyarmu da ladabtarwa, waɗanda bai kamata a ce an ƙaurace musu ba. Kamata ya yi a kyautata su tare da inganta su domin su dace da ci gaban rayuwar zamani, ta yadda za a yaƙI munanan halaye da ɗabi’un al’ummomin yammacin Turai. Al’adun da Hausawa ke kwaikwaya kuwa, da waɗanda suke ƙirƙira wa kansu, su ma a tsaya a kale su da idon basira, masu kyau daga ciki a yi amfani da su. Maras kyau kuma a ɗauki makin kau da su cikin hanzari.

Ma’anar Tarbiyya

            Tarbiyya kalma ce ta larabci, mai kushe da ma’anar koyar da hali na gari da kyautata rayuwar al’umma da shiryar da su zuwa ga halaye da ɗabi’u masu kyau da nagarta. Duk al’ummar da ta kasance haka, za ta zama mai kima da kwarjini da ganin mutuncin abokan zama. Kazalika za ta ding aba kowa haƙƙinsa kamar yadda ya dace. Tarbiyya ta kunshi renon jikin ɗan Adam da ruhinsa da kyawawan abubuwa masu kamala (Mafara, 1989), da (Yahaya da wasu, 1992), da (Tanko, 1993), da (Sa’id,2001).

Amfanin Tarbiyya

            Tarbiyya ta haɗa da kyautata hankalin ɗan Adam domin ya sami nagartrtar rayuwa da yadda za ta dace da yanayin al’ummarsa. Haka kuma tana kyautata al’adun al’umma su kasance kyawawa, ta kuma inganta su. Ta hanyar tarbiyya ne ake koyar da ladabi da biyayya da sanin ya kamata, da gargaɗI a kan tsare halayen kirki da kunya da haƙuri da yin gaskiya da kiyaye mutuncin al’umma da kiyaye ladabin Magana da kyautata sutura da muhalli don su dace da ɗabi’un al’ummar ƙasar (Yahaya da wasu, 1992:78).

Cuɗanyar Hausawa Da wasu Al’ummomi

            Duk inda aka sami baƙuwar al’umma ta zo ta cuɗanya da wata al’umma ta daban, dole ne a sami ɗaya ta yi tasiri a kan ɗaya. Musamman idan cuɗanyar ta ɗauki dogon lokaci, ta hanyar saye da sayarwa ko ta hanyar mamaya ko yaudara da fifikon ƙarfin makaman zamani, tamkar yadda ‘yan mulkin mallaka suka yi a wasu sassan ƙasar Hausa. Irin haka kan sa a wayi gari al’adun al’ummar da ta yi mamaya su yi tasiri a kan na waɗanda aka mamaye. In aka yi rashin sa’a sai a wayi gari sannu a hankali kyawawan al’adu da ɗabi’un al’ummar da aka mamaye suna gushewa ɗaya bayan ɗaya.

            Ƙasar Hausa ta sha gwagwarmaya da al’ummomi daban-daban na kusa da na nesa. Irin wannan cuɗanya da ta auku tsakanin ƙasar Hausa da ƙas ashen Turai ta haifar da sauye-sauyen al’adu da ɗabi’un Hausawa. Sakamakonsa ya wanzar da taɓarɓarewar tarbiyya a tsakanin al’ummar ƙasar Hausa.     

            Duk ƙasar da Turawa suka yi kaka-kaka gida, har suka kafa mulkin mallaka, sukan yi ƙoƙarin cusa wa al’ummar ƙasar wasu ra’ayoyi cikin zukatansu, don su rungumin hanyoyin tsarin rayuwarsu da tsarin iliminsu. Turawa kan yi ƙoƙarin gabatar da tsarin iliminsu ne ta hanyar buɗa makarantu don koyar da nau’in iliminsu. Wannan shi zai taimaka har a koyi karatu da rubutunsu, har a iya karanta littattafansu da ke kunshe da dangogin adabinsu da falsafar yanayin tsarin zaman rayuwarsu ta yau da kullum. Ta haka ne akan karanci al’adunsu da ɗabi’o’insu, sai a wayi gari su zama sun yi tasiri a cikin zukatan al’umma, musamman samari. Sannu a hankali sai su yaɗu a cikin zukatan sauran al’ummar ƙasar.

Gina Tarbiyyar ‘Ya’ya a Kan Tsarin Ilimin Boko Da babu Addini

            Babbar manufar kafa makaratun boko a ƙasar Hausa ba ta wuce ƙudurin wargaza tarbiyyar al’ummar ƙasar Hausa ba, wadda Turawa suka same su da ita. Wannan ne ya sa suka shata tsarin bayar da ilimin da ba su yi wani tanadi na koyar da ilimin addinin musulunci a cikin makarantunsu ba. Duk da kasancewar sun san cewa, koyar da addinin musulunci yana kyautata halayen yara har su kasance masu kyan hali. Shi kansa jagoran Turawan Mulkin Mallaka Lugga ya san da haka har ga abin da y ace:

                        “Dole ne gwamnati ta tsaya tsayin daka ta ga an samo wa addini

                        Gindin zama ta yadda su yaran da suka yi karatu za su zama masu

                        Kyan hali. Domin abin da addininsu ya koya musu, ko da kuwa

                        Kowane irin addini ne (Abdullahi, (b.kw) :92).”

            Haka kuma Gwamna Lugga ya nuna munin da ke tattare da bayar da ilimin boko ba tare da an gauraya shi da ilimin addini ba. Domin yin haka ya na haifar da matsalar tabarbarewar tarbiyya a tsakanin al’umma. Hasali sun ga abin da ya faru a wasu ƙasashen da aka tsara bayar da ilimin bokon da ba a surka da addini ba. Ga kaɗan daga cikin abin da ya ce:

                        “ Mai hankali hattara yake yi da abin da ya sami waninsa, domin ya

                        Wa’azantu da shi. Karatun boko ya jawo tsiya, bala’i da tajarifi a

                        ƙasashe kamar Hindu (Indiya) da Sin (China) da kuma Afirika. A

                        Sanadin yin bokon da ba a gauraya shi da addini ba. Duk wanda ya

                        yi bokon da babu addini to shi kam ya shiga uku. Domin kuwa ba zai

                        girmama iyayensa ba. Ba zai ga girman magabatansa ba. Sannan shi

                        kansa ma ba zai iya yi wa kansa wani abu na alheri ba (Abdullah (b.kw:92).

Ke nan, za a iya tabbatar da cewa a sane ne suka yi wannan tsarin domin a ɓata al’ummar ƙasar Hausa, don ƙasar ta lalace. Ku lura fa wanda yay i wannan Magana shi ne jagoran ‘yan mulkin mallakar ƙasar Hausa. Shi ne fa da kansa ya jagoranci mutanen da suka shata mana tsarin ilimin bokon da aka ƙaddamar a farfajiyar Hausa. Hasali ma shi ne da Kansa ya naɗa Hanns Vischer daraktan ilimi a ƙasar Hausa. Shi ya umurci Hanns ɗin,  ya ziyarci ƙas ashen Sudan da Masar domin ya duba yadda suke tafiyar da nasu tsarin makarantun. Amma saboda manufar da ke cikin zukatansu, sai aka ƙi bin bayanin aka aiwatar da wani abu na daban. A ka kuma ƙI gauraya bokon da ilimin addinin.

            Wani muhimmin lamari da ke ƙara tabbatar da wannan da’awa shi ne, duk da kasancewar Ɗan Hausa (Hanns) ya yi amfani da Malaman Arabiyya ta hanyar ba su horo a matsayin malaman makarantar boko na farko, da suka yi aikin koyarwa, amma ba wani tsari da ya tanadar a cikin manhajar ta Elimantare wadda ta nuna ana koyar da wani fanni da ya danganci addinin musulunci, tamkar yadda ya tarar ana aiwatarwa a Sudan da Masar. Abin da kawai suka yi shi ne ƙyale ɗaliban su halarci masallacin juma’a da makarantar Muhammadiyya, domin sallar juma’a da kuma ɗaukar darussan addinin musulunci a wuraren malaman azure (Graham, 1966:87). Ƙarawa da ƙarau, albashin da ake biyan malaman Arabiyyar bai taka kara ya karya ba. Haka malamin Arabiyyar da ya tafi ƙasashen Larabawa wajen ƙaro ilimi, albashinsa bai kai na wanda ya je ƙasar Turai ba ( Mahmud, 1988:6-9).         

 

 Me Aka Fa’idantu Da shi A Shirin Nasu?

            Dun tsawon lokacin da ‘yan mulkin mallaka suka yi suna gudanar da makarantun bokon ƙasar Hausa, har zuwa watan Satumba na shekarar 1913, lokacin da suka ɗaga darajar Makarantar Elimantare ta Katsina zuwa  Makarantar Lardi, wadda ke ƙarƙashin kulawarsu, ba wata fa’ida da ɗaliban suka samu in aka cire wasannin motsa jiki, waɗanda suka ƙaddamar irin na ƙas ashen Turai. Wasannin sun haɗa da: rawar soja, da ƙwallon ƙafa, da ƙwallon gora da sauran su (Graham,1966:95). Sun yi hakan ne domin su kawar da hankalin ɗaliban daga karatun Muhammadiyya, su karkata ga wasannin. Domin a daidai lokacin da ake wasannin ne suke zuwa ɗaukar karatun na muhammadiyya. Ke nan a kaikaice an cin ye lokacin ɗaukar karatun. Kuma ba a fito fili ƙarara aka ce an hana su ba.

             Katsina Kwalej, wadda aka buɗe a shekarar 1921, an sake tsarin bayar da iliminta daga falsafar ilimin Islama zuwa falsafar ƙasar Turai da al’adun yammacin Turai. Don haka aka mayar da darasin Ingilishi mafi muhimmanci a makarantar. Kuma ya zama harshen sadarwa a tsakanin ɗalibai, wanda suke amfani da shi a sauran lamurran rubuce-rubucen yau da kullum (Director, 1913:50). Amma fa duk tsawon lokacin da aka yi ana karatun boko ba wasu darussa na kimiyya da ake koyarwa. Sai daga baya, lokacin da aka fara gudanar da makarantu tamkar yadda ake tafiyar da su a Kudu. A lokacin ne aka soma horar da ɗaliban Katsina Kwalej yadda za su zauna jarabawa da ake shiryawa daga waje. Aka kuma fara koyar da su darussa kamar Physic da Biology da Chemistry. A shekarar 1949 ɗaliban makarantar suka soma zauna jarawar samun takardar shaida ta Cambridge, bayan shekaru 28 da kafuwar makarantar (Ozigi & Ocho, 1981:52). Me ya haifar da haka? An yi ƙanfar ɗaliban ne ko yaya? Ko malaman da za su koyar da irin waɗanca darussan ne babu? To me aka karantar da su a makarantar tun wanca tsawon lokacin? Tambayar da ke buƙatar mai karatu ya natsu yay i tunani a kan amsarta cikin natsuwa da basira.  

            Duk lokacin da aka shata horar da mutun a kan wata sana’a to lallai ne akwai matakai da akan bi don cimma manufar da aka sa a gaba. Haka ko lokacin da Turawa suka zo sun tarar da mu da namu tsarin ilmantarwa. Kuma abin mataki-mataki ne, har ɗalibi ya kai wani matsayi da zai zama malami. Amma a tsarin nasu, ba haka suka soma shi ba. Dalili kuwa shi ne, sai da aka ɗau tsawon shekaru 40 ana karatun bokon a ƙasar Hausa kafin Turawa su ba da sukolashif ga ɗalibai don su zurfafa karatun nasu. Anya kuwa sun so mu ci gaba ke nan. Domin sai a 1945 suka soma tura ɗalibai Jami’ar London , don ƙaro karatu. Rukunin farko su ne: Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa, da Mamman Kano, da Shatima Kashim Ibrahim, da Salisu Hayi Ilorin, da Abdurrahman Okene, da kuma Yahaya Bauchi. A shekarar 1946 aka tura rukuni na biyu waɗanda suka haɗa da: Malam Aminu Kano, da Shatima Ajiram, da Salihu Ilorin, da kuma Mr. Dimka ( Kano, 1989:13-14).

            Fahimtar da wasu masu kishi yankin, wato ‘yan bokon farko suka yi, na makircin da ake shiryawa yankin ya sa su yin yunƙurin tura ‘ya’yan yankin waje karatu a ƙasar waje ta hanyar karo-karo da suke yi daga cikin albashinsu.  A shekarar 1949, ‘yan bokon Nijeriya ta Arewa suka fara ɗibar ‘yan makaranta mutun 7 suka kai su Ingila don su yi karatun sakandare har zuwa Jami’a a fannoni daban-daban da suka haɗa da ilimin injiniya da lauya da likitanci. Wannan ya tilasta wa ‘yan mulkin mallaka ba ‘yan Arewa damar zuwa Kwalejin Yaba (Yaba College) da ke Legas don zurfafa karatunsu. Kafin lokacin , Alhaji Sa’adu Zungur ne kaɗai aka tura makarantar, inda ya karanci fannin haɗa magani (Chemist). Amma aikin da suka ba shi bai da nasaba da abin da ya karanta (Kano, 1987:17). Mai karatu na iya cewa, me ya sa ‘yan bokon farko na ƙasar Hausa, waɗanda Turawa ne suka koyar da su, suka kasance masu gaskiya da rikon amana ga kwarjini a idon jama’a? Amsar wannan tambaya mai sauƙi ce. Domin kuwa alheri ya riga ya zauna cikin zukatansu tun suna ƙanan. Hasali ma akasarin su  sun mallaki ilimin addinin musulunci, wasu har sun zama malamai, sun yi aure har da ‘ya’yansu ko da suka soma ɗalibta a makarantun bokon (Ɗalhatu,2002:161).

Kauce Wa Tsarin Tarbiyyar Gargajiya (al’ada)

            Tun kafin bayyanar musulunci a ƙasar Hausa, tun iyaye da kakanni al’ummar Hausawa suka mallaki wasu kyawawan ɗabi’u da suka ɗabi’antu da su. Yayin  da addin musulunci ya bayyana a ƙasar Hausa, sai ya ƙara ƙarfafa su, har suka tabbata a cikin zukatan al’umma. Suka yi amanna tare da ɗaukar wa kansu cewa, aikin kowa da kowa ne ya kula da gyaran tarbiyyar yara, a duk inda  ya ci karo da buƙatar haka.  Ba sai ‘ya’yansa ba. Wannan shi ya sa kowa ke bayar da tasa gudummawa wajen gina kyakkyawar tarbiyya ta gari a tsakanin al’umma, musamman lamarin tarbiyyar yara maza da mata. A sakamakon  haka ne tsofaffi mata kan tara yara da dare suna yi musu tatsuniyoyi da ke ƙunshe da wasu darussa da ke cusa tarbiyya a cikin zukatan al’umma. Amare mat aba a bar su bay aba, wajen gudanar da irin waɗannan darussa da ke ɗauke da hannunka mai sanda game da lamurran rayuwar duniya. Yayin da manya maza kan halarci matattarar ilimi da wa’azi, inda ake fassara nassoshin Alƙur’ani da Hadisai tare da hikayoyi masu ɗauke da muhimman darussa da suka danganci rayuwar duniya da lahira. Tasirin wannan lamari ba ƙarami ne a rayuwar Hausawa. Kuma shi ya sa idan Bahaushe ya kai mizanin wasu shekaru ko da yana ashararanci, zai yi ƙoƙarin kama kansa ta hanyar ƙaurace musu. In ma bai daina ba akwai matakan ladabtarwa da al’umma kan ɗaukar masa.

            Yayin da Turawa suka zo ƙasar Hausa kuwa, sai suka kawo tsarin karatunsu , suka ƙaƙaba wa al’umma shi, son su da ƙin su, dole aka koye shi. Suka tsara ba wanda zai wasu mƙamai, sai wanda ya koyi karatunsu. Karatun kuma a kullum safiya ƙoƙarin tabbatar da tsarin danniya da mulkin mallaka yake yi. Sun yi ƙoƙarin karkatar da matasanmu zuwa ga addininsu, tare da kawar da tsarin ilimin addinin musulunci da salon rubutun da suka tarar muna amfani da shi, wato Larabci da ajami. Sun maye hanyoyin tarbiyyarmu ta gargajiya da irin tasu, mai yaɗa alfasha da fajirci a tsakanin al’umma. A ɓangaren adabi kuwa, sun gabatar da fasalin nau’o’in  adabinsu da ke ƙunshe a cikin littattafai da jaridu da mujallu masu koyar da ayyukan assha. Haka sun yi amfani da gidajen sinima da akwtunan talabijin da na bidyo da na’urorin tauraron ɗan Adam da suke watsa fina-finai da ke koyar da ayyukan assha da zare tausayi da kunya a tsakanin matasa maza da mata. Da irin waɗannan abubuwa ne suka maye gurabun ɗakunan tsofaffi da na amare, har ma da matattarar ilimin addini. Ai dole ne tarbiyya ta taɓarɓare ƙasa ta lalace al’ummar ƙasa su auka cikin masifu da fitini iri-iri.

            Tasirin da waɗannan abubuwa suka yi a cikin zukatan matsa ba ƙaramar illa ba ce a sha’anin tarbiyyar al’ummar ƙasar Hausa. Sakamakon haka ne, wasu magidanta kan yi husuma, ko su garzaya gaban hukuma don an ladabtar da ‘ya’yansu a waje. Wasu ma har sukan yi tashin hankali a tsakaninsu da ƙannansu ko yayyinsu, don an kwaɓi ‘ya’yansu a kan aikata ba daidai ba. Irin wannan lamarin har ya kai inda ɗa kan zargi mahaifisa da cewa wai ya ɗora ɗansa karan tsana. A wasu lokutan har akan sami canza yawu a tsakanin uba da ɗansa. Wannan rashin tarbiyya ya kai matuƙa, har kunya ta fice daga idanun al’umma. Ina mafita take?

            Hausawa kan ce: “ in ka so naka, ka so shi kai kaɗai. Idan ka ƙi shi duniya ta so shi. Wannan zance haka yake. Duk lokacin da mutun ya nuna ba ya so abin da zai ɓata wa ɗansa rai, to shi wata rana sai ya ga ɓacin rai da baƙin ciki iri-iri da zai fito daga wajen ɗan nan nasa. Kafin bayyanar wannan yanayi, iyaye ba su cika nuna wa ‘ya’yansu jin daɗi ba kama yanzu ba. Amma karance-karance adabin Turawa da yawan kalle-kallen fina-finansu yay i mummunan tasiri a zukatan al’umma. Sakamakon haka ɗin ne ya sa iyaye mata suka taka muhimmiyar rawa wajen taɓarɓarewar tarbiyya. Sau da yawa yaro tun yana goye wasu iyayen ke ɓata shi, ta hanyar saya masa duk wani abu da ya gani , ya nuna yana so. Irin haka kan kai ga  sa yaro kuka, idan ya ga wani abin da yake buƙata. Wani zubin  in ya ga wani abu ko ba nasa ba ne, zai nemi a bas hi. Har akan sami waɗanda kan yi faɗa don su mallaki abin.  Daga irin haka ne birbishin sata kan yi naso a cikin zukatan yara, har su kai ga ɗauke kuɗin iyaye don su biya buƙatunsu.

            Ta fuskar matasa da ke karatu a makarantun sakandare kuwa, wasu iyaye ne kan ɓata tarbiyyar yaransu. Wannan kan faru ta hanyar ba su maƙudan kuɗi in za su koma makaranta. Da isar su makarantar, sai su watsar da karatun su shiga yawace-yawacen shashanci tare da abokai maza da ‘yan mata, ba su wannan gida disko ba su wancan. Daga haka sai aga yaro ya faɗa ciki wasu munanan ɗabi’u, kamar caca da shan giya da neman mata da sauran su. Duk lokacin da babu kuɗin, mai ba shi kuma ya kau, sai ya fantsa fagen ‘yan sace-sacen kayan hukuma in ya sami aikin ko na al’umma.

Rashin Ba Da Kyakkyawar kulawa Ga Samari

            A bisa al’adar ƙasar Hausa, yayin da yaro ya kai matakin  samartaka, akan jawo shi a jiki na jan hankalinsa ana lurar da shi abubuwa nagari masu amfani ga rayuwa ta yau da kullim. Ana kuma bas hi damar yin walwala gwargwadon hali, tare da yi masa gargaɗI akai-akai. Haka akan tanadar masa matsugunni a gidansu, don a sami damar kula da irin take-takensa.

            Saboda wayewar zamani, iyaye sun yi sakaci sun yi watsi da nauyi da mahalicci ya ɗora  musu. Irin wannan wayewa ta haddasa taɓarɓarewar tarbiyya a duk faɗin ƙasar Hausa. Domin an ɗauki cewa yana da ‘yancin walwala, don haka yana iya zama duk inda ya so. Wani lokacin saurayi kan yi sati ko fiye da haka bai leƙa gidansu ba, ba tare da iyayen sun damu ba.

            Waɗanda ma suka tanadar da matsgunni ga saurayi, sai ka tarar an keɓe shi can inda babu wanda ya damu da abin da yake aikatawa, balle a rinƙa taka masa birki, hasali ma an yi masa tanadin akwatin talbijin da bidiyo da makamantan su, da ke iya zama sinadarin taɓarɓarewar tarbiyyarsa. Domin ta irin waɗannan kafofi ne ake kallo yadda ake aikata miyagun ɗabi’u, kamar fashi da makami da fyaɗe da sata kisan kai shaye-shayen maye da sauran lamurran ta’addanci.

Kammalawa

            Duk da kasancewar tsarin mulkin ƙasar nan ya amince gwamnati ta sa baki tare da kyautata lamurran addini da al’adaun gargajiya, amma waɗanda ke da alhakin yin sun yi wa lamarin riƙon sakainar Kashi. Sakamakon haka ne, ya haifar da rashi yi wa ilimin addini kyakkyawan tanadi a cikin manhajar makarantun ƙasar nan tun lokacin da aka soma kafa su. Wannan ba ƙaramar illa ya yi ba wajen haddasa taɓarɓarewar tarbiyyar al’ummar ƙasa. Domin bayar da ingantaccen ilimin addinin musulumci shi babbar madogara wajen shimfiɗa harsashen ginin sahihiyar tarbiyya. Domin shi ke koyar da nagartattun halaye da ke ɗauke da mutunci da gaskiya da riƙon amana da alkunya da girmama kai da ƙaunar juna ga kuma tsoron Allah a ɓoye da bayyane. Irin waɗannan halaye ne suka yi tasiri a rayuwar magabatanmu, a sakamakon samun kyakkyawar tarbiyyar addinin musulunci da suka yi, shi ya sa Turawa ke ganin kwarjininsu, har suka yabi addinin musulunci. Ga abin da Sir. Herry Johnston y ace:

                       

“Addinin Musulunci wata babbar rahama ce ga duk ɗan Afirika da ya

                        Rungume shi. Domin yana sa shi ya zama mai tsoron Allah, mai jaruntaka

                        Da ƙarfin zuciya, mai mutunta kansa, kuma mutum mai kazar-kazar don

                        Tabbatar da kansa” (Abdullahi,(b.kwt):25).

Abubuwan da suka yi ƙamfa a rayuwar mafi yawan jagororin ƙasar nan. Saboda rashin ingantacciyar tarbiyyar addinin musulunci. Sakamakon haka ne ya haifar da rashin tsoron Allah a cikin zukatansu. Aka wayi gari suka auka cikin ɓarna iri-iri tare da wawure dukiyar, wanda ya jefa al’ummar ƙasa cikin wani hali na ni-‘yasu.

 

Manazarta 

Tuntuɓi mai takarda.

Post a Comment

0 Comments