Takardar Da Aka Gabatar A Taron Ƙara Wa Juna Sani Na Ƙasa Na Farko A Kan Harshen Hausa, Adabi Da Al’adu, A Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya A Jami’ar Bayero Da Ke Kano, Litinin 14-16 Ga Janairu, 2013.
Gudunmawar Makadan
Hausa Ga Al’ummar Najeriya; Misalai Daga Waƙar Hada Kan Najeriya
Ta Musa Ɗan Ba’u
ALIYU RABI’U ƊANGULBI
GSM NO. 07032567689
E-mail: aliyurabiu83@gmail.cim
1.0 GABATARWA
Hakiƙa irin rawar da mawaƙan baka na Hausa ke
takawa wajen fadakar da al’umma game da halin da ƙasa take ciki ba ƙarama ba ce, kuma sun
cancanci yabo.
A duk lokacin da wata
matsala ta tusgo, shugabanni ko Gwamnatin Tarayya da Jihohi da kuma Ƙananan Hukumomi sukan
rika tuntuɓar mawaƙan baka na Hausa da su
rera waƙa don su faɗakar da jama’a a kan wannan buƙata. Dangane da irin
wannan kira da Gwamnati kan yi wa mawaƙa ya sa su mawaƙan kan tsaya su kalli
matsala, sannan su shirya mata waƙa da za ta wayar ma
da mutane kawunansu da kuma ilmantar da su ga wani sabon abu da yake gudana a Ƙasa.
Najeriya ƙasa ce mai faɗi da yawan ƙabilu daban-daban da
babbancin addinai da al’adu. Ana hasashen cewa akwai aƙalla kimanin ƙabilu ɗari ukku da casa’in
da huɗu – (Source: K.
Hansford and J.B Samuel: Studies in Nigerian Languages, No. 5 1976, pp 33-366).
Don haka duk ƙasar da ke da yawan ƙabilu da addinai daban-daban
kamar Nijeriya yana da wuya a sami ingantaccen haɗin kai da zaman lafiya da tsaro.
Ganin irin yadda waɗannan matsaloli na
rashin zaman lafiya da hadin kai da tsaro ke aukuwa a ƙasar nan ya sa wannan
takarda ta yi tsokaci a kan waƙar da Musa Ɗanba’u gidan Buwai ya
rera, mai taken “Hadin kai a NIjeriya”, domin jawo hankalin yan Nijeriya da su
zauna lafiya da junansu, don a sami bunƙasar tattalin arziki
da haɗin kai da tsaro;
misali:-
G/Waƙa: ‘Yan Nijeriya, yan uwa mu yi ƙoƙari,
Amshi: Mu zan haɗa kanmu mu kama hanyar gaskiya“
2.0 MUSA ƊANBA’U
Yana da kyau kafin a yi nazarin waƙar Musa Ɗanba’u a kawo taƙautaccen tarihin rayuwar Musa Ɗan Ba’u. Musa shi ne sunansa na
yanka, Ɗanba’u kuwa laƙabi ne da mahaifiyarsa ta sa masa, saboda al’adar Bahaushe ta alkunya,
wannan suna na Ɗanba’u da shi aka fi saninsa, kuma ake kiransa tun yana yaro ƙarami. Da ya manyata aka
cigaba da kiran sa Musa Ɗanba’u Gidan Buwai wato ana kiran sa da sunansa na yanka
da laƙabi da kuma sunan garinsu.
An haifi Musa a garin gidan Buwai a ƙaramar hukumar mulki ta Illela, a Jihar Sakkwato a
Shekarar 1955, kuma mahaifansa su ne, Malam Abdullahi Maigwangwa da Malama
Aminatu, ya yi karatun Allo a makarantar Malam Mai Littafai. Musa ya yi gadon
waƙa ne daga Mahaifinsa Audu Gwangwa wanda shi makaɗin goge ne, amma kuma idan lokacin damina ya zo sai ya
koma gona don noma abinci. Shi dai Musa ya yi Sha’awar waƙa daga sana’ar babansa. Ya tashi
yana sha’awar waƙa, kuma yakan tara yara yan uwansa ya riƙa rera masu waƙa a dandalin wasannin dambe da
kokuwa. Musa Ɗanba’u shi ka ɗai yake yin waƙarsa a wancan lokaci, watau bai da mai yi masa amshi. Ya kuma soma waƙa a lokacin da ya
fahimci hazaƙa da basira sun zauna masa a kai, ya tanadi kayan kiɗa da masu taimaka masa da kiɗa da amshi da dan ma’abba (Kwando). Ya yi fice a fagen waƙar kokuwa a kowane lungu
na jihar Sakkwato da jamhuriyar Nijer da Sauran jihohin Arewacin Nijeriya
daban-daban.
Da siyasa ta shigo a shekarar 1979 sai “ya’yan jami’yyar NPN; ɗaya daga cikin jam’iyyu guda biyar da muke da su a wancan
lokaci suka buƙaci Ɗanba’u ya yi wa jam’iyyarsu waƙa. Mawaƙin na kokuwa ya shirya wa jamiyyar NPN waƙa, wadda ta zama
sanadiyar karɓuwar jam’iyyar ga mutanen Sakkwato
da sauran masu sha’awar siyasa. Sauran jam’iyyu hudu na ƙasa su ne, (N.P.P, U.P.N, G.N.P.P DA P.R.P). Daga wannan lokaci sai Musa ya bar
waƙar kokawa ya koma mawaƙin siyasa da sauran jama’a daban daban. A halin yanzu
Musa Ɗanba’u yana cikin shahararrun mawaƙan Hausa da suka yi fice a fagen waƙoƙin siyasa. Musa yana zaune a Illela da
iyalansa, yana da matan aure da yaya da dama.
Alhaji Musa Danba’u ya shiga baje kolin hajar tunanensu wajen faɗakarwa da kuma wayar da kan jama’a game da amfanin haɗin kai da zaman lafiya.
Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai ya rera waƙarsa, mai gindi,
Ɗan Ba’u: ’Yan Nijeriya yanuwa mu yi
kokari,
Amshi Mu zam hada kanmu
mun kama hanyar gaskiya”
Ɗanba’u ya tsara wakar ne
ta yin la’akari da yadda Nijeriya take mai fadi da yawan ƙabilu da banbancin addinai da al’adu
inda ya danganta haɗin kai da zaman lafiya da cewa su ne ginshikan cigaban kowace kasa da bunƙasar tattalin arzikinta,
ba wai Nijeriya kaɗai ba.
3.0 MATAKAN DAƊA HAƊA NAJIRIYA A
TUNANEN WAƘA
Haɗin kai shi ne, haɗuwar mutane masu ra’ayi ɗaya, ko daban-daban a wuri ɗaya tare da fahimtar juna, domin su aiwatar da ayukkan
cigaba ba tare da nuna wariya ko banbancin addini ba (Danmaraya Jos). Inda duk
al’umma ta haɗa kanta wuri ɗaya, to babu shakka yana da wuya a raba su balantana a
jefa su cikin rikici da kiyayya da junansu. Rashin hadin kan al’umma yana
haddasa fitina da faɗace-faɗace da ka iya rushe cigaban ƙasa ta kowane fanni.
3.1 GARGAƊIN ’YAN BARANDA
Mutane ne masu kai kawo, suna sayen haja daga hannun waɗanda suka sarrafa ta na asali suna kaiwa wata kasuwa ko
kamfani suna sayarwa domin su sami riba. A nan Musa ya kamata America da Ingila
da Faransa a matsayin yan barandar Siyasa da ke shiga a cikin wata ƙasa su sami labari su
tafi su watsa a duniya ta kafafen watsa labaransu. Irin waɗannan ƙasashe, su ne Ɗanba’u ke kira da suna yan baranda, sannan yana kiransu
da su daina yimana shisshigi ga ƙasarmu domin kada su roshe haɗin kanmu; ga abinda yake cewa.
Ɗanba’u: Ƙasashen da ka shisshigi haɗin kan mu ya wargaje
To Najeriya ta
yi sayyu ta kafu
Amshi: Munafuccin nasu ba
za ya gurguntamu ba
3.2 GARGAƊIN YAN ZAMBAR
CIKI
Yan zambar ciki, su ne
mutanen cikin gida/ƙasa waɗanda aka amince masu, amma da haɗin kansu ne yan baranda ke yiwa ƙasarsu zagon ƙasa, watau suna sayar da labaraii ko
kwashe asirin ƙasa, suna sayarwa ga yan baranda domin su sami wata biyan buƙata taƙashin kansu, saboda haka
ne, mawaƙin ya gargaɗi jama’a da su kaucewa yin hulɗa kowace iri da su domin kada su jefasu cikin rikicin
siyasa da addini da ƙabilanci da ka iya ruguje haɗin kai da zaman lafiya a Najeriya. Ga dai abinda yake cewa:
Ɗanba’u Kam mu yarda da yan
baranda da yan zambar ciki
Masu son su haɗamu barna su koma tsallake
Amshi: Idan ta rikice su buƙata ta biya
Haka zai iya kawo munafukai da marasa kishin ƙasa da ‘yan barandar siyasa su kutso kai su rika watsa jita-jita
da ƙirƙiren karya domin su watse haɗin kan al’umma da rushe tattalin arzikin ƙasa.
Alhaji Musa Ɗanba’u ya rera waƙa don ya gargaɗi masu irin waɗannan dabiu su daina, haka kuma ya
kira yan Nijeriya masu yi wa Nijeriya zagon ƙasa da su yi wa Allah su daina kaiwa
da komawa ga abin da zai ruguje hadin kan ƙasa. Musa Ɗanba’u yana cewa.
Musa ya bayyana siffar munafukan Nijeriya a matsayin “Yan baranda da kuma
yan zambar ciki” a sigar mutane biyu, watau yan baranda su ne wadanda ke sayen
haja daga hannun wasu su tafi su sayar don su ci riba. Su kuwa yan zambar ciki
mutane ne yan ƙasa da aka amince masu, amma suna amfani da damar da aka ba su, suna yi wa ƙasarsu zagon ƙasa. saboda haka ne mawaƙin ya yi gargadi ga
jama’a da su kaucewa hulɗa da su don ka da su jefa su cikin rikice-rikicen addini da ƙabilancin siyasa.
3.3 KIRA KAN ZAMAN LAFIYA
Hausawa suna cewa; “Zaman lafiya ya fi zama dan Sarki, amma masu iya magana
sunce, “Ko Sarkin ma ya fi". Zaman lafiya shi ne ginshikin cigaban ƙasa da haɗin kan al’umma. Idan babu zaman lafiya, yana da wuya a
sami haɗin kai da fahimtar juna, Danba’u yana
cewa:
Ɗanba’u: “Na ɗai haɗin kayin ƙasa, ka ga ba zai samu ba,
Amshi: Sai da
zama lafiya muy yi fahimta yan uwa.
Idan aka yi maganar haɗin kai to dole
ne a yi tunanen kauda ƙabilanci a cikin al’umma. Domin nuna ƙabilanci da banbancin
addini suna taimakawa ga ragujewar zaman lafiya da fahimtar juna a ƙasa; Misali.
Ɗanba’u: Kun gani Najeriya mai yawan faɗin ƙasa
Al’adunmu daban-daban,
addinan mu daban daban
Allah mai ƙaddaroƙa a kowane al’amar
Amshi: Shi ya ƙaddaro mun ka zauni
wuri ɗaya
Kuma gidan mu yana ɗaya.
Ƙabilanci shi ne, nuna
banbancin launin fata, ko yare ko addini ko al’ada. Ƙabilanci yana faruwa
ne a ƙasa da ke da yawan ƙabilu daban-daban,
inda kowace ƙabila take nuna jin kanta da ganin fifiko bisa ga wata ƙabila ko nuna bangaranci,
ga wasu rukunin jama’ar ƙasa ko yanki. Misali:-
Ɗanba’u: Kifi da kada da ƙwado, da tsari,
dorina,
Halittarsu daban- daban,
amma in mun tuna,
Amshi: Duk gidansuu yana ruwa
Ɗanba’u: Ina Yarbawa, Nufawa, ina jama’ar Ibo,
Harda ku jama’ar Tibi
Amshi: duk mu taru muje gaba ɗai mu koma ‘yan uwa
Duk ƙasar da ke da yawan ƙabilu irin Nijeriya,
babu shakka ba za a sami cikakken haɗin kai ba, sai idan shugabanni sun tsayar da
adalci wajen raba mukaman gwamnati da arzikin kasa dai-dai. Saboda haka idan
har ana son a sami zaman lafiya da haɗin kai ya ɗore, to dole ne a tabbatar da tsarin raba
dai-dai ya yi tasiri a Nijeriya. Yin haka zai sa a kawar da ƙabilanci da bangaranci
da ke haifar da faɗace-faɗacen addini da siyasa
a kowane lungu na ƙasar nan.
Mawaƙin ya siffanta ƙabilun Najeriya da halittun da ke cikin ruwa wadanda ke da dangantaka ta
wurin zama, misali kifi da kwaɗo, da kada da tsari dukkansu yan uwan juna ne, watau yan kwai ne, sannan
kuma dukkansu cikin ruwa suke zaune. Haka ita ma dorina cikin ruwa take zaune
duk da kasancewa ita ba yar kwai ba ce. Don haka a ganinsa waɗannan halittu masu asali ɗaya da mazauni wuri ɗaya bai kamata su ƙyamaci junansu ba. Haka kuma abin yake ko ga mutanen Nijeriya
irin su Yarbawa da Nufawa da Ibo da Tibi da Hausawa da Fulani da sauran ƙabilun Nijeriya waɗanda ƙaddarar Allah (SWA) ta haɗa su wurin zama ɗaya, watau ƙasa ɗaya. Wannan magana ta Danba’u gaskiya
ce domin idan“yan Nijeriya suka fahimci haka dole ne su kasance masu hakuri da
juna, su haɗa kai don a sami cigaba da bunƙasar tattalin arzikin ƙasa. Malamin yana fatar alhairi
da yi wa ƙasar adu’a kamar haka:
Ɗanba’u: Ni ɗan Najeriya kai ɗan Najeriya
Ke yar
Najeriya ita yar Najeriya
Amshi: Ku mu zauna da juna
mu yi hankuri
3.4
TUNI KAN KYAWAWAN
HANYOYIN SHUGABANCI
Kyakkyawan shugabanci ya dogara ne ga irin
mutanen da aka baiwa jagoranci; idan ana son a sami kyakkyawan shugabanci na
gaskiya da riƙon amana da adalci a ƙasa, dole
ne a zaɓi mutane masu amana da mutunci da dattako da kishin ƙasa. Ka da
a zabi masu tunanen tara abin duniya don ɗai su ji daɗi da su da iyalansu. Shugabanci na gari shi ne a yi rikon talakkawa da
adalci watau a bai wa kowa hakkinsa da ya dace, ba tare da ha’inci da son
zuciya ba, ko nuna ƙabilanci ko bangaranci ba. Musa Danba’u ya ba da
misalai na wasu shugabannin ƙasa, masu adalci da rikon amana
da kishin ƙasa waɗanda suka taka rawar gani wajen
bunƙasa haɗin kan ƙasa da
samar da zaman lafiya da bunƙasa tattalin arziki. Waɗannan dattawa sun haɗa da, Sir Ahmadu Bello
Sardaunan Sakkwato (firimiyan Jihar Arewa) da Sir Abubakar Tafawa Balewa
(firayiministan Nijeriya), da Dr. Nnamdi Azikuwe, da Sir Muhammadu Ribaɗo Yola da Sir Kashim Ibrahim da sauransu. Manufar waɗannan shugabanni ita ce su haɗa kan Najeriya da bunƙasa tattalin arzikinta. Hausawa sun ce “yabon gwani ya zama dole“, saboda
haka ne Musa Danba’u yake tunatar da masu riƙe da
mulkin ƙasa da talakawa game da irin ƙwazo da waɗannan shugabanni suka nuna wajen samar da haɗin kai da zaman lafiya a Nijeriya ya zama abin yabo, wanda har abada ba
za a manta da su ba a tarihin Nijeriya. Don haka Danba’u yake kira da ayi koyi
da su, yana cewa:
Ɗanba’u: “Sir Ahmadu Bello shi
da Tafawa
Sannan Ribaɗo Muhammadu
Amshi: Sun dage ƙwarai namu yanci ya fito.
Ɗanba’u: In Sir Kashim na
Sardauna Ahmad Bello
Dattijo Baba Mazan Jiya
Amshi: Irin hikimakku ba za mu mancikke ta
ba.
Ɗanba’u: “In ga dokta Namandi,
Sannan da Awolawo ciki
Janaral Murtala ga Aminu garin Kano
Amshi: Sun hada kammu ba za mu mancikke su
ba.
Har wa yau Musa ya yi ƙoƙari ya nuna wa jama’a irin namijin ƙoƙarin da
shugabannin Sojoji da yan siyasa suka yi irin su Obasanjo da sani Abacha da
Ibrahim Babangida da Buhari suka yi wajen samar da haɗin kai abin a yaba ne. Ya cigaba da cewa;
Ɗanba’u: “Obasanjo da Shehu
Shagari,
Sa da Buhari Dattijo sai Babangida,
Da Sani Abacha Dattijo mai son gaskiya
Manufarsu guda haɗin kan ƙasar Nijeriya
In sunka hada ta tat tashi lebur
tayyi tsaf
Amshi Ɗan
Nijeriya ba ya shawar wata ƙasa.
Mawaƙin ya yi kira ga yan Nijeriya,
musamman ma shugabanni da su yi koyi da shugabannin da suka taka rawa wajen
hada kan yan Nijeriya da kawo cigaban ƙasa. Rashin kyakkyawan shugabanci yana haddasa taɓarɓarewar haɗin kai da zaman lafiya da
rashin aikin yi da tsaro a cikin ƙasa.
Don haka Ɗanba’u ya ƙara da kiran yan Nijeriya baki ɗaya, musamman yan siyasa da sauran jama’a waɗanda aka zaɓa domin su sake gyara kundin tsarin mulki da cewa suyi koyi da su
Sardauna. Yana cewa:
Ɗanba’u: Wakilanmu da ke Abuja
ku dage dai ƙwarai
Tsarin mulkin ƙasa, wanda shi muka sa gaba
Amshi: Ku ɗauki halinsu don kam mu
faɗa gargada.
3.5 BUNƘASA TATALIN
ARZIKI
Kowace ƙasa ta duniya tana alfahari da tinƙaho da albarkatun ƙasa da take da su. Nijeriya tana daga cikin ƙasashen duniya da Allah
(SWA) ya albarkata da nau’ukan ma’adinai da albarkatun ƙasa irin su manfetur, zinari,
azurfa, tantalayi da sauran albarkatun gona da suka haɗa da auduga, da gyaɗa, da koko da sauransu. Idan ƙasa tana bukatar arzikinta ya bunƙasa, dole ne ta tanadi hanyoyi da zata
haƙo ma’adinanta da bunƙasa harkokin noma. Dalilin haka ne Musa Danba’u ya yi
kira da kuma gargadi ga hukumar Nijeriya da ta lura da irin albarkatun ƙasa da take da su don ta
kafa kamfuna da za su sarrafasu,
tattalin arzikin ƙasa ya bunƙasa. Musa ya kawo sunayen ma’adinai da albarkar gona da muke da su kamar
haka:
Ɗanba’u: “Albarkar ƙasa ba kamar Nijeriya
Akwai zinari da fetur cikin Najeriya
Amshi: Akwai koko, gyaɗa, auduga na nan ciki.
Haka kuma Ɗanba’u ya ƙara da fadakar da al’umma game da masanantunmu inda yake cewa:
Ɗanba’u: In kamfuna da dama cikin Nijeriya
Masana’antu da dama cikin Nijeriya,
Amshi: Saboda hakan ga mu
ba mu kyashin wasu.
Ɗanba’u: “In kamfunan da muke da su, masana’antun mu,
Amshi: Duk mu adda abinmu mun
daina bayarwa aro“
Ɗanba’u: In kaya na aro idan
sun zame ba naka ba
Amshi: Da ka gama moriya sai
ka maida mai gida
Duka abubuwan da Musa ya ambata game da tattalin arzikin ƙasa ba za a amfana da su
ba irin yadda ya kamata sai fa idan an sami kyakkyawan shugabanci a ƙasa.
4.0 KAMMALAWA
Kamar yadda wannan takarda ta nuna makaɗan hausa sun taka rawa wajen haɓɓaka siyasa a Najeriya, Musa Ɗanba’u na ɗai daga cikin su, wanda ya duƙufa ga faɗakar da yan Najeriya da kuma yi
masu gargaɗi ga me da amfanin haɗin kai, musamman wajen samar da zaman lafiya, bunƙasar tattalin arziki, kyawawan shugabanci da
sauransu, wannan maƙala ta kawo takaitaccen tarihin
Musa Ɗanba’u da irin rawar da waƙar sa ta haɗa kan Najeriya ta taka wajen
fito da matakai daban daban da za’a yi amfani da su domin a gina ƙasa da samar da haɗin kai.
Harwa
yau maƙalar ta taɓo hanyoyin da waƙar take gani sune mafita da warware rickicin
siyasar Najeriya domin a samu kyakyawan shugabanci, hanyoyin kuwa su ne; zaɓen mutane dattijai masu gaskiya da riƙon amana, irin su Sa Ahmad Bello Sardauna, da
Abubakar Taɓawaɓalewa da Malam Aninu Kano, da
Dakta Namandi Azukuwai da sauransu.
Zaɓen irin waɗannan mutane, a tunanen waƙar shi zai kai Najeriya ta samu cigaba ta fusar
bunƙasa tattalin arziki da haɗa kai da zaman lafiya.
Najeriya ƙasa ce mai albarka da yawan ƙabilu da addinai daban-daban wadanda ke buƙatar ingantaccen haɗin kai da shugabanci na gari. Irin wannan matsayi da Allah (SWA) ya yi wa
Najeriya ya sa ƙasashen duniya sun sa mata ido da yi mata
barazana da maƙarƙashiyar rugujeta ta hanyar
haddasa rigingimun siyasa da ƙabilanci da addini.
Danba’u ya wayar wa jama’a da kawunansu ta hanyar
waƙar hada kan Nijeriya da ya yi a shekarar 1993
lokacin da rikicin siyasar 1993 ta yi kamari (Watau rikicin Jun 12), ya gargadi
yan Nijeriya da su kula da irin kisisina da makirci da Yahuɗawa, watau Amerika da Ingila da Faransa suke kullawa don su hassasa
fitina da za ta rosa haɗa kan yan Nijeriya. Idan “yan Nijeriya ba su haɗa kai ba, suka zama tsintsiya maɗaurinki guda, babu shakka
munafukai na cikin gida da yan barandar siyasa za su cimma burinsu na wargaza
hadin kan al’umma da rushe tattalin arzikin ƙasa. Saboda
haka ya kamata a farka a natsu domin a sami ingantaccen haɗin kai, a kauce ma rigingimun ƙabilanci da rikicin addini da
siyasa da ka iya kawo hassarar rayuka da dukiyoyin al’umma.
Tabbatuwar haka ba zai samu ba sai da samun
kyakkyawan shugabanci na mutane masu dattako da adalci da rikon amana. Don haka
samun kyakkyawan mulkin dimokuraɗiya a ƙasa ya
dogara kacokam ga zaɓen shugabanni na gari masu kishin ƙasa, adilai da za su kawo haɗin kai da zama lafiya da zai sa
ƙasa ta cigaba.
MANAZARTA
Tuntuɓi mai takarda.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.