Ticker

6/recent/ticker-posts

Gudummawar Marubuta Waƙoƙin Hausa Na Siyasa Wajen Ilmantar Da Al’umma Ga Samar Da Kyakkyawan Mulkin Dimokuraɗiyya A Nijeriya

 Wannan takarda mai taken “GUDUNMAWAR RUBUTUN WAƘOƘIN SIYASA WAJEN SAMAR DA KYAKKYAWAR DIMOKURAƊIYYA A NIJERIYA”, ta zama ruwan dare wajen kawo hanyoyi masu gamsarwa a kan yadda rubutattun waƙoƙin hausa na siyasa ke kawoo canji da ci gaban dimokuraɗiyya. A takardar an kawo tarihin samuwar rubutattun waƙoƙi a takaice da ma’anar waƙa da rabe-rabenta, sannan an kawo taƙaitaccen tarihin samuwar jama’iyyu tare da fito da misalai na baitoci daban-daban daga cikin rubutattun waƙoƙin hausa mabambanta dake ganin zasu zama gudunmawa wajen samar da kyakkyawar dimokuraɗiyya, da ga ƙarshe kuma a kawo jawabin kammalawa.

Gudummawar Marubuta Waƙoƙin Hausa Na Siyasa Wajen Ilmantar Da Al’umma Ga Samar Da Kyakkyawan Mulkin Dimokuraɗiyya A Nijeriya

 

ALIYU RABI’U ƊANGULBI

GSM NO. 07032567689

E-mail: aliyurabiu83@gmail.cim

GABATARWA

            Haƙiƙa waƙa tana da mutuƙar mahimmancii da amfani wajen ci gaba da bunƙasar siyasa, kuma a ba ce mai koyar da darasi da kuma sa a kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaban ƙasa.

            Annabi Muhammad (SAW) ya ce: “A cikin waƙa akwaii hikima”, sannan kuma ya sake cewa “hikima adon mumini”.

            Wannan takarda za ta kawo irin salo da dabaru da marubuta waƙoƙin siyasa suke amfani da su wajen cimma nasarar samar da kyakyawar dimokuraɗiyya taer da kawo hiɗin kai da ƙaunar juna a tsakanin al’umma.

            Takardar ta kawo tarihin samuwa rubutattun waƙoƙi a ƙasar Hausa a taƙaice, sannan kuma ta dubi ra’ayoyin masana dangane da ma’anar waƙa da rabe-rabenta da ma’anar dimokuraɗiyya tare da kawo takaitaccen tarihin jam’iyyu. Haka kuma takardar ta fito da wasu misalai na waɗannan waƙoƙin domin nuna tabbacin marubutan sun taka gagarumar rawa wajen sa jama’a da su shiga siyasa.

 

TARIHI SAMUWAR RUBUTATTUN WAƘOƘI A ƘASAR HAUSA A TAƘAICE.

Yahaya (2002:8) ya bayyana cewa, kafin musulunci ya iso ƙasar Hausa sai da ya fara biyowa ta wasu sassa na ƙasashen Afrika ta yamma tukunna, kamar Senegal da Mali a wajen ƙarni na 11. Sai dai ya kawo ra’ayin wasu malamai irin su limamin Bauchi Ahmad Muhammad da Alhaji Nasiru Kabaro Kano, inda suka nuna cewa musulunci ya iso Afrika ta yamma, musamman Agadas da Barno tun a ƙarni na 7, zamanin Sayyadina Mu’awiya Ɗan Safiyanu.

            To, ko ma dai yaya tarihin yake, an tabbatar da cewa addinin Musulunci ya sami ƙarfafuwa a ƙarni na 15, lokacin da Shehu Musa Jakollo da tawagarsa suka shigo ƙasar Hausa da littattafan addini a kan Fiƙihu da Shari’a da Lugga  a zamanin Sarkin Kano Yakubu (1452-1463) (Yahaa 2002:10), bayan nan kuma zuwan wasu ƙungiyoyi na wangarawa a ƙarƙashin jagorancin Abdurrahman Zagaiti (1463-1499) da almaghili (1484) sun taimaka wajen bunƙasa addinin musulunci da littattafan addinin waɗanda yawancinsu aka wallafa su a waƙe.

            Har’ila yau ayyukan Wali Ɗan Marina a ƙarni na 17 da Wali Ɗan Masani ya tabbatar da samuwar rubutattun waƙoƙi a ƙasar Hausa (Auta: 2007:108).

            A ƙarni na 18, an ci gaba da samun Malamai masu yin wallafe-wallafe a waƙe. An samu ayyukan Muhammad Al-Katsinawi da Muhammad na Birnin Gwari da Malam Shitu ɗan Abdurra’uf wadda ya rubuta waƙoƙi masu yawa. Daga ciki akwai waƙar Tuba da Wawiya (Sarɓi 2007:2).

            A ƙarni na 19, an sami ingantaccen tsarin rubuta waƙaƙi da kuma haɓakarsu. A wannan ƙarni ne aka sami zuwan Shehu Usman Danfodiyo (1804) wanda ya ƙaddamar da jihadi Sakamakon taɓarɓarewa da kuma gurɓacewar ɗabi’un musulmai a wancan lokaci. Shehu Usman da tawagarsa sun ƙaddamar da yake-yake domin kyautata tarbiyar musulmai da ta gurɓata da camfe-camfen waƙoƙin a kan ɓangarorin addini daban-daban kamar wa’azi da tauhidi da yabon Ubangiji da sauransu (Sarɓi: 2007:3).

            A ƙarni na 20 kuwa, an sami ci gaba da wayewar kai na zamani. An sami hanyar rubutun ajami wadda aka yi amfani da ita a ƙarni na 19, da kuma hanyar rubutun boko. A wannan ƙarni an sami bunƙasar rubuce-rubucen waƙoƙi da dalilan rubuta su suka sami bunƙasa. Bayan jigon addini sai aka rubuta waƙoƙi a kan soyayya da siyasar jam’iyyu da talla da yabo baduniye da gasa da sauransu.

 

BAYANIN WASU MUHIMMAN KALMOMI

Ma’anar Waƙa da Rabe-Rabenta.

Masana sun karkasa waƙoƙin Hausa zuwa gida biyu kamar haka:

i.                    Waƙar baka: Ita ce wadda ake rerata da ka, kuma ake adana ta da ka.

ii.                  Rubutcciyar waƙa: Waƙa ce da ake rubutata bisa wani tsari na musmaman, sanan a rereta.

Yahaya (1997) ya bayyana ma’anar waƙa da cewa “Waƙa maganar hikima ce da ake rerawa ba faɗa kurum ba wadda ke da wani sako da ke kunshe cikin wasu kalmomi zaɓaɓɓu, tsararru kuma zaunannu”

            Mukhtar (2005) ya ce “Rubutacciyar waƙa wata hanya ce ta gabatar da wani saƙo a cikin ƙayyadaddun kalmomi da aka zaɓa waɗanda ake rerawa a kan kari da ƙafiya a cikin baitoci”.

Sa’id (2002) ya bayyana cewa “Waƙar baka ita ce wadda ake rerawa don jin daɗi, a ajiye ta a ka a kuma yaɗa ta da baka. Rubutacciyar waƙa kuma ita ce wadda aka tsara aka rubuta ta a takarda don karantawa”.

Dangambo (2007) ya na cewa “Waƙa wani saƙo ne da aka gina shi kan tsararryar ƙa’ida ta baiti, ɗango, rerawa, kari (bahari), amsa-amo (ƙafiya), da sauran ƙa’idoji da suka shafi daidaita kalmomi, zaɓensu da amfani da su cikin sigogi da ba lallai ne hakan su ke a maganar baka ba”.

Sarɓi (2007) ya ce “rubutacciyar waƙa hanya ce ta isarwa ko gabatar da wani saƙo cikin ƙayyadaddun kuma daidaitattun kalmomi da akan rubuta kuma a rera lokacin buƙata”.

 

MA’ANAR DIMOKURAƊIYYA

Skinner (1965) ya bayyana ma’anar dimokuraɗiyya inda ya ce “Dimokuraɗiyya hanyar mulkin ƙasa wadda kowa ke da hannu a cikinta”.

            Ƙamusun Hausa (2006:104) ya bayyan dimokuraɗiyya da cewa “tafarkin mulkin da mutanen ƙasa ke zaɓar shugabanninsu ta hanyar jefa ƙuri’a”.

            Siyasa wani tsari ne na tafiyar da mulkin jama’a ta yadda ake ba su damar faɗar ra’ayoyinsu da zaɓen mutanen da zasu wakilcesu, Hassan (2005).

            Kamusun Hausa (2006: 397) ya bayyana siyasa da cewar “tafiyar da al’amuran jama’a ta hanyar neman ra’ayoyinsu da shawarwari da su”.

 

TAKAITACCEN TARIHIN SAMUWAR JAM’IYYU

Kafin shigowar ilimin boko Hausawa ba su da tsarin mulkin siyasa, sai dai tsarin tafiyar da mulki na addini, domin kafin Turawa su zo Hausawa suna da tsarin mulkinsu na addini kuma suna tafiyar da mulkinsu kan hakan.

            Akwai wani littafi na tsarin gudanar da mulki na Al’magili mai suna Taj al-ɗin Fima Yajibu Ala  Al-muluk a cikin wannan littafi ya yi bayani yadda tsarin mulkin musulunci yake.

            Ilimin boko ya zo ƙasar hausa a (1909) inda a wannan shekara ya yan musulmai suka fara koyar ilimin boko a makarantar Ɗan Hausa ta farko a Arewa, Yahaya (2002).

            Bayan an sami ilimin boko aka sami yan boko, tafiya tai tafiya aka sami ‘yan boko suka fara kafa ƙungiyoyin tattaunawa irinsu Dandalin Tattaunawa (disscussion circle) a Bauchi, sai kuma ƙungiyoyin Al’adun Gargajiya (Cultural Association) as Sakkwato, saii kuma ƙungiyar Taron Masu Zumunta a Kano, sai ƙungiyar Jam’iyyar Mutanen Arewa a Zariya, Shafa’u (2010:5).

            Daga ranar 25 – 27 ga watan Dicamba a (1949) a kai gagarumin taron wannan ƙungiya a cikin birnin Kano da niyyar ta koma jam’iyyar siyasa. A (1950) kuma sai Turawa suka ƙi amincewa da ta zama jam’iyyar siyasa ta zauna a yadda ta ke sai ta zauna a haka.

            Jam’iyyun siyasa sun fara samuwa a shekara ta  (1950) wasu mtuane su takwas ne suka kafa jam’iyyar ‘NEPU’ a ƙarƙashin jagorancin Malam Abba mai Ƙwaru (Shafa’u 2010:6)

 

Jam’iyyar NEPU ta tsara manufofinta kamar haka:

1.                  Rushe zalunci

2.                  Tabbatar da gaskuya

3.                  Neman a bawa jama’ar ƙasa abubuwan da ya wajaba su samu

Jam’iyyar NEPU ta yi taron ta na farko a El-Duniya Cinima a (1951) a Kano, a wannan taron ne aka zabi Alhaji Mudi Spikin ya zama sakataren yaɗa labaran jam’iyyar, a nan ne ya karanta waƙarsa ta zalunci masu mulki Sarakuna da Turawa.

            A ranar 01/01/1951 ne aka kafa jam’iyar N.P.C a cikin garin zariya a ƙarƙashin jagorancin muƙaddashinta Alhaji Sanda, sannan kuma sai aka samii manyan ‘yan boko guda biyu suka shiga cikinta, daga cikinsu akwai alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa da Amadu Raɓe (Sardaunan Sakkwato). Shahararren mawaƙinnan Malam Sa’adu Zungur shi ne ya faɗawa jam’iyyar NPC suna. (Baban Zara 2006).

            Jam’iyyar NPC wacce aka kafa ta da goyon bayan Turawa da sarakuna ita ma ta na ta da manufofi kamar haka:

1.                  Girmama sarakuna da sarauta

2.                  Jingine siyasa da addini

3.                  Duk ‘yan NEPU jahilai ne

Bayan da Nigeriya ta sami ‘yan cin kai a (1960) jam’iyar NPC ita ce ta kafa gwamnati a Arewa da tarayyar Najeriya, inda sir Abubakar Tafawa Ɓalewa ya zama shugaban ƙasa na farko a mulkin farar hula, inda Sir, Ahmad Bello ya zama firimiyan Jihar Arewa (B. Hassan, 2006).

 

JAMHURIYYA TA BIYU

A Jamhuriyya ta biyu (1979- 1983) akwai jam’iyyun siyasa da suka taka rawar gano. Hukumar zaɓe ta wancen lokacin mai suna (FEDECO) ta yiwa ƙungiyoyin siyasa guda biyar rigista akwai N.P.U, U.P.N, N.P.P, G.N.P.P. (Nigeria at 50).

 

Jam’iyyar N.P.N ita ce ta kafa gwamnatin tarayya da wasu johohi a ƙarƙashin jagorancin Chief M.a Akinloye, sai jam’iyar P.R.P ta kafa gwamnati a Kano da Kaduna a ƙarƙashin jagorancin Malam Aminu Kano, har ila yau jam’iyyar PRP itace ce jam’iyyar hamayya a Arewa a tarayya kuma UPN kuma gyaran jam’iyar NEPU ce, ita kuma UPN gyaran jam’iyyar AD ce, sannan jam’iyyar NPP, gyauran jam’iyyar NCNC ce.

            Da yawa daga cikin mawaƙa da Allah ya raya na Jam’yyar NEPU da NPC sun canja shekara sun dawo yiwa sababbin jam’iyyu waƙoƙi.

            Daga cikin Mawaƙan PRP da suka yi fice akwai Alhaji Aƙilu Aliyu, sai Abubakar Ladan Zariya, sai Malam Auwalu Isa Bunguɗu, sai Malam Shehu Taura, kowanne ɗaya daga cikin waɗannan mawaƙa yayi waƙoƙi masu daɗi da tarin hikima kuma sun bayyana manufofin jam’iyyar da alamominta, sannan kuma sun kaɗa shugabancin jam’iyyar da nuna cewa duk waɗanda suka tsaya takarr shugabanci da Malam Aminu Kano shi ne ya fisu cancanta ya zama shugaba fiye da kowa. (B. Hassan 2006).

 

GUDUNMAWAR WAƘOƘIN SIYASA WAJEN SAMAR DA KYAKKYAWAR DEMOKURAƊIYYA A NIJERIYA.

Wannan takarda zata kalli irin gudumawar da marubuta waƙoƙin siyasa ke bayarwa don kawo ingantacciyar siyasa a ƙasa, saboda marubuta waƙoƙin siyasa Malamai ne masu hazaƙa da zalaka da fahimta. Su kan rubuta waƙoƙinsu don ilimantar da al’umma ta yadda za su fahimci irin sakon da suke buƙata su sanar da jama’a domin samun amfanuwa.

            Haka kuma marubuta waƙoƙin siyasa su na taka muhimmiyar rawa wajen amfani da ɓangarori daban-daban ta inda suke ƙoƙari a cikin waƙoƙin su cusawa al’umma manufofin jam’iyyu ko kuma su nuna wa al’umma mahimmancin shiga wannan jam’iyyar, sannan kuma su kan cusa adawa ga sauran jam’iyyum haka nan kuma su kan nasihantar da al’umma a kan jan hankalin mutane cikin lumana don nuna musu abubuwan daya kamata su aikata da wannan bai kamata su aikata ba.

1.         Nasiha

            Misali: Alhaji Mudi Spikin a waƙarsa mai suna nasiha ga ‘yan siyasa yana cewa:

                        ‘Yan siyasar gari – gari

            Duk ku zo kan batun shiri

            Cikin nasiha da hanƙuri

            Inda dai babu tunzuri

                        Sai batun masu gaskiya

Wannan baiti ya na fito da lallai ‘yan siyasa su riƙa yin sulhu da juna (saboda bambancin siyasa) domin kar ya kawo rarrabuwar kai da gaba.

            Daga nan kuma, sai ya ƙara yin wata nasihar da cewa, Allah ya umarci musulmi su zama tsintsiya maɗaurinki daya duk da cewa kowa da ra’ayinsa, amma wannan ba zai hana kawo zaman lafiya ba. Ga abinda ya ce kamar haka:-

                        Mai ya sa za a ƙin shiri

            ‘yan gari ko da ‘yan gari

            Duk cikin babu ja’iri

            Kuma ga faɗar Rabbi Ƙadiri

                        Muminai duk su zam ɗaya

Haka nan kuma, a cikin waƙarsa ta nisiha za a fahimci cewa nasiha yake yiwa ‘yan siyasa da su zauna da juna lafiya tare da bayyana gaskiya a dukkanin al’amurransu. Inda yake cewa:

                        ‘yan uwa kunga duniya

            Duk ciki sai hatsaniya

            An ƙi yarda da gaskiya

            Ana ta faman hatsaniya

                        An ƙi gane wa gaskiya

 

Shi kuwa Auwalu Isa Bunguɗu a waƙarsa ta ‘yan santsi yana cewa:

                        Domin waƙar nisiha ce

            Kuma ka riƙe nafsi ce

            Ta zame hujja cikin zance

            Ka tunawa wanda ya mance

                        In bai yi riƙon nasiha ba 

 

                        Shaiɗan ma bai biyayya ba

            To amma bai ci riba ba

            Bai sha daɗin butulci ba

            Fahrijminha ka dudduba

                        Ayar ba za ta shafe ba

A waɗannan baituka Malam Auwalu Isa Bungudu yana nasiha da kada ayi butulci, domin ya ƙarfafa batun har ayar Al-Ƙur’ani ya kawo da nuna ƙarshen mai yin butulci.

 

KAMMALAWA

A wannan takarda, anyi ƙoƙarin bayyana irin gudunmawar da rubutattun waƙoƙin siyasa suke bayarwa don kawo chigaban dimokuraɗiyya a Nijeriya. Takardar ta fito da ɓangarori da ake ganin marubuta waƙoƙin siyasa suna amfani da su wajen cimma manufofin ga al’umma.

            A takaice, takardar ta gano hanyoyi da marubuta waƙoƙin siyasa suke bi don yaɗa manufar jam’iyyarsu, ko ta hanyar nuna adawa, ko kuma ta hanyar yin nasiha ga al’umma. Sannan kuma takardar ta fito da misalai na wasu baitoci daga rubutattun waƙoƙin siyasa mabambanta domin tabbatar da cigaban dimokuraɗiyya a ƙasar Nijeriya. Saboda Marubuta waƙoƙi Malamai ne masu fasaha da hikima da hankali da tunani sukan ƙulla magana kamar yadda masu sana’ar goro suke ɗaure shi domin siyarwa.

MANAZARTA

Tuntuɓi mai takarda.

Post a Comment

0 Comments