Al’ummomi daban-daban kamar Romawa da Girkawa da Misirawa kan tatso mai daga ‘ya’yan zogale wanda sukan sarrafa shi wajen aiwatar da turare da man shafawa. A cikin ƙarni na goma sha tara (19), gandayen zogale da ke Yammacin Indiya sun fitar da man zogale zuwa ƙasar Turai domin yin turare da giris don amfanin na’urori.
Gudummawar Zogale
Cikin Sha’anin Magunguna a Ƙasar Hausa
Dr.
Adamu rabi’u bakura
08064893336
Shimfiɗa
Ma’anonin Tubalan
Ginin Take
Kalma ce Bahaushiya da ke cikin
jerin sunayen jinsin mata. Ana faɗar ta da lafazin gudunmawa a Karin
harshen Sakkwatanci da na Kananci da kuma zazzaganci, kamar yadda Bargery
(1993:402) ya nuna. Shi kuwa Abraham (1975:337) ya nuna cewa, a Karin harshen Sakkwatanci ne ake
faɗar ta da lafazin gudunmowa
wato akan saka wasalin /o/ a gaɓa ta uku maimakon wasalin /u/da wasu
Karin harsuna ke amfani da shi. Har ila yau Ƙamusun Hausa na
Jami’ar Bayero (2006:171) ya nuna ana furta gaɓa ta uku da wasalin /a/ ko /o/,
misali gu-dum-ma-wa. Kalmar gudummawa tana ɗauke da ma’anar taimako na aiki ko kuɗI ko abinci ko sutura
ko wani abu. Kuma daidai take da agaji ko ceto daga wahala kamar yadda Garba
(1990:4) ya bayyana.
ZOGALE:-
Wata itaciya ce da ake shukawa ko
dasawa a gida ko gona, wadda ake tsigar ganyenta ana dafawa a kwaɗanta a ci ko a yi
dambu ko fate ko a yi miya da shi. Haka kuma akan yi danga da itaciyarta. Tana
da furanni farare.Ana kuma yin yaji da saiwarta (Garba, 1990:167).Ita zogale
matsakaiciyar itaciya ce, wadda girmanta ya kama daga tsawon mita biyar (5)
zuwa mita goma (10). Saboda yawan amfanin da ake da ita ya wanzar da nomanta a
duk kusan sassan duniya. Ana samun ta a yammacin duniya da ƙasashen Asiya
musamman a yankunan tsaunukan Himalaya
da ƙasashen
Indiya da Pakistan da Afirika da kuma ƙasashen Larabawa.
Al’ummomi daban-daban kamar Romawa
da Girkawa da Misirawa kan tatso mai daga ‘ya’yan zogale wanda sukan sarrafa
shi wajen aiwatar da turare da man shafawa. A cikin ƙarni na goma sha tara
(19), gandayen zogale da ke Yammacin Indiya sun fitar da man zogale zuwa ƙasar Turai domin yin
turare da giris don amfanin na’urori.
Al’ummomin ɓangaren ƙasar Indiya sun daɗe suna amfani da
kwasfan zogale wajen abinci. Shi kuwa ganyen zogale ya kasance wani muhimmin
abu da ake ci a duk farfajiyar ƙasashen Afirika ta Yamma da wasu
sassan Asiya.Abin ƙayatarwa ne ƙwarai dangane da
jerin nau’o’in magungunan da ake yi da zogale waɗanda ke ƙunshe da muhimman
sinadaran gina jikin ɗan-Adam. Sakamakon
amfanin da ake yawan yi da ita ne ya sa aka gano tana maganin cuwurwuta da
dama. Wannan ne ya haifar da mayar da hankali wajen binciken irin cutar da take
magani.
Zogale A Farfajiyar Ƙasar Hausa
A farfajiyar ƙasar Hausa akan kira
ta da sunaye dabam-daban. Wasu yankunan na kiran ta zogalagandi ko
zogale ko kuma tamakka. A wani yanki na ƙasar Zamfara kuwa,
kamar Bunguɗu da Maru suna yi
mata laƙabi da ɗanhaki. Yayin da ake kiran ta dakable a yammacin ƙasar Gummi. A ƙasar Ruwan Ɗoruwa da kewayenta
ana kiran ta ‘yarmakka. A yankin ƙasar Nijar kuwa akan
kira ta da sunan bagaruwar makka.
Ana kyautata zaton wannan itaciyar
ta zo ƙasar Hausa ne ta hannun mahajjata, kamar yadda sunayen da
aka yi mata a ƙasar Hausa da ƙasar Nijar suka yi
ishara. A wani hasashen kuwa, zogale ta zo ƙasar Hausa ne daga
Misira. Tarihi ya nuna, ƙasar Masar na daga cikin ƙas- ashen da aka fara
kai zogale daga Indiya. Misirawa sun daɗe ƙwarai suna amfani da
zogale wajen magungunansu na gargajiya, musammam ma mai da ake samu daga
‘ya’yan zogale wanda aka ce Misirawa na shafa shi a fatar jiki don kariya daga
illar da iskar Hamada ke yi wa fatar jiki.
A ra’ayin Hambali Junju, Hausa ta
samo asali ne daga Misira. To idan muka ɗauki wannan ra’ayin za a iya cewa, ke nan
koda Hausawa suka zo ƙasar Hausa, sun zo ne tare da abarsu. Ai ko banza masara
ma daga Misira ta zo ƙasar Hausa. Saboda haka ba abin mamaki ba ne idan aka ce
zogale daga can ta zo. Sai dai ba wani mahaluƙi da zai fito fili ya
ce ga ƙayyadadden lokacin da ta zo ƙasar Hausa da kuma
wanda ya fara shigowa da ita, sanin wannan sai Allah.
Asalin Zogale:
Masana da dama kamar (Nickon &
others 2003) da (Ndong, 2007) da (Agrawal da wasu, 2008) da (Busani da wasu,
2012) sun nuna cewa, zogale tun can asalatan itaciyar ƙasar Kudancin Indiya
ce, wato ƙasar Sirilanka. In
kuwa haka ne, za mu iya cewa, Allah cikin ikonSa da hikimarSa da iradarSa, Ya
samar da zogale a can ne domin Annabi
Adamu da zuriyarsa na farko su sami abin yin riga-kafi da maganin cututtuka da
ita. Musamman idan aka yi la’akari da irin sinadiran ban mamaki da ta’ajibi waɗanda Allah Ya halicce
ta da su, da ke da muhimmanci a cikin jikin ɗan-Adam, ta fuskar waraka da garkuwa daga
wasu nau’o’in cuwurwuta da kan addabi jiki. Masana tarihi sun nuna an saukar da
Annabi Adamu (A.S.) a farfajiyar ƙasa da ke yankin
Sirilanka, yayin da Matarsa Hauwa’u aka saukar da ita a Jidda. In kuwa haka
lamarin yake, za mu iya cewa, zogale na ɗaya daga cikin itatuwan Aljanna. Musammam
idan muka yi la’akari da irin ɗinbin sinadiran da take kunshe da su, da kuma yadda take
maganin cututtuka fiye da ɗari uku (300) tun ƙarnukan da suka shuɗe kamar yadda za a
gani nan gaba. Sai dai sanin gaskiyar lamarin yana wajen Allah.
Wata hujjar da ke tabbatar da
hasashen ita ce, za a tarar cewa,
itaciyar zogale ta sha bamban da sauran itatuwa ta hanyoyi da dama. Da farko
dai takan tsiro (toho) a lokacin rani da damina, muddun tana samun danshin
sanyi. Haka kuma tsananin fari da sara bai haddasa ta mutu, sai ko in har an haƙe saiwarta gaba ɗaya, ba kamar wasu
itatuwan ba. Abu na biyu da ya bambanta ta da sauran itatuwa shi ne tana rayuwa
a ƙasashe
masu tsananin zafi da matsakaita da masu danshi da ni’ima, har ma a cikin
yankunan rairayi.
Magani: Ma’anarsa Da Asalinsa
Masana da dama sun yi ƙoƙarin bayyana ma’anar
Kalmar magani gwargwadon fahimtarsu. Kano (2006: 316) sun bayyana ma’anar
magani da cewa:
Magani, yana nufin
duk wani abu da ake sha ko shafawa ko
Kuma ɗurawa a jiki ta
hanyar yin allura, don neman samun
Lafiya ko kariya daga
wata cuta.
Shi kuwa Ahmad (1984)
ya bayar da ma’anar magani da cewa:
Magani shi ne duk
wani abu da za a yi, ko wata hanya ko
kuma wata dabara da
aka yi don gusar da cuta daga jikin
mutum ɗungurumgun ko kuma
kwantar da ita don kawo
jin daɗI ga jiki ko ga
zuciya da sauƙaƙa duk wata wahala
ga jiki da damuwa da
ita cutar kan iya haifarwa.
Bakandamiyar ma’ana
ta magani ita ce wadda Bunza (1989:134) ya bayyana inda yake cewa:
Magani wata hanya ce
ta warkar da ko kwantar da ko rage wata
Cuta ta ciki ko ta
waje ko wadda aka samu ta haɗari. Ko kuma
Neman kariya daga
cuta ko abokan hamayya ko neman ɗaukaka
Ta daraja ko ta
buwaya ta hanyar siddabaru da sihirce-sihirce na
ban al’ajabi.
Asalin Magani
Magani ya samu ne tun bayan da Allah
Maɗaukakin Sarki Ya
halicci Annabi Adamu (A. S.) sai ya
sanar da shi dangogin ilmomi masu yawan gaske cikin yardarSa ( Alƙur’ani, 2: 31). Daga
cikin ilmomin kuwa har da ilimin cututtuka da yadda za a magance su. Haka ya
halitta wasu tsirrai a doron ƙasa domin amfanin Annabi Adam da
zuriyarsa. Aka kuma fahimtar da su hanyoyin sarrafa su a matsayin maganin yunwa
da na cututtuka.
Yayin da zamani ya shuɗe, mutane suka ƙara yaɗuwa zuwa sassa
daban-daban, sai Allah cikin jinƙanSa da rahamarSa Ya
jefa wa ɗan Adam, a ransa, in
aka yi amfani da abu-kaza zai yi maganin ciwo kaza da kaza.
Wasu lokuttan kuma a mafarki za a
gayawa ɗan-Adam, ya yi amfani da wani abu don
maganin wata cuta. Wani zubin kuwa, murya kawai mutun zai ji kamar daga sama,
ana umurtarsa, ya yi amfani da abu kaza domin magance cuta kaza.
Akan kuma sami magani ta hanyar
gwaji da kwatantawa, musamman ta la’akari da yadda dabbobi da tsuntsaye ke
amfani da’ya’yan itatuwa da hakukuwa da ganyaye yayin da suke cikin yanayin
rashin lafiya, da yadda suke nuna halin ko’inkula da su a lokacin da suke cikin
ƙoshin
lafiya ( Adamu, 2003:10).
Yaɗuwar al’umma da nuna kyakkyawar
biyayya, ya wanzar da ɗorewar mallakar
asirran magani daga hannun masana magunguna na haƙiƙa. Kyakkyawar biyayya
ta sau- da ƙafa kan sa a sanar da waɗansu daga cikin zuriya ko waɗanda suka yi barance,
asirran magungunan da Allah Ya sanar da su. Ta waɗannan hanyoyi ne aka cigaba da gadon
asirran magungunan gargajiya a ƙasar Hausa. Kuma ta irin wannan hanya
ce ilimin sirrin magungunan da zogale ya bi ya cigaba da bunƙasa.
Rabe- Raben Magani a Bahaushiyar Al’ada
Kamar yadda aka faɗa a bay akaɗan, magani abu nemai
daɗaɗɗen tarihi wanda
al’ummomi daban-daban na duniya ke bin hanyoyi mabanbanta domin samar da shi da
kuma amfani da shi. Nau’uka ko ire-ire ko rabe-raben magani abu ne da ya ja hankalin
masana al’adun Hausawa, kuma sun yi tsokaci a kan wannan batu. Sarkin Gulbi
(2014:86) ya kawo rabe-raben magani kamar haka:
i.
magungunan
riga-kafi.
ii.
Magungunan waraka.
iii.
Magungunan cutarwa
iv.
Magungunan biyan buƙata
v.
Magungunan camfi
Zogale A Fagen Magani
Zogale, nau’in itaciya ce wadda Allah Ya tsirar a bisa doron ƙasa domin amfanin
mutane da dabbobi da Aljannu. Ita kanta ƙasa ma tana amfana da
ita. Wani abin mamaki da ta’ajibi shi ne, irin yadda halittun da ke ruwa suke
amfani da saiwar zogale da ke kusa da gulbi ko ƙorama.
,‘Yanmagori da bokaye
da sauran wasu daga cikin masu sana’o’in gargajiya kamar wanzamai da masunta da
makamantan su, duk suna amfani da zogale a gargajiyance domin yin magunguna
nau’i-nau’i a farfajiyar ƙasar Hausa da ma wasu sassan Nijeriya.
Rabe-Raben Magungunan
Zogale
Ana iya karkasa magungunan da zogale
ke aiwatarwa ta la’akari da yadda al’umma ke sarrafa ta wajen biyan buƙatunsu waɗanda suka danganci
rayuwar yau da kullum. Daga cikin irin waɗannan buƙatun akwai:
1. Waraka.
2. Kariya Da Buƙatar zuci.
3. Biyan Buƙatun zuci.
Zogale A Fagen
Maganin Waraka
Zogale na taka muhimmiyar rawa waje
kawar da dangogin cuwurwuta da ke addabar jikin ɗan Adam. Irin waɗannan cututtuka nau’i
biyu ne. wadda ake iya gani da wadda ba za a iya gani ba, sai dai kawai maras
lafiya ya ji wasu alamomi tare da sauyawar yanayin jikinsa. Daga cikin
cututtukan da zogale kan yi maganinsu akwai:
Ƙaiƙayin Ido
A fagen magance ƙaiƙayin ido, sai a nemo
ganyen zogale ɗanye, a murtsuke shi,
a sami auduga (kaɗa/ tauhwa) ko wani
farin ƙyalle mai tsabta. A tsoma cikin ruwan ganyen, a tatsa
(matsa) ɗigo uku (3) a idon
har sau uku a rana (jinju,1990:19). Shaihin Malamin ya tabbatar da ingancin
maganin ta hanyar gwaji shi da kansa.
Ƙaiƙayin Jiki
Ta fuskar ƙaiƙayin jiki kuwa, sai a
samu ɗanyen ganyen zogale
cikin tafin hannu uku (3) a daka, a tarfa ruwa kimanin babban cokali huɗu (4). A tace da ƙyalle fari mai kyau.
Ruwan ne za a riƙa shafawa a wurin da ke yin ƙaiƙayin. Za a shafa
maganin ne sau uku (3) a rana har tsawon kwana bakwai (7) (Jinju, 1990:73).
Malamin ya tabbatar da ingancin maganin tare da rashin wani lahani
(aibu/cutarwa) a jikin ɗan Adam.
Ƙaiƙayin Al’aura
Akwai wata cuta da ke addabar mutane
musamman mata, inda sukan fuskanci matsalar matsanancin ƙaiƙayi a daidai farji ko
dubura. Irin waɗannan mata kan
fuskanci matsalar rashin son saduwa da maigida, a sakamakon mummunan ƙaiƙayi bayan jima’i. Sai
a sami saƙe-saƙin zogale a dafa tare da jar kanwa
‘yar kaɗan. Sai a sha kofi ɗaya (1) safe da
yamma, ta kuma riƙa yin tsalki da ruwan maganin( hira da Sahabi Kardaji,
Gummi). Haka su ma maza masu fama da ƙaiƙayin matsematsi na
iya yin amfani da wannan haɗin, don nema samun waraka
Ciwon Ido da Kunne
Yayin da mutun ke fama da lalurar
ciwo ido ko kunne, sai ya ɗebo ɗanyen ganyen zogale. Ya murza, ya matse ruwan ya dinga
(riƙa)
ɗigawa a ido ko a
kunne. Insha Allah za a samu lafiya.
Ciwon Kai
Ga mai fama da lalurar ciwon kai,
sai ya nemi ɗanyen ganyen zogale,
ya murtsuka shi ya shafa a goshinsa. Da izinin Allah zai sami waraka.
Ƙurajen jiki
Idan mutun yana fama da ƙuraje a jikinsa, sai
ya nemi garin zogale, ya haɗa da man zaitun ya shafa a jiki. Zai sami waraka insha
Allah.
Idan kuma mutun na fama da kurajen
jiki, sai ya nemi garin zogale ya haɗa da man zaitun, ya kwaɓa, sai ya riƙa shafawa a jiki. Da ikon Allah zai sami waraka.
Ciwon Haƙora
Shi kuwa wanda ke fama da matsalar
ciwon haƙori, sai ya nemo ƙaron ( jirrai/
jillan) zogale, sai ya liƙa a inda ke ciwon (Jinju, 1990:23).
Ciwon Ɗankakkarai
Ciwo ne da ke shafar yatsan hannu ko
na ƙafa.
A irin wannan yanayi yatsa kan kumbura, ta riƙa ciwo da zogi (raɗaɗi) mai tsananin
gaske, har sai wurin ya ja ruwa, wanda ke bayar da damar yin sakiya. Ana amfani
da ganyen zogale wajen maganin wannan cuta. Mai fama da wannan lalurar sai ya
samo ganyen zogale, ya mutsuka shi, sai a saka kanwa, sai ya kunsa a yatsan da
ke ciwo, kamar yadda ake kunsa (ɗaura) lalle. Da izinin Allah, cikin ‘yan
kwanaki kaɗan kumburin zai sace
ya kuma daina raɗaɗi sai wurin ya ƙafe (bushe).
Harbin Kunama
Idan kunama ta harbi mutun (Allah Ya
tsare), sai a nemo ganyen zogale, sai a murmurza tare da turare sai a saka a
daidai wurin da ta yi harbi. In Allah Ya so za ta faɗi ba tare da jinkiri
ba.
Ciwon Sanyi
Mai fama da matsalar sanyi, sai ya
nemi ganyen zogale, ya dafa tare da jar kanwa ‘yar kaɗan. A tace, ya rinƙa shan ruwan moɗa (kofi) ɗaya, sau biyu (2) a
rana ga babban mutun. Yaro kuwa ya sha rabin moɗa sau biyu a yini (Jinju,1990:66).
Haka kuma ana tafasa furen zogale
tare da albasa, a rinƙa sha kamar shayi, don magance ciwon sanyi.
Idan ciwon sanyi ya yi yawa, yakan
shafi hanyar mafitsara, sakamakon da kan haifar da wahala ainun kafin fitsari
ya fito..wani lokaci ma fitsarin kan faskara fita. Maras lafiya na jin fitsari
amma ko ya duƙa (tsugunna) domin yin fitsarin sai lamarin ya gagara. A
irin wannan yanayi, sai a nemi sayyun zogale, a wanke su sosai domin a tsabtace
su. A kuma sami ruwan tsami da aka tsiyayo daga ƙullun gero, sai a jiƙa sayyun a ciki, idan
sun jiƙa, sai maras lafiyan ya sha moɗa ɗaya (1) da izinin
Allah cikin ɗan ƙanƙanin lokaci fitsarin
zai fito ( Fadama,2014: ).
Ciwon Sanyin Mata
Akan kamu da irin wannan cutar a
sakamakon saduwa da mace. Idan namiji ya harbu da ƙwayar cutar, sai a
nemo sayyun zogale wadda bata daɗe da tsira ba. Sayyun za a kwanɗare ɓawonsu, sannan a dake
su cikin turmi tare da jar kanwa. A yi kunun dawa, sai a ɗebo garin maganin a
saka a cikin kunun. Maras lafiya zai riƙa shan kunun domin
maganin wannan cutar sanyi. (Sahabi Ƙardaji, Gummi).
Sanyin Ƙashi Da Kumburi
Mai fama da lalurar sanyin ƙashi ko kumburin
jiki, sai ya nemo ‘ya’yan zogale a soya, sannan a daka har su zama gari. Sai a
haɗa garin da man kwakwa
a rinƙa shafawa a wurin da lalurar take.
Sanyin Ƙashi
A wannan nau’in kuwa, za a sami
saiwar zogale da tafarnuwa a kirɓe su. Sai a dinga haɗawa da man tega ana
shafawa a ƙafa sau uku (3) a rana, har tsawon kwana bakwai. Za a
sami sauki da ikon Allah.
Ana kuma kwaɓa garin zogale tare
da manja, a riƙa shafawa a wurin da ake jin raɗaɗi.
Tsayar Da Zubar jini
Ta fuskar dakatar da jini daga
zubewa kuwa, zogale nan ma ba a baya take ba. Domin in mutun ya yi rauni ta
hanyar yanka ko sara ko tuntuɓe wanda har ya haifar da kwararar jini, sai a sami ganyen
zogale ɗanye, a murtsika shi,
a shafa ruwan ganyen a wurin raunin. In Allah Ya so jinin zai daina zuba.
Rauni Ko Gyambo
Wanda ya ji ciwo har fatar jikinsa ta
fashe tare da zubar jini. Ko kuma yana da
wani miki (ciwo) a ƙafa da ya daɗe bai warke ba,
lamarin ya kai yana fitar da mugunya (ruwan ƙurji mai launin
fari). Sai a nemi garin zogale a zuba a kan raunin ko gyambon. Insha Allahu zai
yi saurin warkewa.
Gyambon Ciki (olsa)
A dafa ganyen zogale da zuma a sha
kamar shayi don maganin gyambon ciki.
Ciwon Shawara
A dafa ganyen zogale tare da kanwa
‘yar kaɗan. A ci, a kuma sha
ruwan don maganin shawara.
Ciwon Sukari
A nemi furen zogale a gama da citta
mai yatsu a dafa, a rinƙa sha kamar shayi. Yin haka yana maganin cutar da ke
haddasa yawan fitsari wato Diyabitis.
Haka kuma, wanda ke fama da irin
wannan lalurar, sai ya ɗebo ganyen zogale tun
da safe kafin rana ta fito. A shanya shi a wajen da ba hasken rana har ya
bushe. In ya bushe sai a rinƙa dafa shi kamar shayi ana sha da
madara, sau biyu a rana. A kula da zuwa wajen awo.Idan ba sauran cutar sukari
sai a daina sha.
Ciwon Hanta Da Ƙoda
A nemo ganyen zogale da ‘ya’yan ɓaure, a daka su har
sai sun koma gari. Garin nan za a rinƙa sawa a nono ko
kunu, a sha sau uku a yini. Insha Allahu za a sami lafiya.
Tsakuwar Ciki
(Appendis)
A sami saiwar zogale a gama da
‘ya’yan kankana a dake su har su zama gari. Sai a rinƙa zuba garin a nono
ana sha. Insha Allah za a sami lafiya.
Tsutsar Ciki
Idan yaro na fama datsutsar ciki,
sai a sami ɗanyen ganyen zogale,
a wanke a ba mai fama da lalurar ya ci, sau biyu a rana.
Maganin Bugun Aljani
Idan Aljani ya bugi mutun har ya faɗi, sai a sami garin
zogale a shaƙa masa a hanci. Zai yi saurin sakinsa. Wani zubin ma
aljanin kan yi magana.
Kariya Da Buƙatun Zuci
Magunguna ne da akan yi amfani da su
don taimakon ɗan-Adam wajen kare
lafiyar jikinsa tare da biyan wasu buƙatunsa da suka jiɓinci jin daɗin rayuwarsa. A
wannan haujin ma zogale na taka muhimmiyar rawa. Musamman idan aka yi la’akari
da amfanin da ake yi da ita ta ɓangarori kamar:
Hawan Jini Da Ƙarin Kuzari
Sanya (saka/zuba) zogale cikin abinci ana ci, yana maganin
matsalar hawan jinni. Yana kuma ƙara wa mutun kuzari a
jikinsa.
Kare Kai Daga Cuta
Magunguna ne da ke taimakawa mutun
wajen kare lafiyar jikinsa daga cuta da ke haifar masa da wata illa a jikinsa.
Akan yi amfani da zogale domin ƙoƙari dakatar da wata
cuta daga shiga cikin jikin mutun, ko kuma hana cutar yaɗuwa. Don haka za a
iya cewa zogale na maganin da ya danganci riga-kafi tare da hana yaɗuwar cuta.
Hawan Jini (tashin
jini)
A sami albasa, a kasa ta kasha huɗu, a yanka kashi ɗaya bisa huɗu na albasar a gama da dafaffiyar zogale a
ci. A aiwatar da wannan haɗi sau uku ko huɗu a wata. Yin haka na maganin hawan jini,
kamar yadda Jinju (1990:32) ya bayyana.
Magungunan Biyan Buƙatun Zuciya
Magunguna ne da suka jiɓinci buƙatun rayuwar ɗan Adam. Ta wannan
fuskar ma ana amfani da zogale domin neman samun biyan irin waɗannan buƙatun rayuwa. Misalai
daga cikin irin waɗannan buƙatun sun haɗa da:
Ƙara Yawan Ruwan Mama
(nono)
A sami furen zogale a dafa shi tare
da zuma. Mace mai shayarwa ta rinƙa ci sau uku a yini.
Yin haka na ƙara yawan ruwan mama.
Ƙarin Nishaɗi
A sami zangarniyar zogale tare da
‘ya’yan da ke ciki, a haɗa da kanunfari da
citta da masoro da kimba a dake su, har sai sun koma gari. Sai a riƙa sawa a cikin abinci
ana ci. Yin irin wannan haɗin na ƙara wa mata ni’ima da nishaɗi.
Haka kuma mata ma’aurata na iya
samun garin ganyen zogale a riƙa haɗa shi da madara ko nono ana sha domin ƙarin ni’imar
kwanciyar aure da maigida. Amfani da wannan haɗin na ƙara sa mace ta
ni’imtu, kwanciyar aure da maigida ta yi
armashi sosai har kuma a kwaɗaitu da sake maimaitawa.
MANAZARTA
Tuntuɓi mai takarda
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.