Aure
al’ada ce wadda ta daɗe
a duniya baki ɗaya. Hasali ma tushen
aure ya samo asali ne tun lokacin da Allah (S W A) cikin ikonsa ya halacci
mutum na farko a doron ƙasa,
watau Annabi Adamu (A S). Sannan cikin ƙaddarawarsa
ya halicci Hauwa’u domin ta zama matarsa. A wannan maƙala
za a yi ƙoƙarin
nazarin kwatance ne na wasu daga cikin al’adun neman auren Hausawa da na
Dakarkari. Don haka, maƙalar
ta yi tsokaci ne a kan tsarin neman auren Hausawa da na Dakarkari
musamman abin da ya shafi wasu keɓaɓtattun al’adu kamar: soyayya a tsakanin saurayi da budurwa
da zance ko taɗi
da matsayin ɗanrakiya da matsayin
iyaye da al’adar na-gani-ina-so da dai sauransu. Da yake muƙalar
ta shafi al’adun al’umma biyu ne, don haka, an yi ƙoƙarin
kawo bambanci da kamancin tsarin yadda ake aiwatar da
waɗannan al’adu. A ƙarshe
maƙalar ta yi ƙoƙarin
bayanin wasu hikimomi ko falsafar da ke tattare a cikin wannan rumbu na al’adun
neman auren Hausawa da na Dakarkari.
Gwagwarmayar Kamancen Neman Auren Hausawa Da Na Dakarkari
Rabiu Aliyu Rambo
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sokoto.
Email: Rabiualiyurambo@yahoo.com
GSM:08125507991
1.0
GABATARWA
Neman aure a al’adar al’umar Hausawa
da na Dakarkari abu ne da ke tattare da kai-komo na iyaye da saurayi da budurwa
. Wannan kila shi ya sa Hausawa ke masa kirari da cewa: Aure marmari daga nesa,
ko Aure wane yaro, ko Ba neman aure ke da wuya ba shiga da fita. Wannan ya nuna
muna cewa akwai gwagwarmayar da mai neman aure zai yi ta cin karo da su a
lokacin neman aurensa. Don haka, mallakar mace ga al’umar Hausawa da na
Dakarkari ba ƙaramin aiki ba ne, sai namijin gaske . Duk da yake, kafin zuwan
addini, Hausawa na da wasu hanyoyi na mallakar mace kamar : Neman aure da yaƙi
da samame da hari da cire da tsituwa da bashi da saye da kyauta da kwartanci.
Al’umar Hausawa da na Dakarkari al’uma ce da ke
da daɗaɗɗiyar dangantaka da cuɗanya a tsakaninsu mai daɗaɗɗen tarihi. Don haka,
wannan maƙala za ta yi ƙoƙarin nazarin wasu daga cikin al’adun neman auren
Hausawa ne da na Dakarkari . Da yake al’adun aure yawa ne da su, don haka,
wannan maƙalar ta taƙaita ne ga irin gwagwarmayar da ake yi a wurin aiwatar da
wasu daga cikin al’adun neman auren waɗannan al’umma guda biyu (Hausawa da
Dakarkari).
A ƙoƙarin nazarin waɗannan al’adu ,wannan maƙalar
ta yi nazarin yadda ake aiwatar da kowace al’ada daga al’ummomin Hausawa da na
Dakarkari. Bayan wannan, maƙalar za ta yi ƙoƙarin kawo irin kamance-kamance da
kuma bambance-bambancen da ake samu a lokacin aiwatar da waɗannan al’adu a
tsakanin waɗannan ƙabilu biyu. Haka kuma , yana daga cikin manufar wannan maƙala
ita ce, zaƙulo wasu hikimomi ko falsafofin da ke tattare da aiwatar da waɗannan
al’adu a tsakanin ƙabilun Hausawa da na Dakarkari
Daga cikin al’adun neman auren da za a yi nazari
a wannan maƙala sun haɗa da: soyayya da zance ko taɗi da matsayin iyaye da isa
gida da gaisuwar abokai da al’adar na-gani-ina-so da sauransu.
2.0 Ma’anar Aure:
A gaskiya zai yi wuya kai tsaye a ce ga ma’anar
aure guda ɗaya karɓaɓɓe kuma gamsasshe ga al.uma baki ɗaya.Wannan kuwa ba zai
rasa nasaba da ganin cewa kowace al’umma tana da yadda ta ɗauki aure ba .Bisa
ga wannan ne masana ilimin zamantakewa da ɗaliban al’adun al’umma musammam na
Hausawa da na Dakarkari suka kawo ra’ayoyinsu dangane da ma’anar aure .Misali
Habibu Alhassan da wasu (1980) sun haɗa hannu suka bada ma’anar aure kamar
haka:
Aure alaƙa ce ta halaccin zaman tare
tsaƙanin namiji da mace. Ana yin sa ne saboda
abin da aka haifa ya sami asali da mutunci da
kiwon iyaye. Kuma shi ne maganin zina da ‘ya’ya
marasa iyaye.
Wannan ma’anar ta nuna aure zamantakewa ce a
tsakanin namiji da mace tare da amincewar juna .Amma ita kuwa Fatihiya Migdad
Sa’ad (1998:196) tana da ra’ayin aure a musulunci kamar haka:
Aure shi ne halaccin zaman namiji da mace
tare da cika wasu dokoki , tare da ba kowa
nasa
hakkin zamantakewa a tsakaninsu. Wannan
yarjejeniyar ta zama tare kuma za a yi ta bisa
koyarwar addinin musulunci wanda ake samu
a cikin al’kur’ani da hadisan manzon Allah(SAW)
Haka ma M A Rauf (1970:78) ya bayyana cewa; bisa
ga shari’ar musulunci aure shi ne :
Ƙulla wata yarjejeniya da za ta haifar da
halalcin saduwa da mace dasamun zuri’a.
Kuma wani bangare ne na mu’amula da ibada.
Harwayau, wasu masana zamantakewar al’umma (sociologist)
sun kalli aure ta wannan fuska. Misali: Burgess da Locke (1953) sun bayyana
aure da cewa:
“
Zamantakewa ce ta amincewar mutum ɗaya ko fiye da ɗaya ko mace ɗaya ko fiye da ɗaya mai dangantakar mata da miji”.
Anan muna ganin cewa, ga tasu fahinta ba
dole bane aure ya kasance a tsakanin mace da namiji. Domin ana iya samun inda
mace zata auri mace, namiji kuma ya auri namiji domin wasu al’adu ba su hana
haka ba . Amma a ra’ayin wani masanin Dr Wester Mark (1984) yana cewa: “Akwai muhimmam abubuwa uku ga
kowane aure, sune biyan buƙata na kwanan aure da dangantaka a
tsakanin namiji da mace da kuma domin samun zuri’a (haihuwa)”
Bisa ga waɗannan ra’ayoyi da ke sama dangane da ma’anar aure , anan muna
iya cewa aure alaƙa ce ta zamantakewa tsakanin mace da namiji bisa ga amincewar
juna tare da bin wasu ƙa’idoji da addini ko al’ada ta aminta da su.
Don haka, aure a al’adar Hausawa da na Dakarkari
al’ada ce mai muhimmanci tattare da wasu hikimomi na musamman a cikin al’umma.
Daga cikin falsafar yin aure ga al’umar Hausawa da na Dakarkari sun haɗa da :
Bunƙasar arziki da samun ‘ya’ya(ɗiya) da tushen zuri’a da nuna kamala da
zumunci da biyan buƙatun aure da sauransu.
3.0
TSARIN NEMAN AUREN HAUSAWA DA NA DAKARKARI
3.1 Soyayya Tsakanin Saurayi Da Budurwa
Soyayya ita ce ƙauna ta wani mutum
ko wani abu daban. A zahiri an fi amfani da wannan tsakanin namiji da
mace musammam saurayi da budurwa. Soyayya a harkar aure wata aba ce mai
nuhimmancin gaske ga auren Hausawa da Dakarkari. Idan babu soyaya da wuya a iya
zaman aure , don haka soyayya ita ce ƙashin bayan zaman auren Hausawa da na
Dakarkari. Duk da yake ana iya samun zaman aure ba tare wata soyayya ba.
3.1.1 Tsarin soyayya a al’adar Hausawa:
A al’umar Hausawa, tsarin soyayya ta taka
muhimmiyar rawa a tsakanin saurayi da budurwa. Galibi wannan soyayyar ita ke ƙara
danƙon zama tare wanda zai haifar da aure. Bincike ya gano cewa, al’umar
Hausawa suna da soyayya iri biyu ne zuwa uku .Ga su kamar haka:
- Soyayyar da ke
haddasuwa saboda haɗuwar jinni tsakanin saurayi da budurwa. Wannan yana
iya shafuwar ƙirar jikin saurayi ko budurwa.
- Soyayya saboda hali,
ma’ana ɗabi’ar mutum
- Soyayya saboda hali
(arziki) watau ana samun ginuwar soyayyar Bahaushe saboda irin arzikin
gidan saurayi ko budurwa.
Duk waɗannan soyayya suna ginuwa ne yayin da
saurayi zai rinƙa ganin budurwa yana yi mata wata ‘yar ƙyauta. Bincike ya gano
cewa amfi samun soyayya ta zahiri a tsakanin saurayi da budurwa kafin zuwan
addini. Don haka, muna iya cewa soyayya a wannan zamani ta yi ƙaranci,
don an maye ta da sha’awa . Za ta yi yu saboda rashin wannan soyayya ake samun
yawaitar mutuwar aure a cikin al’umar Hausawa a yau. Domin ita sha’awa gushewa
ta ke, amma soyaayya ba ta gushewa. Hasali ma soyayyya ga Bahaushe a wancan
lokacin ta dogara ne a kan irin bajinta da kirkin saurayi, domin ba a duban
arzikinsa balle a dubi abin da za a samu daga cikin arzikin .
Wani abin kulawa anan shi ne , ga al’adar
Bahaushe saurayi ke ganin budurwa ya ce yana so,; duk da yake a al’adance
Bahaushe bai yarda saurayi ya rinƙa cuɗanya da ‘yanmata a tsakaninsu ba .Don
haka lamarin soyayya abu ne mai muhimmamci ga zamantakewar neman auren Hausawa.
3.1.2 Tsarin Soyayya a al’adar Dakarkari:
Kamar Hausawa , su ma Dakarkari suna da tsarin
soyayya wadda ke wanzuwa a tsakanin saurayi da budurwa musamman a lokacin da
samarin Dakarkari ke aiwatar da wata al’ada ta “Golmo” . Duk da yake wani
lokaci ana samun auren da iyaye kan tilasta ‘ya’yansu ba tare da soyayya ba,
amma galibi Dakarkari suna aurensu ne don soyayya. Duk da yake a yanzu ana
samun masu auren sha’awa.
Ga al’adar Dakarkari, budurwa ce ake neman
soyayyarta .A ƙoƙarin samun soyayyar yarinya saurayi kan shiga aikin “golmo”
tun yana da shekaru goma sha biyar (15) zuwa sama. Yin wannan aiki na golmo
yana ƙara danƙon soyayyar. Wannan kuma na faruwa saboda irin bajinta da dauriya
da hanƙurin da saurayi kan nuna wajen ayyukansu na yau da kullum. Haka a
soyayyar Dakarkari tana da walwala domin ba su kange cuɗanya tsakanin saurayi
da budurwa ba.
3.1.3 Bambanci Da Kamancin Tsarin Soyayyar
Hausawa Da Na Dakarkari:
Kamar yadda bayani ya gabata a baya , al’umar
Hausawa da na Dakarkari duk suna aiwatar da wannan al’ada ta soyayya. Amma ba a
rasa wasu ‘yan bambance-bambance ba, haka kuma ta wata fuska sun yi kama da
juna.
Da farko dai abin da ya bambanta tsarin soyayyar
Dakarkari da Hausawa ita ce walwalar soyayya. Domin a al’adar Hausawa ta hana
cuɗanya tsakanin saurayi da budurwa, amma su Dakarkari ba su hana wannan ba.
Ta fuskar kamanci kuwa , Dakarkari suna gina
soyayyarsu ne ta hanyar golmo inda ake gane bajinta da dauriya da hanƙurin
saurayi .Ga al’ada duk saurayin badakkaren da ya kasa yin golmo, to ya yi
abin kunya ko zagi a cikin al’umma . Kuma da wuya a samu budurwar da za ta so
shi . Wannan kuwa muna iya ganinsa idan muka dubi wasu al’adu na Hausawa kamar ɗauko
maiki na maguzawan kwatarkwashi. Haka kuma, kamar Hausawa su ma Dakarkari ana
samun sha’awa a tsakanin saurayi da budurwa, amma wannan bai zama hujjar
cewa ba su auren soyayya ba .
3.1.4 Falsafa ko Hikimar Da Ke Cikin Al’adar
Soyayya
Bisa ga bayanan da aka yi na tsakuren al’adar
soyayya, muna iya fahintar cewa, akwai wasu falsafa ko hikima na aiwatar da
wannan al’ada ga Hausawa da Dakarkari. Za ta yiyu saboda wannan ne ya sa
al’umar ba su cika yin aure ba sai an tabbatar da akwai soyayya a tsakanin
saurayi da budurwa .
Da farko dai za mu ga cewa, tana kawo
sanin halin juna . Idan kuwa aka samu matsalar soyayya ,to tun a wannan lokacin
ne ake rabuwa . Haka kuma cikin wannan lokacin ne ake samun gyaran halayen juna
. Bayan wannan , ta wannan zaman soyayya ne ake auna irin hanƙurin juna
da dauriya da sauransu a tsakanin masoya.
3.2 Zance ko Taɗi
Wannan shi ne zuwa hira da saurayi kan yi a
gidan budurwa ko wani muhalli na daban da suke haɗuwa a wani lokaci na musamman
. Galibi a irin wannan hirar(zance) ana tattauna lamurran yau da kullum ne.
3.2.1 Tsarin Zance A Al’adar Hausawa
Hausawa sun ba wannan al’ada muhimmanci sosai .
Don haka, sun tanadi wani tsari na musammam domin aiwatar da ita. Kuma ganin
cewa, Hausawa sun fahinci irin hatsarin da ke tattare da wannan al’ada ,sai
suka tanadi lokaci da wuri na aiwatar da wannan al’ada. Domin ba su yarda su
bar ‘ya’yansu ba tare da sa ido da jagoranci ba. Da farko za mu ga cewa wannan
al’adar sai da dare ko yamma ake yin ta, kuma galibi gidan budurwa ake
zancen, inda ake samun gidin bishiya ko zauren gida.
Haka kuma, Bahaushe na da tsarin zuwa da ‘yar
rakiya, kuma al’ada ba ta yarda saurayi ya rinƙa zuwa zance kullum ba , don
haka galibi an fi zuwa zance ranar kasuwar garin . Kuma Hausawa na da al’adar
bada kuɗin jin-kira . Amma duk da wannan, Bahaushe na da wata al’ada ta
tsarance inda saurayi zai rinƙa zance da budurwa har ta kai su kwana ɗaki ɗaya
,amma saboda gaskiya da aminci ba za su san juna ba .
3.2.2 Tsarin C’mene (Zance) A Al’adar
Dakarkari
A al’adance Dakarkari ba su hana cuɗanya a
tsakanin saurayi da budurwa ba ,don haka ba su keɓe wani lokaci ko wuri na
musammam da za su haɗu ba . Dakarkari a wancan lokacin kafin zuwan addini suna
haɗuwaa duk lokacin da suka ga dama amma wani abin kunya baya faruwa a
tsakaninsu. Saboda irin wannan aminci ne ya sa Dakarkari suna wata al’ada wurin
neman aure wadda ake kira “c’mene”(tsarance).A wannan lokacin zancen, saurayi
da abokansa suna ƙoƙari ne su ƙara danƙon soyayya a tsakaninsu. Don haka, a
al’adar Dakarkari ba su amfani da kuɗin kira; duk da yake a yanzu ana samun
wannan jefi-jefi.Kuma galibi raha ne da barkwacci ake yi ma juna. Amma duk da
rashin ƙangin da ba a yi wa saurayi ba na ganin budurwarsa duk
lokacin da ya ga dama, bai hana sa ido ga iyayensu ba .
3.2.3 Bambanci Da Kamancin Tsarin Zance A
Al’adar Hausawa Da Na Dakarkari
Abin da ya bambanta su ta fuskar tsari shi ne,
su Dakarkari ba su kange saurayi daga zuwa wurin budurwa ba a kowani lokaci ko
wuri na musammam ba. Haka kuma Dakarkari ba su kange cuɗanyar saurayi da
budurwa ba a kowani lokaci.
Ta fuskar kamanci kuwa, anan za mu ga tsarin
zuwan saurayi gidan budurwa da na ɗan rakiya da kuɗin jin –kira (kindin c’pogo)
duk waɗannan ana samunsu a cikin al’adun zance na Hausawa da na Dakarkarkari.
3.2.4 Hikimar Da Ke Cikin Tsarin Zance A
Al’adar Hausawa Da Na Dakarkari:
Akwai hikimomi da yawa da ke tattare da wannan
al’ada ta zance a tsakanin Hausawa da Dakarkari. Daga cikinsu kuwa sun haɗa da;
Cusa soyayya a tsakanin saurayi da budurwa,don yana basu damar fahintar juna da
tattauna muhimmam zantuka a tsakaninsu .Kuma wannan shi ke nuna ma jama’a ba su
da wata muguwar manufa a tsakaninsu . Domin ga al’ada, duk sauaryin da baya iya
zance a gidan budurwarsa to yana da wata muguwar manufa, kuma ba auren yake
nema ba. Kuma idan budurwa ba ta fita zance wata alama ce ta nuna ba ta son
saurayin . Don haka zance wani ma’auni ne na soyayya. Haka kuma idan muka
dubi lokaci da wuri , wannan lokacin iyaye sun dawo gida suna ganin duk wanda
zai zo gidansu. Kuma wanan lokacin an ba saurayi da budurwa damar taimaka ma
iyayensu wasu ayyukka da rana. Kuma wannan na nuna kunyar surukkai.
Ta fuskar amfani da ɗan rakiya kuwa, shi ɗansanda
ne mai kawo rahoton duk abin da ya faru tsakanin saurayi da budurwa .Haka kuma
yana zama ɗan saƙo a lokacin zance, yana kuma kare kaɗaitar saurayi da budurwa
, domin a wannan lokacin tana ɗan yin wasa da shi,don haka za ta fi ɗaukan
lokaci tana zancen. Bayan waɗannan,ɗan rakiya yana taimakawa wajen kai bante.Su
kuwa kuɗɗin jin- kira (kindin c’pogo) suna ƙara soyayya domin Hausawa na cewa:
“Hannun da ke karɓa ba ya cewa a’a” Kuma ƙyautar tana ƙara martaba da daraja a
idon budurwa da gidansu.
Bisa ga wannan dan tsokaci, za mu fahinci
al’adar zance ta taka muhimmiyar rawa wajen gwagwarmayar neman auren Hausawa da
na Dakarkari.
3.3 Matsayin Iyaye Wurin Neman Aure
Bisa ga tsarin neman auren Hausawa, iyaye
suna da muhimmanci. Da yake aure al’ada ce da ake yi domin zaman rayuwa baki ɗaya,
don haka, al’adar Bahaushe an aza ma iyaye haƙƙin neman ma ‘ya’yansu matar
aure. Don haka, iyaye suna biɗan ma ‘ya’yansu aure a gida mai asali domin su
suka san tarihin gidajen, kuma suna da masaniyar halin tarbiyar gidan. Anan
iyaye suna kulawa da wannan ne domin kaucewa gurɓata zuriyarsu da wani jini mai
tarihin wani abin kunya. Misali sata ko wata cuta ta musamman kamar kuturta.
Haka kuma, a lokacin neman auren, iyaye suna
duban inda yarinya za ta samu abinci. Domin abin kunya ne ga Bahaushe ya bada
aure ga gida wanda ba ya ciyar da matarsa. Za ta yi yu domin tabbatar da wannan
ne ake yin al’adun bikin ɗauko Maiki a kwatarkwashi ta yankin Zamfara a
matsayin wani ma’auni na nuna jarumtar saurayi.
Iyaye suna bada shawarwari kuma ga su da cika
fuska da iya gabatar da Magana.
3.3.1 Fitowa gida (Biɗar Iyaye) A Neman Auren
Hausawa
Iyaye suna fitowa biɗar aure ne idan sun
tabbatar da mutuncin gidan da za su neman auren. Anan idan za su fita sukan ta
fi da goro da ‘yan wasu kuɗi da za a aza sama. Kuma mafi yawa akan samu
dattijai ne ‘yan uwa su kai waɗannan kaya. Duk da yake a yanzu ana samun
masu bada auren ba tare da sanin dangin uwa ba balle na uba. Bisa
ga tsari, idan iyaye suka isa gidan yarinya, bayan sun gaisa sai su bayyana
abin da ke tafe da su.musamman kuma ana wannan neman ne a wurin iyayen yarinya
ko wani danginta na jini kuma namiji. A wannan lokacin sai iyayen yarinya suma
su faɗi nasu bayani na amincewarsu ko rashin amincewarsu. Duk da haka, wani
lokaci tun yarinya na ciki ko jaririya ake fara neman aurenta ta hanyar ba da
zobe da za a sanya mata mai nuna an yi kammenta kenan.
3.3.2 Gaisuwar Abokai
Wannan wani mataki ne daga cikin tsarin neman
auren Hausawa. Abokai su ne waɗanda mutum ke zaune da su lafiya suna yawo tare
da cin abinci tare da dai sauran mu’amaloli. Ita wannan al’ada ana yin ta ne
bayan saurayi da budurwa sun sasanta kansu da niyyar auren juna, kuma iyaye sun
isa gida neman auren an kuma amsa saurayin ya ci gaba da neman auren. Anan ne
saurayi zai samu abokansa domin su fito gaisuwa.A irin wannan lokacin ne ake
tura aboakai gaisuwar sanin dangin yarinyar. A al’adance idan za a tafi wannan
gaisuwar, ana zuwa da goro ne da wasu ‘yan kuɗi wanda za su rinƙa bayarwa. Kuma
lokacin wannan gaisuwar, saurayin da ke neman auren baya magana sai dai
abokansa su yi. Wannan al’adar ana yin ta ne domin gabatar da saurayi ga sauran
dangi domin su san sa, shi kuma ya san su.
3.3. 3 Tsarin Neman Auren (c’gai) Dakarkari
Lelna (Dakarkari) sun ba aure muhimmanci, don
haka sun shimfiɗa wani tsari na neman aure tun kafin zuwan addini. Bisa ga
al’ada, Dakarkari suna da hanyoyi da dama na neman aure. Daga cikin su kuwa,
akwai ta hanyoar iyaye da kuma tsakanin saurayi da budurwa.
Ta hanyar iyaye: Dakarkari sun ba iyaye daraja
sosai ta yadda aka bar masu ragamar neman ma ‘ya’yansu aure. Domin
a al’adance yaro bai da iznin neman ma kansa aure. Tadurga U.,(1997) yana cewa:
Idan aka haifi yarinya a gida,
idan akwai tsohon da ke son neman
wa ɗansa, yana iya shaida wa iyayen
wannan yarinya tun tana jaririya da
cewa ya kama wa ɗansa wannan
yarinya. To wannan ya tabbata domin
ba wanda zai auri wannan yarinya
sai yaron.
Irin wannan neman auren, ana yin sa ne ta
hanyar al’ƙawali inda za a kama ma yaro mata ta hanyar kai wani jan zobe.
Wannan zoben za a sanya wa yarinya shaidar cewa an yi mata kame.
Amma wasu Dakarkari nasu al’adar ta banbanta.
Misali hirar da na yi da Ibrahim Wakaso Galadiman Rambo cewa ya yi:
za a kai masara goyo uku a gidan
yarinyar kame, idan wata shekara ta dawo
a kai biyar. Anan uban yarinya zai
samu kuɗi wuri uku, a samu ɗan
ƙwarya a sa a ciki, idan an kai
wannan kayan, to rannan ne aka
tabbatar da kamen auren.
Yin wannan shi ya tabbatar da cewa, iyayen suna
son haɗa jini da juna. Ya ƙara da cewa, bayan an tabbatar da kamen idan yaro ya
kai shekara goma sha shida zuwa ashirin ne zai shiga golmo. Daga nan sai a samu
kwandon dawa a kai gidan sarukkai.
Ita wannan al’ada ta golmo wata bauta ce da
saurayi yake wa surukkansa na tsawon shekara bakwai ko ƙasa da haka. A wannan
lokacin golmo (nema), saurayi zai rinƙa zuwa gonar surukkai tare da
takwarorinsa suna noma. Idan rani ya yi, ya yo masu hakin baibayan ɗaki. Sai
dai a yanzu akwai damar idan saurayi ba zai iya cika shekarun bakwai ba, sai a
yanka masa wasu kuɗi ya biya a madadin sauran shekarun da ba zai yi golmo ba.
A hirar da na yi da mai unguwar Zuttu (maigari
kwai-masa) cewa ya yi:
Iyaye su ne ke biɗan ma yaransu aure,
duk da yake yanzu yara suke neman
ma kansu aure musamman a wurin bukukuwa
ko kasuwanni. Amma mai biɗa ba ya kai
komai sai iyaye sun haɗa kansu.
Ya ƙara da cewa bayan an samu haɗuwar kan iyaye
za a kai wasu kaya da ake cema ‘uv-kwanta’ inda ake samun turmin Atamfa
da Sabulu da Mai a samu wata tsohuwa da wasu daga cikin dangi a kai gidan
yarinya. Daga nan ne saurayi zai shiga golmo bayan ya yi ‘yadato’ na ƙare
samartakansa.
Amma mafi yawa a yanzu, saurayi ke fara neman wa
kansa aure ta hanyar sasantawa tsakaninsa da budurwar. Daga baya a tura iyaye
gidan budurwa neman auren.
Bisa ga wannna za mu fahimci Dakarkari suna da
tsarin neman aure kusan bai ɗaya da na Hausawa musamman idan muka dubi matsayin
Iyaye da fitowar Iyaye da gaisuwar abokai da sauransu.
3.3.3 Bambanci da kamancin tsakanin neman auren
Hausawa da na Dakarkari.
Al’umar Hausawa da na Dakarkari suna da cikkaken
tsari na neman aure. Kuma mafi yawan tsarin ya yi kama da juna illa wasu ‘yan
wurare da ba a rasa ba.
Ta fuskan bambanci, abin da ya shafi gaisuwar
abokai; Hausawa suna zuwa da goro da wasu ‘yan kuɗi a sama. Amma su Dakarkari
ba a zuwa da komai.
Ta fuskar kamanci kuwa, anan za mu ga cewa
dukkan ƙabilun, iyaye sun taka muhimmiyar rawa wajen neman aure, kana sun
amince a nemi yarinya aure tun ana da cikinta, wani lokaci kuwa sai bayan ta yi
wayo. Haka kuma, a dukkan ƙabilun iyayen namiji ne ke zuwa wurin iyayen yarinya
neman aure; kuma a wannan lokacin iyayen na zuwa da wata ‘yar kyauta ga dukkan ƙabilun.
Bayan wannan kuma, a lokacin neman samari suna yi ma gidajen surukkansu wata
‘yar bauta (golmo ko gayya) da dai sauransu. Don haka anan za mu ga cewa
waɗannan al’adu sun yi kama da juna ƙwarai da gaske.
3.3.4 Falsafar Da Ke Cikin Tsarin Neman Auren
Hausawa Da Na Dakarkari
Bisa ga al’ada, Hausawa da Dakarkari sun ba
neman aure muhimmanci sosai. Wannan kuwa ba zai rasa nasaba da irin hikima ko
falsafar da ke tattare da wannan tsari na neman auren ba.
Da farko dai za mu ga cewa, falsafan sanya iyaye
wurin neman aure shi ne cewa: Su ke da tarihin kowane gida domin sun ga jiya
sun ga yau. Da yake Bahaushe ko badakkare baya son haɗa jininsa da wani jini
wanda ke da tarihin wani abin kunya. Kuma iyaye suna zaɓen gida mai tarbiya,
domin ga al’ada ba a barin yara kara zube ba tare da jagorancin iyayensu ba.
Kuma iyaye suna duban halayen yara domin gane cancantarsu ko rashin
cancantarsu. Wata falsafa kuma ita ce, ƙara fahimtar juna da nuna soyayya tun
kafin auren. Wannan na haifar da kyautata halayen saurayi da budurwa. Haka kuma
gaisuwar abokai na tabbatar da maganar da iyaye suka yi a lokacin da suka fita
nema wa ɗansu mata. Wannan gaisuwar tana nuna yaron ya amsa shi ma yana son
yarinyar. Kuma a wanan lokacin yana sa iyaye su san surikinsu musamman abin da
ya shafi ƙirar jikinsa, irin kaifin hankalinsa da dai sauransu.
3.4. 1 Tsarin Na-Gani-Ina-So A Al’adar
Hausawa
A al’dar Hausawa, bayan Magana tsakanin
saurayi da budurwa da iyayen yaro da na yarinya ta zauna , watau an amince wa
juna. Daga nan ne za a kai kayan Na-gani-ina –so, su waɗannan kayan galibi ana
samun wasu dattijai maza ko mata ne su kai waɗannan kayan . zaɓen dattijai ba
zai rasa nasaba da irin matsayinsu a cikin al’umma ba, domin sun fi sanin irin
lafuzzan da za su yi amfani da su. kuma galibi waɗannan kaya ana haɗawa da ‘yan
wasu kuɗi da goro a ciki, sauran kayan sun haɗa da tufafin sawa da na kwalliya.
Anan yawan kayan ya danganta ne da irin ƙarfin arzikin gidan saurayi.
Bayan an kai waɗannan kayan ne za a dawo da
bayanin da aka samo daga gidan budurwa dangane da kayan.Waɗananan kayan za a
rinƙa yawo da su gida-gida ana nuna ma dangin yarinya , wani lokaci ma, goro da
kuɗin da aka aza sama ana rabawa sauran dangin shaidar cewa ‘yarsu ta sami
masoyi . Duk da yake kafin shigowar addini, Hausawa suna amfani da kayan gona
ne da wuri a matsayin kayan na-gani-ina-so.
3.4.2 Tsarin Na-gani-Ina-so A Al’adar
Dakarkari
Dakarkari su ma suna da tsari na musammam
dangane da al’adar na-gani-ina-so. Duk da yake ana samun bambance
bambance tsakanin wannan yanki na Dakarkari zuwa wancan. Bayan saurayi da
budurwa da iyayensu sun amince da juna, magana ta zauna. Daga nan ne za a
kai waɗannan kayan riƙo . Duk da yake wani lokaci iyaye na kai kayan ba
tare da sanin saurayi ko budurwa ba. Domin a al’adance yara ba su
da ikon kansu sai abin da iyaye suka zantar a kansu.
A wani sashe na Dakarkari kuwa, iyaye suna kai
kuɗi wuri ashirin da jan zobe wanda za a sanya wa yarinya a matsayin shaidar
ana kamenta. A wajen Dakarkarin Rambo kuwa, ana fara kai masara goyo uku, idan
wata shekara ta zagayo a kai masara goyo biyar. Haka kuma uban yarinya zai samu
kuɗi wuri uku ya kai, yin wannan shi ke tabbatar da kamen yarinya . Bayan
saurayi ya kai shekara ashirin sai ya kai kwandon dawa gidan surukkansa. Haka
kuma, zai yi asabari biyu ya kai gidan surukkansa.Amma a yanzu bayan shigowan
addini, Dakarkari suna amfani da kudi ne da wasu ‘yan kaya na sawa da na
shafe-shafe a matsayin kayan na-gani-ina-so.
3.4.3 Bambanci Da Kamancin Tsarin Na-gani-Ina-so
A Al’umar Hausawa Da Na Dakarkari.
Bisa ga al’ada musamman kafin shigowan
addini, bincike ya gano cewa, kusan duk tsarin aiwatar da wannan al’ada
ta na-gani-ina-so ɗaya ne tsakanin Hausawa da Dakarkari sai dai ɗan abin da ba
a rasa ba.
Da farko dai za mu ga cewa dukkan Hausawa da
Dakarkari suna amfani da kayan gona da zobe kafin zuwan addini, kuma waɗannan
kayan gona sun danganta da irin waɗanda ake nomawa a kowani yanki . Kuma dukkan
ƙabilun suna sanya iyaye dattijai wurin kai kayan na-gani-ina-so. Ta fuskar
lokacin kai kayan kuwa, duk tsari ɗaya suke bi, domin ba a kai su sai an
tabbatar da soyayya a tsakanin iyaye da saurayi da budurwa.
Bayan haka, ɗaukan kayan yana nuna an karɓi
manemin, rashin ɗauka kuwa yana nuna manemin bai samu karɓuwa ba. Wannan tsarin
kuwa duk ɗaya ne a tsakanin al’umar Hausawa da Dakarkari.
3.4.4 Falsafar Al’adar Na-gani-ina-so A Al’umar
Hausawa Da Dakarkari
Dangane da falsafar da ke tattare a cikin wannan
al’ada kuwa , gasu kamar haka:
Da farko dai wannan wata alama ce mai tabbatar
wa iyaye da sauran dangi cewa ‘yarsu ko ɗansu ya samu masoyi . Domin waɗannan
kayan na-gani-ina-so su ake rabawa sauran dangi su shaida cewa an fito gida
neman ‘yarsu.
Wata falsafa ita ce , karɓar wannan kayan na
nuna irin karɓuwar da saurayi ya samu a gidan budurwa. Domin a al’adar
Bahaushe, idan aka bada tukuici, to ya samu karɓuwa, idan kuwa aka karɓi
kayan aka ajiye ba tare da wata Magana ba , wanna yana nuna akwai shakku
ga mabiɗin. Amma idan aka tsaya binciken kayan, yana nuna dama akwai wani mabiɗi.
Anan za mu fahinci waɗannan kayan tamkar wani madubi ne da manemi zai kalla ya
san matsayinsa.
Kayan ga Hausawa da Dakarkari, suna matsayin
nizani na auna arzikin mabiɗi. Don haka, kayan suna ƙara ko rage darajjar mabiɗi
a gidan yarinya ko al’umma baki ɗaya. Musammam idan muka dubi yadda ake yawo da
kayan ana gwada ma dangi. Kuma waɗannan kayan suna ƙara danƙon soyayya a
tsakanin saurayi da budurwa . Yawansu na sa budurwa alfahari , amma idan ba su
cika ido ba, za a ji nauyin bayyana su.
A al’adance wasu na ganin ana iya auna arzikin
yarinya tun daga irin kayanta na na-gani-ina-so. Domin idan ta samu kaya masu
yawa , to wannan wata alama ce mai nuna budurwar tana da ƙashin arziki, idan
kuwa kayan ba su cika ido ba , to wannan na nuna ba ta da ƙashin arziki.
4.0
Kammalawa
Al’adun alumma sun bambanta daga wannan al’umma
zuwa waccan. Haka al’adun aure suna da yawa, kuma kowace al’ada akwai yadda
kowace al’umma ke aiwatar da ita. A wasu al’adun sukan ɗauki tsari ɗaya wajen
aiwatarwa, wasu kuwa ana samun wasu ‘yan bambance-bambance wajen aiwatar da su
a tsakanin wannan al’umma zuwa wata al’umma.
Bisa ga abin da wannan maƙala ta yi ɗan taƙaitaccen
bayani a kansu, za mu ga cewa an yi ƙoƙarin kawo wasu daga cikin gwagwarmayar
da ake yi lokacin neman auren Hausawa da na Dakarkari. Don haka, an zaɓi wasu
al’adu ne aka yi bayaninsu sama-sama. Daga cikin al’adun da aka duba sun haɗa
da: Al’adun soyayya a tsakanin saurayi da budurwa da zance ko taɗi da matsayin ɗanrakiya
da matsayin iyaye da al’adar na-gani-ina-so da sauransu.
Muƙalar ta yi ƙoƙarin kawo kamanci da
bambance-bambancen da ake samu wurin aiwatar da waɗannan al’adu a tsakanin
al’umar Hausawa da na Dakarkari. An yi ƙoƙarin kawo wasu hikimomi ko falsafar
da ke damfare a cikin waɗannan al’adu a tsakanin waɗannan alummomi.
A ƙarshe bisa ga ɗan abin da wannan maƙala
ta yi bayani a kai , za mu fahinci cewa al’umar Hausawa da na Dakarkari suna da
tsari kusan iri ɗaya da juna musamman abin da ya shafi al’adun neman aure da
falsafar da ke cikin aiwatar da waɗannan al’adun a tsakanin al’ummominsu. Ba
shakka, wannan nazarin zai ƙara sa fahintar juna wanda zai haifar da
zamantakewa mai inganci da nagarta ba tare da kushe wa juna ba a tsakanin waɗannan
al’ummomi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.