15) 'Yan uwanka ka iyakance
mata irin yadda kake so ta yi mu'amalla da su. In sun raina ta kai ka jawo mata. In ta wulaƙanta
yayyinka ba ta ɗauke
su komai ba duk kai ne sila...
Kundin Ma’aurata 46:
Kafin Ka Zama Maigida na Ƙwarai
Baban Manar Alƙasom
Zauren Markazus Sunnah
1) Ka tabbatar da cewa
aurennan saboda Allah SW za ka yi ba don kawar da sha'awa ba.
2) Ya zamanto cewa wace za
ka auro za ta iya ba ka kariya daga fadawa abubuwan da Allah SW ya hana.
3) Kar ka dogara da bangaren
sha'awa kawai wajen zabar wace za ka aura.
4) Uwar yara za ka auro,
wace za ta tarbiyantar da diyoyinka mata,
ba wace ita ma take buƙatar
tarbiyar ba, wanda bai da abu ba zai iya bayar da shi na.
5) Duk yadda za a yi ka
dauko wace za ta girmama mahaifanka da 'yan uwanka kamar yadda kake girmama su
kai ma.
6) Ka zabo wace za ta yi
musu hidima ta taimaka musu da wani aikin kamar yadda ta riƙa taimakon nata kafin ta zo gidanka.
.
7) Ka zabo matar da za ta
iya cuduwa da uwayenka a matsayin zuriya daya, ba tare da ƙyashi ko tsaginagini ba.
8) Ka yi tunani sosai wajen
daukar wace za ka iya tanƙwara
ta, ka saka ta a hanya ta ƙwarai,
ba wace in ka gama biyan sha'awarka za ta wargaza maka gida ka dawo kana
da-ka-sani ba.
9) Kar ka yarda ka yi mata ƙaryar mallakar abin da ba ka da shi, girmanka zai fadi a
idonta tun shigowarta gidanka in ba ta gansu ba.
.
10) Ka yi ƙoƙarin
bayyana mata wasu abubuwan da ka san za su iya bata ka a idonta kafin ta ji su
ta wata hanyar.
11) Tunda aurennan ibada ne,
ka yi tunanin yin abin da Allah SW ya yarda da shi don ya sanya muku albarka,
ka kiyayi abin da zai fusata mahalicci a ciki, kamar bukukuwan kide-kide da
cakuduwar maza da mata da bayyana tsaraici zuwa shaye-shaye.
12) Ka yi ƙoƙarin
yin walima wajen dafa abinci mai rai da motsi ka kira bayin Allah na gari su
ci, wato waɗanda za su yi maka addu'a su yi wa
mahaifanka.
.
13) Ka yi ƙoƙarin
zama da iyalinka tun farko ku sabonta fahimtar juna, kowa ya san abin da
junansa yake so da wanda ba ya so.
14) Ka nuna mata girman mahaifanka,
kai ma ka girmama su, sai ita ma ta dauke su yadda ka dauke su.
15) 'Yan uwanka ka iyakance
mata irin yadda kake so ta yi mu'amalla da su. In sun raina ta kai ka jawo mata. In ta wulaƙanta
yayyinka ba ta ɗauke
su komai ba duk kai ne sila.
16) Kar ka sabar mata da
abin da ka san ba za ka iya jure kawo mata koda yaushe ba, kamar kudi, ko
nau'in abinci, ko tufafin sakawa, ko matsuguni.
.
17) Ka sabar mata da ibada,
kamar salla kan lokaci da azumi irin na nafila da sauransu.
18) In ka ga ba ka da lokacin
koyar da ita addini ka yi ƙoƙari ka bar ta ta je inda za ta koya.
19) In ka yi mata alkawarin
wani abu kafin ka aure ta, kamar ci-gaba da karatun boko ka yi ƙoƙari
ka cika.
20) Ka fara kai ta wurin
uwayenka ka gaya mata yadda za ta taimake su.
21) In ka ga ba ta iya wani
abu na gida ba, ka samo hanyar da za a gyara cikin dabara da sauƙin kai.
22) Mace ba ta son hayaniya,
ka san yadda za ka riƙa yi
mata fada, da inda ya dace ka yi din.
23) Kar ka riƙa kushe ta idan ta yi maka abu.
24) Tana son in ta yi abu ka
yaba mata, ka daure ka riƙa
fadin ra'ayinka game da duk abin da ta yi maka.
25) Babban abin da ta fi buƙata shi ne a zauna da ita a saurare ta.
26) Komai shagulgulanka ka
riƙa ware lokacin da za ka zauna da ita ku
yi wasa da dariya.
27) Ka sani cewa mata da
yawa ba saduwar aure ne kadai matsalarsu ba, har da rashin zama da su.
28) Idan iyalinka ta fara
kawo maka kukan wani abu koda ka san shi ka saurare ta ta gama kafin ka fadi
ra'ayinka.
.
29) Ka sani cewa ba wai
mafita kawai take nema ba, tana ma son ka riƙa
jin matsalolinta kuna tattaunawa.
30) In ta yi kuskure ka yi
mata hanzari, dole hakan ya faru.
31) Kar ka riƙa raina hankalinta don ta saba maka,
kamar ka ce mata yarinya ko maras hankali.
32) In ka ga kuskurenta sau
daya ka tuna goma na arziƙi da
take maka.
33) Ka riƙa kallon bambancin dake tsakaninku na
shekaru da wayewa da wadata wurin yi mata hanzari.
34) Ka riƙa kallon cewa ita ma fa 'yar gata ce a
wurin mahaifanta kafin ka rabo ta da su ka kawo ta gidanka.
35) Ka dauke ta a matsayin
mataimakiyarka in kana gida, in kuma ba kanan ka ba ta kujerarka.
36) Ka sa ido sosai a yadda
take mu'amalla da kowa in kananan ko ba kanan.
37) In kana da matsala da
shimfida ka nemo magani.
.
38) Ki kiyayi wasu nau'o'in
abinci da suke rage sha'awa kamar abubuwa masu tsami ko daci, ko shan zobo ko
latas da 'yan mintuna kadan kafin jima'i.
39) In kana saurin kawowa ka
koyi dabarar saduwa, ka riƙa
tafiya mai tsayi a ƙasa,
ka lura da nau'in abinci.
40) Ka ji tsoron Allah wajen
saduwa, ka tabbatar ita ma tana biyan buƙatarta
ba kai kadai kake biyan naka ba.
41) In ka zo saduwa ka yi ƙoƙari
ta riga isa ƙololuwa don in ka
riga isa sauka za ka yi.
.
42) In tana da juna biyu sai
ka riƙa haƙuri,
saboda tsarin da Allah ya yi mata a lokacin na tsananin buƙatarka, da saurin fushi ba dalili ko
ninkuwar kwadayi.
43) Ka fahimci cewa haihuwa
ta Allah ce, in matarka ba ta haihuwa ba haka take so ba, kar ka ƙara mata damuwa.
44) Kar ka bari uwayenka ko
'yan uwanka su wulaƙanta
ta a kan abin da ba a hannunta yake ba.
45) Alhakin samun da namiji
hukuncin Ubangiji ne, sannan kai ne kake iya fitar da ƙwan namiji ko mace ba ita ba, kar ka ce
tana haifa maka 'ya'ya mata.
.
45) Ka sani cewa yawan
haihuwa ba matsalarta ba ce, kai kake yin cikin.
46) Kar ka matsa mata sai ta
yi tsarin haihuwa don abu ne da yake da jibi da lafiyarta, kai ma za ka iya yi
in kana so, ka nemi yardarta kuma ka nuna mata illolin da suke tattare da hakan
don kar ta zarge ka a gaba.
47) Ka taimaka mata a wurin tarbiyar
yaran, ka riƙa daukar jaririnku za
ta ji dadin yadda kake ba su kulawa.
48) Ka riƙa tambayarsu lafiyarsu kowani lokaci.
49) Ka tabbatar ta yi duk
allurorin da yaron yake buƙata
tun daga ciki har zuwa watannin da aka tsara masa.
50) Ka yi ƙoƙari
iyalinka su fi sonka sama da kowa.
51) Duk abin da za ka yi
musu ka san cewa haƙƙoƙi ne da Allah ya daura a wuyarka, ibada
kake yi, kar ka ce za ka bari don sun baƙanta
maka rai.
.
Ƙarshen
dan wannan littafi kenan, ba zan iya ambato duk waɗanda
suka ƙarfafa ni kan wannan aiki ba, amma ina
miƙa saduwar gaisuwa ga Sani Abu-Unaisa,
Maijidda Abdulƙadir, Albani Dabai,
Nura
Ja'afar Dallaje, Muhammad Inuwa, Musa Bala Gwarzo, Abu Husari Rabiu Abdu,
Imranatu M Usman, Muhammad Abu Muhammad Ramadan, Usouph Muh'd Sani, Fatima
Ahmad, Falalu Abdullahi, Ibrahim Nasidi Baban Ilham, Kabir Ahmed Abubakar,
Hauwa T Musa, Abdurrahman Mustapha, Baffa Adamu Safiyanu, Al Amin Rabiah,
A'isha Mahmud Yusuf, Rukayya Haruna, Alfa Usman, Abdullahi Muhammad, Sadear
Haidar, Pheenearh Isah, ba iyakarsu ba kenan, waɗanda
na dan iya kawowa kusa kenan, Allah ya saka da alkhairi, ina godiya da ƙwarin gwiwar da kuke ba ni.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.