Ticker

6/recent/ticker-posts

Hankaka Mai da Ɗan Wani Naka: Waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau a Bakin Mawaƙan Ƙarni na 21



Tsakure: Mazaunin wannnan maƙala shi ne nazari kan yadda mawaƙan Ƙ21 suke baddala waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau zuwa waƙoƙin zamani na kiɗan fiyano, shi ya sa ma aka yi mata take da ‘Hankaka Mai Da Ɗan Wani Naka’. An kawo tarihin rayuwa da gwagwarmayar da Sa’in Makafin Zazzau ya yi da kuma shahararsa a fagen waƙa duk da kasancewarsa makaho mabaraci. Binciken ya kawo mawaƙan da suka bi salon waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau tun daga makafi almajiransa da kuma mawaƙan zamani da suka baddala waƙoƙin nasa suka gwama su da kiɗan fiyano. Maƙalar ta gwama tsakanin gwanjo da orijina inda aka fito da waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau waɗanda mawaƙan Ƙ21 irin su Adam A. Zango (Ba ni bayanin Zango) da Funkiest Malam (Ga Lemu) da Sadi Sidi Sharifai (Direba Makaho, Idi Wanzami, Bayanin Naira) da sauransu.

Hankaka Mai da Ɗan Wani Naka: Waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau a Bakin Mawaƙan Ƙarni na 21

Na
Abdullahi Mujaheed
Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna
Waya: +2348069299109, +2348156747550
i-mel:mujaheedabdullahi@gmail. com
1. 0 Gabatarwa
Salisu Abdullahi Sa’in Makafin Zazzau ɗaya ne daga cikin shahararrun mabarata kuma mawaƙa a ƙasar Hausa. Cikin barar ne yake gudanar da waƙoƙinsa waɗanda suke ƙunshe da saƙonni daban-daban a ɓangarori na rayuwa da suka haɗa da siyasa da zamantakewa da nishaɗi da faɗakarwa da yabo da zuga da sauransu. Bisa wannan shahara tasa ne wasu mawaƙan zamani na Ƙ21 suka tasirantu daga waƙoƙin nasa, suke bin salo da tsari da karin muryar waƙoƙin Sa’in suna gudanar da nasu waƙoƙin na kiɗan fiyano. Domin haka wannan maƙala ta nazarci fasalce-fasalcen hankakancin da mawaƙan fiyano a Ƙ21 suka yi wa wasu daga cikin waƙoƙin nasa suka mayar da su nasu ɗauke da kiɗan fiyano. A wasu wuraren mawaƙan salo da tsari suke ɗauka na waƙoƙin Sa’in, a wasu wuraren kuwa har da jigon suke juyawa ya zamo nasu. Waƙoƙin da aka bi ta kansu wajen fito da wannan fasali su ne ‘Bayanin Naira’ da ‘Bayanin Ƙira’ da ‘Idi Wanzami’ ‘Direba Makaho’.
2. 0 Tuna Baya Shi Ne Roƙo
Duk da cewa ba a yi wani aiki kacokan a kan Salisu Sa’in Makafin Zazzau da waƙoƙinsa ba illa aikin Mujaheed (2017), manazarta kamar su Karofi (1980:160-203) da Ummar (2002:35) da Tukur (1985) sun yi tsokaci game da Salisu Sa’in Makafi da waƙoƙinsa ta fuskoki mabambanta. Karofi (1980:160-203) ya mai da hankali ne ga mabarata jimillarsu, ya nazarci tasirinsu da gudummuwarsu ga adabin Hausa, cikin mabaratan da ya bayar da misalai a kansu ne har da Sa’in Makafin Zazzau da waƙoƙinsa uku. Shi kuwa Tukur (1985), ya nuna cewa mawaƙan baka ciki har da Sa’in Makafin Zazzau sun bayar da gagarumar gudummuwa wajen yayata manufofin gwamnati. Sai dai bai taɓo wani abu game da waƙoƙin Sa’in ba, illa abin da ya sha masa kai na manufofin gwamnati cikin waƙoƙin nasa. Kamar yadda Ummar (2002:35), ya mayar da hankali ga nazarin illolin waƙoƙin bara na yau, amma duk da haka sai da ya nuna cewa waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau cike suke da faɗakarwa da nishaɗantarwa. Yayin da ita kuma Karima (2012), ta nazarci yadda mawaƙan baka ke ambaton abinci ne a waƙoƙinsu da kuma irin salon da suke amfani da shi wajen rattaɓo nason abincin Hausawa cikin waƙoƙin nasu, sai nazarin nata ya yi gam-da-katar ɗin kawo waƙa ɗaya ta Salisu Sa’in Makafin Zazzau cikin misalai wato waƙar ‘Bayanin Wulli”. Ita kuwa wannan maƙala ta fito da yadda mawaƙan zamani na Ƙ21suke baddala waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau cikin waƙoƙinsu na kiɗan fiyano.
3. 0 Sa’in Makafin Zazzau Da Waƙoƙinsa
An haifi Sa’in Makafin Zazzau Salisu Abdullahi Rafin-Mai-Baka, cikin shekarar 1933 a ƙasar Daura, daga bisani kuma shi da iyayensa suka baro ƙasar Daura da ƙuruciyarsa, suka koma Rafin-Mai-Baka. Iyayen Salisu Sa’in Makafin Zazzau ba makafi ba ne. Ya sami lalurar makanta ne tun yana jariri, lokacin bai wuce kwana arba’in a duniya ba, sakamakon cutar ƙyanda da ya yi fama da ita. Sa’i ya yi karatun addinin Musulunci gwargwado a lokacin ƙuruciyarsa, sai dai bai samu yin karatun boko ba (Hira da Haruna Galadima, ranar 20/12/2012).
A wajajen shekarun 1960 Salisu Sa’in Makafin Zazzau ya koma Zariya da zama. Maigidansa a Zariya shi ne Sa’i Ibrahim ɗan Tofa (wato mutumin Tofa ne kamar yadda sunansa ya nuna) kuma daga gare shi ne Salisu ya sami sarautar ‘Sa’in Makafi’ bayan rasuwar Sa’i Ibrahim ɗan Tofa. A birnin Zariya, Salisu Sa’in Makafin Zazzau ya zauna a yankin da ake kira ‘Marmara’ cikin ‘Unguwar Juma’ ta birnin Zariya daga bisani ya koma garin Kaduna da zama a farkon shekerun 1970. Sa’in Makafin Zazzau ya kasance ma’abocin hulɗa da gwamnati domin yana waƙoƙin farfaganda da yaɗa manufofin gwamnati. (Hira da Muhammad Lawal Salisu, ranar 10/03/2013).  Bayan shahararsa, kusan kowane lungu na arewacin ƙasar nan da kudu-maso-yamma babu jihar da Salisu Sa’in Makafin Zazzau bai sanya ƙafarsa ba. Wani lokacin yakan yi tafiye-tafiyen ne a karan kansa, wani lokacin kuma gayyatar sa ake yi. 
Salisu Sa’in Makafin Zazzau ya auri mata shida tsawon rayuwarsa ta duniya. Amma kamar yadda addinin Musulunci ya gindaya cewa namiji ɗaya zai iya auren mata huɗu ne kacal a lokaci guda, saboda haka Sa’in Makafin Zazzau bai zauna da waɗannan mata lokaci guda ba. Ana hasashen cewa mata uku ne ya zauna da su lokaci guda, wato Rabi da Amina da kuma Yalwa. Shi kansa Sa’in Makafin Zazzau ya jaddada haka da bakinsa cikin waƙarsa, inda ya ambaci waɗannan mata uku daga cikin matan nasa.
Ga abin da yake cewa; 
“Kai mai mata ukku,
 Rabi da Amina,
Saboda hakan nan
Zuwa kuma Yalwa
In ka samu Nairar ba su,
Kai ka zauna kai hakuri,
                         ('Y/ Amshi: An mana sabon launi). ”

Ta yiwu lokacin da ya yi wannan waƙa, matansa uku ne, bai riga ya yi ta huɗun ba. Dangane da ‘ya’ya kuwa, Salisu Sa’in Makafin Zazzau ya haifi ’ya’ya goma sha uku, cikin goma sha ukun nan, goma maza ne, uku mata. Sa’annan cikin wannan adadi, uku suna raye, goma kuma sun rasu a mabambantan lokuta.
An naɗa Salisu Abdullahi a matsayin Sa’in Makafin Zazzau a shekarar 1968, lokacin Sarkin Makafi Umaru. Kafin naɗin, ana kiran sa ‘Wazirin Samari’ ne. A ƙarƙashinsa kuma,  akwai yaransa da suke masa amshi waɗanda kowannensu da sarautarsa. Salisu Sa’in Makafin Zazzau ya rasu ne a watan 8, na shekarar 1988 (Hira da Sarkin Makafin Zazzau Ahmadu Tijjani Hassan, ranar 03/03/2013).
Sa’in Makafin Zazzau bai gaji waƙa ba, walau ta wajen mahaifi ko mahaifiyarsa, basira ce Allah (SWT) ya ba shi daga waƙoki na bara, har ya kai ga shahara ga waƙoƙi na fadaƙarwa da isar da saƙonnin gwamnati ga al’umma. (Hira da Haruna Galadima, ranar 20/12/2012). Ya fara waƙa ne tun yana Kano, musamman a lokacin da yake tare da ubangidansa Magaji na Ɗambatta, wanda aka ƙaddara shi ne ya koya masa waƙoƙin baran. Har ila yau, ya daɗe yana ‘yan waƙoƙinsa na bara, kafin shahararsa a wajajen shekarun 1965/1966 sakamakon rikicin juyin mulkin da ya kunno kai a lokacin. Wannan ne ya haifar da waƙarsa ta “Soja” wadda ta shahara sosai kuma ita aka fara sanyawa a gidan rediyo domin fadaƙar da jama’a dangane da muhimmancin haɗa kan ƙasa. (Hira da Haruna Galadima, ranar 20/12/2012).
Tun daga wannan lokaci, duk abin da ya tusgo daga manufofin gwamnati da take buƙatar a jawo hankalin jama’a, ko a gargaɗe su, sai Sa’in Makafin Zazzau ya shirya waƙa a kan abin, ya riƙa gudanar da ita yayin da yake bararsa a matsayinsa na makaho. Idan ‘yan jarida suka ji shi, sai su ɗauka su watsa a gidajen rediyo. Da abin ya ci gaba, tun yana yi a matsayin sa-kai, har ya kasance gwamnati ko hukumomin gwamnati musamman Hukumar Watsa Labarai da Gidan Rediyon Tarayya na Kaduna, suka riƙa neman sa domin ya tsara waƙoƙi game da wasu manufofin gwamnati, idan sun kunno kai ana buƙatar a yi wa jama’a farfaganda har manufofin suka sami gindin zama a zuƙatan jama’a. Alalmisali, sauyin kuɗi da aka yi a shekarar 1973 Sa’in Makafin Zazzau ya yi waƙar ‘An mana Sabon Launi’ wadda ta yi matuƙar tasiri ga manufar da ake son cim ma ga al’umma. Haka kuma ya yi waƙa game da sauya tuƙi daga dama zuwa hagu, duk a waɗannan shekaru. Shi kuma a ɓangarensa, Sa’in Makafin Zazzau yakan sami abin masarufi daga hukumomin da suka ɗauki alhakin waƙokin. Wannan ya haifar da dangantaka kyakkyawa irin ta cuɗan-ni-in-cuɗe-ka tsakanin Sa’in Makafin Zazzau da gwamnati.
Wajen shirya waƙoƙinsa, Salisu Sa’in Makafin Zazzau da yaransa, sukan zauna ne su tsara yadda amshinsu zai kasance, bayan tattaro bayanai game da abin da kayan cikin waƙokin za su ƙunsa, kafin su rera kowace waƙa. Daga nan ne, sai su rera a duk lokacin da ake buƙata. A wasu lokutan kuma, yakan ƙiri waƙa nan take idan buƙatar hakan ta taso. Dangane da waƙoƙinsa na farfaganda kuwa, gidajen rediyo su ne suke kasancewa mahaɗa tsakaninsa da gwamnati. Ta hanyar su ne yake samun bayanai game da abin da duk ake buƙatar ya waƙe.  (Hira da Haruna Galadima, ranar 20/12/2012).
Kafin rasuwarsa, ya yi waƙoƙi da dama, kuma ta hanyar waƙoƙin ne, yake samun duk abin masarufin da yake buƙata a rayuwarsa ta yau da kullum. Haka kuma ta hanyar waƙa ya sadu da jama’a daban-daban. Kuma ya sami shahara da ɗaukaka a duniya fiye da sauran takwarorinsa makafi. Wannan ya tabbatar da faɗin malam Bahaushe cewa ‘nakasa ba kasawa ba ce’.
Sa’in Makafin Zazzau yana daga cikin rukunin mawaƙan baka masu shirya waƙoƙinsu cikin ƙungiya inda yake a matsayin jagora, sannan da yaransa waɗanda su ne suke a matsayin ‘yan amshi. A tsarin ƙungiyar Salisu Sa’i, akwai shi kansa a matsayin jagora, sai kuma ‘yan amshinsa, waɗanɗa dukkansu makafi ne. Kowanne daga cikin ‘yan amshin nasa da matsayinsa kamar haka:
-          Abdu, shi ne Sarkin Yaƙi
-          Hudu, shi ne Ciroma
-          Haruna, shi ne Madawaki.

Sa’in Makafin Zazzau da bakinsa ya jaddada haka inda yake cewa:
“Ciroma Hudu,
Da Sarkin Yaƙi Abdu,
Da Madawaki Haruna,
Da ni kuma Sa’i Makaho…,
                       (‘Y/Amshi: An mana sabon launi. )”
                         
Haka wannan ƙungiya take zagayawa tana waƙe-waƙenta na bara a kasuwanni da wurare na musamman da sukan kai ziyara, ko idan an gayyace su.  (Hira da Haruna Galadima, ranar 20/12/2012).
Wasu daga cikin waƙoƙinsa sun haɗa da Waƙar Yabo’ ta 1 da ta 2 da ‘Kun Ji Barar Zamani’ da ‘Sa’idu Mai Mota’ da ‘Mahammadu ɗan Shu’aibu’ da ‘Alhaji Baƙo Zuntu’ da ‘Mainasara Daga Allah’ da ‘Shehu Kwasau Zazzau’ da ‘Gai da Aminu Haruna’ da ‘Alhaji Baital Lahi’ da ‘Don Mu Wadata Ƙasarmu’ da ‘A Daina Shan Ƙwaya’ da ‘Yan Ƙasa Mu Yi Ɗa’a’ da ‘Ba Ni Bayanin Naira’ da ‘An Mana Sabon Launi’ da ‘Zamani Na Rajista’ da ‘Mu Duba Sunayenmu’ da kuma ‘Gyara Ƙasa Sai Soja’. Sai kuma‘Bayanin Wulli’ da ‘Idi Wanzami’ da‘Bayanin Ƙira’ da ‘da ‘Direba Makaho’ da sauransu.
4. 0 Mawaƙan Da Suka Bi Salon Sa’in Makafin Zazzau
Karofi (1980:160-203), ya bayyana cewa:
“Malam Salisu shahararren mabaraci ne a ƙasar nan kuma Allah yi masa basira mai yawa, duk da Allah ya yi shi makaho. Shi ya sa ma kashi sittin cikin ɗari na mabarata makafi ɗalibansa ne kuma akasari shi ne ya ƙirƙiri waƙoƙin da suke rerawa, sai dai ‘yan canje-canjen da ba   a rasa ba. Misalin ɗaliban nasa su ne, Malam Ibrahim Kunkunna da Malam Ibrahim Sakkwato da Malam Audu Sakkwato. ”

Wannan haka yake, domin kuwa ko bayan rasuwar Salisu Sa’in Makafin Zazzau, an sami wasu makafin da suka cigaba da rera wasu fitattun waƙoƙinsa musamman a ƙasar Kano da Daura. Misali Ɗahiru Daura da Tafida Makaho sun shahara da waƙoƙin Idi Wanzami da Direba Makaho, har ma akasarin mutanen da suka san waƙoƙin a yanzu sun fi alaƙanta su a matsayin maƙirƙiran na asali maimakon Sa’i Makaho, ciki kuwa har da mawaƙan zamani da suka kwaikwayi waɗannan waƙoƙi. A yanzu an wayi gari da zarar an ji waƙoƙi irin su ‘Direba Makaho’ ko ‘Bayanin Naira’ ko ‘Idi Wanzami’ sai ‘yan zamani su fara tunanin Sadi Sidi Sharifai ko Ɗan Ibro . Ko kuma a fara tunanin Ɗahiru Daura ko Tafida Makaho ne maƙirƙiran waƙoƙin na asali (musamman a ƙasar Kano da Daura) alhali kuwa ainihin maƙirƙirin waɗannan waƙoƙi shi ne Salisu Sa’in Makafin Zazzau kamar yadda Karofi (1980: 160-203) ya tabbatar. Sa’annan ga mawaƙan zamani nan birjik kamar su Adam A. Zango (Ba ni bayanin Zango) da Funkiest Malam (Ga Lemu) da Sadi Sidi Sharifai (Bayanin Girki, Idi Wanzami, Bayanin Naira) da sauransu. Waɗannan mawaƙa da ma wasu da dama, sun tasirantu da salon waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau suna waƙoƙinsu na kiɗan fiyano a zamanance (Mujaheed 2017: 165).

5. 0 Baddala Waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau Zuwa Waƙoƙin Fiyano a Ƙ21
Tun kafin tasirin wasu baƙin al’ummomi kiɗa da waƙa ya samu gindin zama a al’ummar Hausawa. Daga baya ne zamani ya shigo da wasu abubuwa cikin waɗannan waƙoƙi na Hausawa (Gusau,  2012). An bayyana cewa a kafa ta waƙoƙin samartaka ne zamani ya shigo da tasirinsa a cikin waƙoƙin Hausa, wato waƙoƙin da samari da ‘yammata ke  yi (Gusau, 2008 : 345-360).  Waƙoƙin zamani sun kunno kai gadan-gadan ne a tsakiyar ƙarni na ashirin  (Ƙ20) zuwa ƙarshensa , wato bayan yaƙin basasa, lokacin da ƙabilun kudanci Nijeriya suka yawaita  (ɓarko) arewa da kuma yawaitar otel-otel a manyan garuruwan arewa. Tun a wajen shekara ta 1980 aka sami wasu makaɗa waɗanda suka dinga rera waƙoƙin Hausa ta amfani da kayan kiɗa baƙi. An sami makaɗa irin su Bala Miller da Fumi Adams da Audu Kwarisko da Sa’adu Bori da sauransu.  (Gusau, 2008: 348). A wajen shekara ta 1995 wasu Hausawa, musamman samari, suka fara tsara waƙa a rubuce sannan su samar mata rauji, su kuma rera ta amfani da  kayan kiɗa baƙi. Wasu su haddace waƙoƙin da ka,  wasu  su ajiye su a kasa-kasai da CD – CD. Zuwa shekara ta 2000 jama’a ta fara sabawa da waɗannan kaɗe-kaɗe na fiyano da ake tsarmawa a  cikin fina-finai.  (Gusau, 2008:349). Yawancin irin waɗannan mawaƙa idan suka zo maimaita rera waƙoƙin suna bin  rerawa ta farko ne daga CD wanda aka riga aka naɗa a sitidiyo, abin da  ake kira ‘Mamming’ da Ingilishi. Wannan kai tsaye tasiri ne baƙo wanda Hausawa suka samo shi daga tsari na  naɗar waƙoƙin Turawa. Ga abin da Alan Waƙa yake cewa game da wannan:
                  “Baituka na zo in yi da kiɗa na Nasaranci,
                         Kun ga na yi gurmi da kiɗa na Yahudanci,
                        Baituka da sauti da salon masu Hausanci,
                        Yakana na taso in gwada da badangalci,
                        Ibrahimu za mu taya godiyar Allah. ”
                                  (Aminu ALA: Waƙar Farfesa Malumfashi).
Bisa irin wannan tasiri ne mawaƙan zamani suka riƙa ɗaukar waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau suna rerawa a sitidiyo ta amfani da fiyano da sauran nau’o’in kayan kiɗan zamani. A yawancin lokuta, karin murya da saƙon iri ɗaya ne da na waƙoƙin Sa’in na asali, sai dai sukan bi wasu salo na zamani wajen tsara waƙar da kuma gwama su da kiɗa na zamani.
6. 0 Tsakanin Gwanjo Da Orijina
Sa’in Makafin Zazzau ba ya gwama waƙoƙinsa da amo na kiɗa, su kuwa mawaƙan Ƙ21 da suka ari waƙoƙinsa suka baddala zuwa nasu, sun gwama da kiɗan fiyano. Waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau kuwa suna da tsarin amshin Shata ne, wato amshi ɗaya ne na gindin waƙa ake ba yara, ba sa ƙarawa ba sa ragewa, komai ya ce gindin za su ci gaba da maimaitawa har sai ya gaji ya ba su wani gindin wata waƙar ta daban. Irin wanna salon amshi shi yake fitar da sunan galibin waƙoƙinsa. Misali, ‘Ba Ni Bayanin Ƙira’ da ‘Ba Ni Bayanin Wulli’ da ‘Gyara Ƙasa Sai Soja’ da sauransu. A irin wannan tsarin, ‘yan amshin suna maimaita gindin waƙar ne a kai, a kai, ba tare da sun numfasa ba har yakan zamo tamkar amshin ne kiɗan waƙoƙin kasancewar ba su da kiɗa. 
Abin da za mu yi a nan, shi ne fayyace fasali biyu na ire-iren waƙoƙin Ƙ21 da suka tusgo daga waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau. Fasali na farko shi ne ɗaukar salo da tsari na waƙoƙin nasa domin gabatar da wasu waƙoƙin zamani na kiɗan fiyano masu ƙunshe da saƙonni mabambanta da waƙoƙin Sa’in. Mawaƙan da suka bi wannan salo su ne Adam A. Zango da Billy O, a waƙarsu ta ‘Bayanin Zango’ da kuma Babawo da Habibullahi a waƙarsu ta ‘Bayanin Gausi’ sai kuma Funkiest Malam a galibin waƙoƙinsa.
Abin lura shi ne, su waɗannan mawaƙan zamani sun bi salo da tsari na wasu waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau ne kamar su ‘Bayanin Ƙira’ da ‘Bayanin Naira’ suka ari karin murya da tsari da salon waƙoƙin amma sai suka ƙunsa saƙonninsu daidai da zamanin da ake ciki da kuma manufar da suke so su isar ta amfani da kiɗan fiyano. 
A waƙar ‘Bayanin Naira’, Sa’in Makafin Zazzau ya faɗakar da jama’a kan muhimmancin a tashi a nemi naira don a huce takaici sannan ya tsarma jigon nishaɗantarwa a waƙar inda ya dubi alaƙar maigida da uwargidansa in yana da naira. A cewarsa, naira ita ce:
Abin sha'awa ga mutane
Abin riƙo a ji daɗi
Mai sa farin ciki ga mutane
Mai wanke zuciya sai Naira
Kai! Ku ji zancen Naira
Ku nemi Naira huce-takaici
Mai sa zaman jin daɗi
Ko a wurin zance, da iyali
In kana da Naira
In kai tari mai ƙarfi
Matarka na barci ta tashi
"Mai gida wane aikin za a yi?"
Saboda tsoron kada ka sake ta
          ('Y/ Amshi: Ba ni bayanin Naira)


A waƙar ‘Bayanin Ƙira’ kuwa, Sa’in Makafin Zazzau ya nishaɗantar da mutane ne ta hanyar ƙulla saƙonsa mai labarta wa maisauraronsa yadda a matsayinsu na makafi shi da yaransa suka je koyon ƙira, wani mai ido kuma ya lallaɓo kallon su, inda a ƙoƙarin makaho na ɗora ƙarfe a kan maƙera, kawai sai ya ɗora kan mai idon nan da yake kallon su tun da bai yi magana an ji shi ba, shi kuma makaho bai shafa ya ji shi ba:
Ƙarfe da wuta
Ni kuma babu ido a gare ni
Da nakai magana na biyu
Ashe da mai ido ya raɓe
Ganin ƙira ga makaho
Ina "ku ja sawunku"
Shi bai magana ba na ji shi
Ni kuma ban shafa ba na ji shi
Da na ɗauko ƙarfe
Na jefa za in yi ƙira
Ca nake na sa a maƙera
Ashe a kan cinyarsa na ɗora
Ya ji zahi ya maka ihu
Na ji tsoro na maka ihu
Gaba ɗaya duk muka miƙe
Muka tashi da rumfar ƙira
Ƙirar tun daga nan ta waste
        (Ba ni bayanin ƙira)

Irin fasalin waɗannan waƙoƙi ne wasu mawaƙan zamani suka ɗauka suka tsara waƙoƙinsu na kiɗan fiyano. Alal misali, Babawo da Habibullahi sun ɗauki amshin ‘Ba ni Bayanin Ƙira/Naira’ sun tsara waƙarsu mai amshin ‘Ba ni Bayanin Gausi’. Yayin da waƙoƙin ‘Bayanin Naira’ da ‘Bayanin Ƙira’ suke ƙunshe da saƙonni na faɗakarwa da nishaɗantarwa, ita wannan waƙa ta ‘Bayanin Gausi’ tana bayyana wa maisauare irin darajoji ne da karamomi ta Shehu Ibrahim Inyasi, sa’annan sun yi amfani da kiɗan fiyano amma karin muryar iri ɗaya ne da waƙar asali. Hankaka mai da ɗan wani naka! Misali:
            Jagora:             Subahanallahi
            'Y/ Amshi:       Ba ni bayanin Gausi
            Jagora:      Subahanallahi
           'Y/ Amshi:   Ba ni bayanin Gausi
           Jagora:       Ba ni bayanin Gausi
           'Y/ Amshi:    Ba ni bayanin Gausi
           Jagora:       Shin wai wane ne Barhama?
           'Y/ Amshi:    Ba ni bayanin Gausi
           Jagora:       Wasu duk sun san shi
          'Y/ Amshi:    Ba ni bayanin Gausi
          Jagora:       Wasu ko ba su san komai ba
          'Y/ Amshi:    Ba ni bayanin Gausi
                             (Waƙar Bayanin Gausi)

Su ma Adam A. Zango da Billy O, sun baddala amshin waƙar ‘Bayanin Naira/Ƙira’ ne suka bi salo da tsarinta suka shirya waƙarsu ta ‘Bayanin Zango’. Sai dai kamar yadda aka yi bayani a sama, yayin da waƙoƙin ‘Bayanin Naira/Ƙira’ Suke kimshe da saƙonnin nishaɗi da faɗakarwa, ita wannan waƙa Adam A. Zango ya shirya ta ne musamman domin huce haushi a kan ce masa arne da ake yi sakamakon wasu ɗabi’u nasa a harkarsa ta fina-finan Hausa. Ga abin da yake cewa:
                           Ku saurara,
                                Ku ji zancen Malam Zango,
                                            Zan fara bayani,
                                      To ku saurare ni,
                                To yau dai zan ɓaro ta,
                          Subahanallahi,
                         Walhamdullahi
                         La’ilaha illallahu,
                         Muhammadu Ya Rasulillahi,
                         Sunana Adamu Zango,
                         Ɗan Ibro jikan Abdu,
                          Ɗan Furera baban Haidar
                        Sannan jikan Hafsatu
                        Sun ce mini arne,
                       Malam wane ne arne?
                              La’ilaha ilallahu,
                                   O! Wai ni ne arne,
                      Muhammadurrasulillahi,
                     Ni na kama ƙafa da Muhamman
                      Domin shi zai cece ni.
                            (Amshi: Ba ni bayanin Zango).

Fasali na biyu kuwa shi ne ɗaukar salo da tsari da saƙonnin waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau kai-tsaye a sake maimaita su da kiɗan fiyano.  Sadi Sidi Sharifai shi ne mawaƙin zamani da ya fi shahara a wannan fage. Domin kuwa, tun yana yaro ƙarami, Sadi Sidi Sharifai ma’abocin wasa da dariya ne, akwai shi da son nishaɗi, duk lokacin da yake cikin sha’aninsa yana ɗaukar muryoyin mutane daban-daban yana kwatanta su kuma su yi tamkar na wanda yake kwaikwayo. Ko da a wajen waƙa ne yana yin amfani da muryar mawaƙi ya dinga rera waƙa irin ta mawaƙin ba tare da samun wani bambanci sosai ba. Yakan ɗauki waƙar Shata ya dinga rera ta da tsarin muryar da Shata ke amfani da ita a waƙar (Suleiman, 2013:20-21). Da irin wannan ƙwarewa ce Sadi Sidi Sharifai ya hankakantar da waƙoƙin ‘Idi Wanzami’ da ‘Direba Makaho’ da ‘Bayanin Naira’ cikin muryar ɗan Ibro. A waɗannan waƙoƙi, salo da tsari da saƙonnin duk iri ɗaya ne da waƙoƙin na asali, sai dai abin da ba a rasa ba na tsarma wasu ƙananan saƙonnin da kuma uwa-uba rera su da kiɗan fiyano. Hankaka mai da ɗan wani naka!
Waƙar Idi Wanzami:
Kamar yadda aka bayyana a sama, waƙar ‘Idi Wanzami’ tana daga cikin waƙoƙin da Sadi Sidi Sharifai ya hankakantar. Domin fitar da aya cikin tsakuwa, ga abin da Sa’in Makafin Zazzau ke cewa;
Idi Wanzami,
Ka ji yana yin aski,
Kamar ana fiɗar ɗan taure.

Idi Wanzami,
Wai wanzaman kirki,
Suna yawo da zabira,
Idi Wanzami,
Sai ya zubo askarsa a sanho.

Askarsa guda huɗu,
Kowace aska ga sunanta:
Ɗaya ‘Kura kya ci da gashi’,
Ɗaya ‘Ladanki na jikinki’,
Akwai wata ‘Wa aka samu?’,
Sannan ga ‘Кare dangi’.
Amma ita ‘Кare dangi’,
Idan ta fito daga sanho,
Rannan mutum dubu sa ƙare.


Askar Wanzamin,
Ka ji ma sunanta:
Walfa’ilati kurfan,
Summa walan luran,
Ɗaya Kurjama’u Jamila,
Kurjama’u Jamila
Wannan ba a biya mata lada,
Da kanta ma ta ɗiba.
                    (Sa’in Makafin Zazzau: Idi Wanzami)
Shi kuwa Sadi Sidi Sharifai a tasa waƙar ta ‘Idi Wanzami’ ya kawaikwayi salon Sa’in Makafin Zazzau ne kaitsaye ya gabatar da tasa waƙar. Misali:
Idi Wanzami,
Ka ji yana yin aski,
Kamar ana fiɗar ɗan taure.

Idi Wanzami,
Aska da tausayi shi babu,
Wai wanzaman kirki,
Suna yawo da zabira,
Idi Wanzami,
Sai ya zubo askarsa a sanho.

Askarsa guda huɗu,
Kowace aska ga sunanta:
Ɗaya ‘Kura kya ci da gashi’,
Ɗaya ‘Ladanki na jikinki’,
Akwai wata ‘Wa aka samu?’,
Sannan ga ‘Кare dangi’.
Subahanallahi,
Amma ita ‘Кare dangi’,
Idan ta fito daga sanho,
Rannan mutum dubu sa ƙare.

Sannan Wanzaman kirki,
Suna yawo da ƙaho,
Idi Wanzami,
Bakin garwa aka fafe,
Majaujawa ita ce ‘yar kamu,
Idi Wanzami ga shegen ƙarfi a gurinsa,
In yay i ƙahonsa ya ƙare,
Idan ya je zuƙa,
                 Sai ya fito da autar hanji.

Askar Idi Wanzami,
Ka ji ma sunanta:
Walfa’ilati kurfan,
Summa walan luran,
Sai Kurjama’u Jamila,
Kurjama’u Jamila
Wannan ba a biya mata lada,
Da kanta ma ta ɗib,
                 Subahanallahi!
                      (Sadi Sidi Sharifai: Idi Wanzami)
                     
Idan aka kwatanta ɗiyan waƙoƙin da suka gabata na Sa’in Makafin Zazzau da na Sadi Sidi Sharifai, saƙon da salon da tsarin duk iri ɗaya ne. Hatta kayan cikin waƙar da bayanin askar wanzami da yadda yake askinsa duk Sadi ya kwaso ne daga waƙar Sa’in Makafin Zazzau kaitsaye ya mayar da su nasa. Hankaka mai da ɗan wani naka!
Waƙar Bayanin Naira:
Waƙar ‘Bayanin Naira’, ta Sa’in Makafin Zazzau ta ƙunshi faɗakarwa ne ga jama’a a tashi a nemi naira da kuma ɗan abin da ba a rasa ba na nishaɗantarwa inda ya dubi musaman alaƙar maigida da uwargidansa game da sha’anin naira. Sa’in ya ce:
Abin sha'awa ga mutane
Abin riƙo a ji daɗi
Mai sa farin ciki ga mutane
Mai wanke zuciya sai Naira
Kai! Ku ji zancen Naira
Ku nemi Naira huce-takaici
Mai sa zaman jin daɗi
Ko a wurin zance, da iyali
In kana da Naira
In kai tari mai ƙarfi
Matarka na barci ta tashi
"Mai gida wane aikin za a yi?"
Saboda tsoron kada ka sake ta
     (Sa’in Makafin Zazzau: Ba ni bayanin Naira)

Shi ma Sadi Sidi Sharifai a tasa waƙar ta ‘Bayanin Naira’ ya hankakantar da waƙar Sa’in Makafin Zazzau ya bayyana darajar naira wajen inganta alaƙa tsakanin mace da namiji. A cewarsa:
Idan na ce yarinya,
Kin san babu ido a gare ni,
Sai ta ce kai Malam,
Don Allah manta da makanta,
Masu idon ma me suka fi ka,
Ga ka ɗan siririn yaro,
Kuma ga ka da kyawun fuska,
Kuma ga ka da damman naira,
Don Allah manta da makanta,
          (Sadi Sidi Sharifai: Ba ni bayanin Naira)


Domin sake fito da saƙon fili, a wani wajen kuma sai Sadi Sidi Sharifai ya sake jaddada batun, inda ya ce:
Amma in ba ni da naira,
Ko da mummuna ce,
In na ce ina ƙaunarta,
Sai ta koma gefe,
Ta ce La’ilaha illallahu,
Yanzu ka dubi kamata,
Sai ka ce ni ce matarka,
Ko babu maza a garin nan,
Ni me zan da makaho
Yaya zan yi in auri makaho,
     (Sadi Sidi Sharifai: Ba ni bayanin Naira)

Saboda haka, saƙon da salon duk iri ɗaya ne da waƙar ta asali, sai dai ‘yan ragi da ƙari da sauran kwaskwarima da ba a rasa ba a waƙar ta biyu wadda Sadi Sidi Sharifai ya yi.
Waƙar Direba Makaho:
Ita waƙar ‘Direba Makaho’ tun daga farkonta har ƙarshenta, labari ne na yadda makaho da abokan aikinsa (‘yan amshi) suka tafi Legas domin su kama sana’ar tuƙi, saboda barar da suke yi ta dame su. Da wannan salo ne mawaƙin ya labarta yadda suka nemi mota da inda aka ba su motar da kuma yadda lodinsu ya kasance. Sa’in Makafin Zazzau ya buɗe waƙarsa ne kamar haka:
Ina labari?
Direba makaho,
Yaya aka fara?
Wai sai ni direba makaho,
Karen motanmu makaho,
Ɗan kamashonmu makaho,
Kwandastan namu makaho,
Akawun namu makaho,
Duk babu mai ido a cikinmu.

Haba ‘yan amshi,
Kun san halin mota,
Masu ido ma ya suka ƙare,
Balle mota da makaho,
Sannan ba mu da ɗan jagora.
       (Sa’in Makafin Zazzau: Direba Makaho)

Shi ma Sadi Sidi Sharifai a tasa waƙar ya fara ne da bayyana yadda tuƙin motar tasu zai kasance tun daga direba da akawu da kwandasta da karen mato duk makafi ne, kamar dai yadda Sa’in Makafin Zazzau ɗin ya gabatar. Misali:
Ina labari?
Ƙaƙa muka ƙare?
Ƙaƙa muka ƙare?
            Ahalallah, Subahanallahi,
            Faifai na direba makaho,
Karen motanmu makaho,
Ɗan kamashonmu makaho,
Kwandastan namu makaho,
Akawun namu makaho,
Duk babu mai ido a cikinmu,
Haba ‘yan amshi.
       (Sadi Sidi Sharifai: Direba Makaho)

A dunƙule, wannan ya nuna a fili cewa hankakancin da mawaƙan zamani suke yi wa waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau suna da fasalce-fasalce iri biyu, yayin da a kaso na farko wasu mawaƙan suke ɗaukar salo da tsarin waƙoƙin nasa su gabatar da nasu waƙoƙin da mabambanta jigogi, shi Sadi Sidi Sharifai kaitsaye yake ɗaukar waƙoƙin ya sake rera su da kiɗan fiyano.

7. 0 Kammalawa
Duk da irin shahara da waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau suka yi, a yanzu an wayi gari da zarar an ji waƙoƙi irin su ‘Direba Makaho’ ko ‘Bayanin Naira’ ko ‘Idi Wanzami’ sai ‘yan zamani su fara tunanin Sadi Sidi Sharifai ko Ɗan Ibro. Ko kuma a fara tunanin Ɗahiru Daura ko Tafida Makaho ne maƙirƙiran waƙoƙin na asali (musamman a ƙasar Kano da Daura) alhali kuwa ainihin maƙirƙirin waɗannan waƙoƙi shi ne Salisu Sa’in Makafin Zazzau. Ga kuma mawaƙan zamani nan birjik irin su Adam A. Zango (Ba ni bayanin Zango) da Funkiest Malam (Ga Lemu) da sauransu. Waɗannan mawaƙa da ma wasu da dama, sun tasirantu da salon waƙoƙin Sa’in Makafin Zazzau suna waƙoƙinsu na kiɗan fiyano a zamanance. Saboda haka, aka rarrabe tsakanin gwanjo da orijina, inda aka bayyana tarihin rayuwar Sa’in Makafin Zazzau da shahararsa a fagen waƙa. Sannan kuma aka fayyace fasali biyu na irin hankakancin da mawaƙan Ƙ21 suka yi wa wasu waƙoƙin nasa.

Post a Comment

0 Comments