Lokaci wani
zamani ne. A hangen wasu masana wani zarafi ne da ba shi da bagiren da za a
riske shi bayan an yi gaba da gaba da shi ya ba da baya. A ganin matasa, wani
yayi ne da ke tashe sa’ar da aka miƙa wuya gare
shi gadan-gadan. Idan aka ba shi baya ko ya ba da baya sai ya wuce kamar ruwan
faƙo.
A tunanin Bahaushe, komi na da lokacinsa, idan ba a yi katari da lokacinsa ba
za a yi aikin banza wa kare wanka. Idan an dace da lokacinsa za a ga an yi dace
tsintuwar guru a cikin suɗi. Ashe gaskiyar masana da ke cewa, mutum uku
suna cikin wahalar da ba ta da ranar hutawa. Na farko shi ne, wanda lokacin abu
ya yi, ya ƙi mika kai bori ya hau, wai shi bai yarda ba sai
ya gani…
Lokacin
Abu A Yi Shi
Aliyu Muhammad Bunza
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya
Jami’ar Umaru Musa Yar’adua
Katsina, Nijeriya.
Takardar
da aka gabatar a bukin ƙaddamar da Littafin Kyakkyawar Safiya Tarihin
Mai Girma Sarkin Kabin Yabo Alhaji (Dr) Muhammadu Maiturare II, na Malami Umar
Torankawa, Ranar Asabar 31 ga Mayu, 2014 da ƙarfe 11 na
safe a ɗakin taron
makarantar tunawa da Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo, Sakkwato.
Gabatarwa
Lokaci
wani zamani ne. A hangen wasu masana wani zarafi ne da ba shi da bagiren da za
a riske shi bayan an yi gaba da gaba da shi ya ba da baya. A ganin matasa, wani
yayi ne da ke tashe sa’ar da aka miƙa wuya gare
shi gadan-gadan. Idan aka ba shi baya ko ya ba da baya sai ya wuce kamar ruwan
faƙo.
A tunanin Bahaushe, komi na da lokacinsa, idan ba a yi katari da lokacinsa ba
za a yi aikin banza wa kare wanka. Idan an dace da lokacinsa za a ga an yi dace
tsintuwar guru a cikin suɗi. Ashe gaskiyar masana da ke cewa, mutum uku
suna cikin wahalar da ba ta da ranar hutawa. Na farko shi ne, wanda lokacin abu
ya yi, ya ƙi mika kai bori ya hau, wai shi bai yarda ba sai
ya gani. Na biyu, wanda lokacin abu bai yi ba ya ce sai ya yi shi. Babban wahaltacce
na uku shi ne, mai ba su shawara da su dage su sa ƙwazo, har da
faɗar ba a san maci tuwo ba sai miya ta
ƙare.
Kada in cika ku da gafara sa ba ku ga ƙaho ba, ga
bakin zaren tunanina.
Na Gaba Idon Na Baya
Mutumin
da ya rasa tarihi an taƙaita masa sake jiki cikin masoya, an hana masa
miƙe
ƙafafu
cikin magabatansa. A kowace al’umma gabaci abin bege ne da tinƙaho ga
mamaya baya. A addinance gabaci abin koyi ne. A ilmance wata babbar madogara ce
ga na baya. A tarihance, komai saurin Laraba tana barin Talata ta wuce. Sanin
irin ƙimar gabaci ya sa a tarihin duniya kowa ƙoƙari yake ya
taskace gabacinsa ya zama furen kallo a kowane zamani ya rayu. Dalilin da ya sa
ke nan takardun kuɗaɗen duniya ke ɗauke da
hotunan magabatan ƙasar. Wasu wurare a sassaƙa surorinsu
a matsayin gumaka da za a adana a gidajen tarihi. Wasu a kafa su a ƙofofin
birane ko tsakiyar manyan wuraren shawagin jama’a a ji su, a gan su. Wasu a yi
wa daularsu ko ƙasarsu ko garinsu ko unguwarsu suna da
sunayensu. Wasu a taskace tarihinsu a adabin bakan al’ummarsu. A ci gaban
zamani, yau rubutu ne babbar hanyar adana tarihin magabatanmu. A nawa gani, ya
yi kusan zama tilas ga ma’ilmantarmu su tashi tsaye ganin sun taskace tarihinmu
domin sanin:
Fakon Kaya Ya Fi Ban Cigiya
A
tarihin duniyar baƙar fata, ba a taɓa
ba Turawan mulkin mallaka mamaki ba kamar yadda aka ba su a ƙasar Hausa.
Sun tarar da daulolinmu nagartattu girkakku. Sun sami mutanenmu amintattu
fitattu ‘yantattu. Sun tarar da tsarinmu daidai da rayuwarmu. Sun sami ƙasarmu da
addinin da ya koro su daga ƙasashensu. Sun tarar da
tsarin dokokinmu da shari’armu ba su buƙatar gyaran
fuska ga kowane mahaluki. Sun riske mu da ilmin da bai da ƙila-wa-ƙala kuma ba
ya jin kunyar idon kowane masani. Babban abin da ya ɗaure musu kai ya ɓatar
musu da ƙidaya shi ne, sun tarar da shugabanninmu ba su
yarda a ci gajiyar talakka da su ba. Talakawa ba su yarda a taɓi gabacinsu ba sai dai komi taka zama ta zama.
Wannan dalilai suka tilasta Turawa ɗaukar
makamai na fuskantarmu da sarakunanmu gadan-gadan abubuwan da suka auku su
auku.
Jin haushin haka ya sa masanansu ke ta
rubuce-rubucen izgili a kan ƙasashenmu da shugabanninmu.
Wasu su ce, ba mu da tarihi. Wasu su ce, daga birai muka fara. Wasu su ce,
rayuwarmu ta dabbobi ce. Wasu su ce, ba mu da tsarin shugabanci bale na siyasa
da walwala, ga su nan dai. Abubuwan nan suna nan a rubuce a duniyar karatu kuma
da su wasu takkwalan ‘yan boko ke cin abinci suna koyar da ‘ya’yanmu cewa
kakanninmu dambalallu ne, mayaudara ne, fitinannu ne, wai don ɗai sun ƙi magana da
hanci da ƙwambo da kirshe da ragama da soka alƙalami hagu
zuwa dama. Wannan ita ce musibar ƙarninmu. Don
haka, duk abin da zai yi fito-na-fito da ita tilas mu ba shi goyon baya. Irin
wannan aiki na daga cikinsu.
Lokaci Ba Ya Jira
Lokaci ya yi na a ce, a yau tarihin ƙasarmu da na
magabatanmu mu muka rubuta abinmu da kanmu. Manyan sarakunan daulolinmu mu
tabbata suna cikin kundayen tarihin da ‘ya’yanmu ke karatu. Al’adunmu da
harshenmu da adabinmu su taskace a ɗakunan
karatunmu. Yaƙe-yaƙenmu da sulhunmu
da ƙaurace-ƙauracenmu da
abubuwan da suka wakana a ƙasashenmu mun san su mun
taskace su da alƙalaminmu. Ku dubi shigen kutsen da baƙin al’adu ke
yi muna suna son su rinjayi tantagaryar sahihin tarihinmu. Yau fitattun mawaƙanmu na baka
sai dai a garmahon ƙauyawa. Cimakarmu ta gargajiya sai dai a cikin
wasan kwaikwayo. Tsarin suturorinmu sai a bukin daba. Uwa uba, ladabi da
biyayya da muka yi wa maƙwabta fintinkau a yau ya zama rashin wayewa da
rashin sanin ‘yancin kai. Fito-na-fito da hukuma, gwada tsawo da mahaifa, cin
zarafin gabaci, yin ido huɗu da kunya,
yi wa ƙarya cefane, baƙi ne a ƙasarmu.
Wanda duk ya ba su masauki Allah Ya isa muna. Idan muka sa wa lokaci ido zai
kama musu gidan haya a ƙarƙashin
‘yancin demokraɗiyya. Don
haka, za mu ce:
Da Abinmu Aka Gan Mu
Idan dai tsarin demokraɗiyya za a yi dodo-rido da shi a yi wa tsarinmu idon marurugiya, a yi furjin
mussa (mussa) da mu da sarakunanmu da shugabanninmu. To! Tun kafin a haifi uwar
mai sabulu balbela tana da farinta. A irin tsarin sarautun ƙasashenmu,
demokraɗiyya wasan yara ce.
Sarakunanmu ba dodanni ba ne irin sarakunan Turai da Asiya da ƙasashen
Larabawa. Kowane fanni na rayuwa yana da mai sa ido a kai. Kowace sana’a tana
da jagora. Kowane jinsi yana da shugaba. Kowace fasaha tana da jagora. Kai!
Hatta da naƙasassu da marasa galihu da ‘yan gudun hijira da
tawagogin musiba ba a yi ko oho da su ba. Abin ban haushi, waɗanda suka saci tsarinmu, wai yau su ke da ƙima ga idon
masu ilmin boko, kayansu ne na gaske namu ne jabu. Aka sace magungunanmu na
asali aka bar bokaye bautar Iskoki. Aka rusa littattafan aƙida na masu
jihadi, aka raya na tsibbu. Aka haramta wa maƙeranmu
fasahar ƙera makamai, aka bar su da yuƙa da
takubban faɗa da
junansu. Aka rusa muna fasahar saƙa, aka cika
mu da Osho. Haka ma tunanin kakanninmu na, in ka ci ya ƙare, in ka
ba wani ya ƙaru, a yau, ya koma in ka ci ka ƙoshi, in ka ɓoye, ka daɗe kana cin
abinka. Idan dai an fahince ni, to za a ga, rubuta tarihin shugabanninmu da
magabatanmu wani farfaɗon tunatar
da mu zancen Farfesa Ibrahim Narambaɗa Tubali
ne:
Jagora:
Banza sharanin maras kare
Sai kuwwa, sai ko wanda yak kasa
Ya ce mishi anshi rataya
Gindi:
Ya ci maza, ya kwan shina shire
Gamda’aren Sarkin Tudu Alu
Baya
Ba Ta Da Kaɗan
A yau jihadin Mujaddadi bai cika ƙarni uku ba,
har yanzu ba za a rasa tsofaffin da kakanninsu aka yi yaƙin ba. Duk
da haka, Turawa sun cika shi da ƙura da ature
da zantukan ɓatanci irin:
Jihadin Fulani, daular Fulani, daular Usmaniyya. Masu jihadi ƙwacen mata
suke yi (wato irin na ‘yan ɗaukar
amarya). Mujaddadi gabanin ya rasu ya samu motsuwar hankali a kan kashe mutane
da ya yi. Mujaddadi ya raba ƙasa biyu ta ɗansa da ƙanensa.
Jihadin ƙabilanci ne. Domin tattalin arziki aka yi shi.
Sarkin Musulmi Attahirun Amadu layar zana ya yi aka kamo shi aka kashe. Wanda
duk ya ratsi ire-iren waɗannan
sokiburutsu zai ga hikimar marubutanmu na gida da ke ta ƙoƙarin taskace
tarihinmu domin Kabawa cewa suka yi, ba don kifin da ya wuce akan yi saba ba,
don mai shirin komowa. A kakkaɓe wundin
jawabinmu ina son a lura da lokaci ka da mu yi:
Saki Zari Kama Tozo
Ga alama mun riga mun yi kamun gafiyar
Ɓaidu.
Take-taken da tsarin Turai ya yi wa magabatanmu na mulki da siyasa ya sagarta
mu muka yi zaton jini a babe. Mun yi wa sarakunanmu da masarautunmu riƙon sakainar
kashi. Mun yi wa addininmu dubin mai bisa ruwa. Muka yi wa al’adunmu kallon
hadarin kaji. Ƙasarmu da yankinmu muka muzantar da su. Kaico!
Wai duk irin wayonmu ya zama na banza, muka sayar da gona muka sayi kwasa. Muka
sa gida kasuwa domin biyan dukiyan aure. Ni dai abin da ya fi ba ni takaici shi
ne, mu sayar da jaki mu sayo mangala, kun ko san ko Buzu ya haukace ba ya
sayar da raƙumi ya sayo
akala. Da gangan muka sa kanmu cikin ƙuncin da
babu lada babu la’ada. A gai da Narambaɗa da ke
cewa:
Jagora:
Ko dauri kyawon ƙunci
In da Musulmi ka zama
Ana ta saka kullum
Ana ta bautan Allah
Ana ta samun lada
Kun ji kyawon ƙunci
Yara:
Wani ƙunci sai jaɓa
Sai karen daji
Sai Ƙadangare sai
Tunku
Gindi:
Sardauna kandaren Magajin Rafi
Na Baciri Baban Madaye mai ban tsoro
Kayya! Mun
riga mun shiga wannan ƙunci. Yanzu ina mafita? Ga nawa Basakkwacen
tunani zan ce:
In Ba a Ɗatu da Yaro
a ba shi Daddawarsa
Sarakunanmu
sun sa baki an yi biris da su. Da mu ake gama baki a ci musu mutunci saboda
biyan buƙatun siyasarmu. Shugabannin addininmu an gano
sirrinsu an yi musu takunkumi da Ɗangote da
taliya da kujerun Umura. Ƙungiyoyin addininmu sun fi Ɗanƙwairo jiran
tsammani. Limamanmu sun zama ‘yan kwangila masu wa’azi da nasiha su ne wakilan
mazaɓu. An yi tsaye an raba addini da
siyasa a Arewa domin bai wa maƙiya ƙarfin guiwa
su karya ko babu gaɓa. Abokanin
zamanmu addininsu ɗaya,
siyasarsu ɗaya, yankinsu ɗaya, aƙidarsu ɗaya, da burinsu ɗaya
na ganin ba mu sake tasiri a farfajiyar ƙasarmu ta
gado ba. Gwannoninmu da suka hango wannan ta’asar suka riddance wa kowace irin
hanya da za a yi muna kisan kashi a yi muna korar ɓarawo a ƙasarmu ta
gado. Kash! Sai wasu daga cikinmu suka fifita aƙidar siyasa
sama ga aƙidar Laa’ilaaHa illal Laahu. Allah ka cece mu,
ka da ka bari a cuce mu.
Naɗewa
Duk mai karatun jaridun ƙasar nan ya
san Musulunci na cikin ta tsaka mai wuya. Wanda duk ke sauraren kalaman
shugabanninmu ya san Musulmi sun shiga uku. Take-taken abokanin zamanmu na
tarayya na a kashe mu ne a ƙona, ba na a hura wuta kowa
ya ga rabonsa ba ne. In dai da demokraɗiyya muke
tinƙaho
ta cece mu, to, mun nuta bai wuri. In da yawan ƙuri’a muke
zaton mu ƙwato haƙƙinmu, ga
irin abubuwan da muke gani an riga an gama ƙidan ƙuri’u tun
bara tare da ‘yan’uwanmu (da za a kashe mu tare) abin da ya rage sanarwa. Cikin
siyasar BOKO HARAM an yi muna taron dangi. Rugumutsin ‘ya’yanmu na Chibok
fassararsa Arewa ta koma Iraqi da Siriya. Allah Ya isa.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.