Al’ummar Gobirawa wata al’umma ce wadda take da
wani mafificin gurbi a tarihin Hausa da Hausawa. Babu wata hanya da tarihin
Hausa zai iya bi ya kaucewa wannan al’ummar. Wasu masana suna ganin cewa
Gobirawa su ne asalin Hausawa, wasu kuma suna ɗaukar su…
Dr. Haruna Umar Bunguɗu (Sarkin
Gobir Bunguɗu)
Kibɗau:harunaumarbungudu@gmail.com
Lambar waya: 08065429369
Da
Muhammad Aminu Saleh
Lambar Waya: 08036166585
Sashen Hausa, Kwalejin Ilimin da Ƙere-Ƙere Ta
Gwamnatin Tarayya,
Gusau, Jihar Zamfara.
Tsakure
Al’ummar Gobirawa wata al’umma ce wadda take da
wani mafificin gurbi a tarihin Hausa da Hausawa. Babu wata hanya da tarihin
Hausa zai iya bi ya kaucewa wannan al’ummar. Wasu masana suna ganin cewa
Gobirawa su ne asalin Hausawa, wasu kuma suna ɗaukar su koma-baya. Wane dalili ne yake haifar
da mafi yawan mutane ke ɗaukar Gobirawa waɗansu mutane na daban? Yaya su kansu Gobirawa
suke kallon kansu a wannan al’umma ta Zamfara? Gobirawa sun warwatsu ko’ina a ƙasar
Zamfara kuma ko’ina suka je sukan yi fice har kowa ya san su, su wane ne abokan
wasan Gobirawa kuma me ya janyo kowa yake wasa da su? Shiga wannan takarda don
samun cikakkun bayanai a kan waɗannan har ma da wasu.
1.0 GABATARWA
Ƙasar Gobir
tana ɗaya daga
cikin ƙasashen Hausa na ainihi, an ce ita ɗin tsohuwar
daula ce kuma wata babbar ƙasa ce da ta yi iyaka
da Zamfara daga Kudu, ta yi iyaka da Mayali daga Gabas, sannan kuma daga
Yamma ta yi iyaka da Ƙwanni.
Ana ganin cewa asalin Gobirawa su ba
Hausawa ba ne tunda wasu na cewa asali wai daga Gabas ta tsakiya suka fito
musamman ma Misira, inda ake da yaƙinin cewa
sarakuna uku daga cikin sarakunan misira Gobirawa ne. idan aka waiwayi tarihi
Hausawa suna danganta kansu da misirawa domin an sami harshen Hausa a can wani
daɗaɗɗen zamani a
Misira, Malumfashi (hira da gidan rediyon Jamus).
Sarkin
Gobir mai daraja Alhaji Abdul’hamid Balarabe Salihu ya taɓa faɗar aslinsu a
wata hira da jaridar ‘Daily trust’ ta yi da shi, inda yake cewa:
Gobirawa sun zo ne daga Misira
(egypt), har ya ce su jikokin Annabi Nuhu A.S ne kuma sun bar Misara saboda
wahalar mulki na sarakunan lokacin . Shi ne suka sauka wani wuri mai suna
Gubur. Daga nan ne suka samo sunan Gobir. Ya cigaba da cewa daga baya sun bar
Yemen, Sun yi yaki sosai a ƙasar saboda su suna da jinin
yaƙi
da jarunta. Daga nan kuma sai suka isa Libya, a haka suna matsawa har suka zo
wani gari mai suna Azbin inda yanzu mutanen Taureg suka mamaye. Da suka bar
Azbin sai suka shiga sahara, har suka kafa wani gari mai suna Magali, daga baya
sai suka bar garin izuwa wani mai suna Surukul (dukkansu yan zubainar
jamhuriyar Niger ne). A hankali suka riski birnin lalle da gwararramu a ƙarni na 15
zuwa na 16. A lokacin kuwa, Sarkin Zamfara Abarshi ke mulki wanda yake da zama
a Katanga, kuma an samu har ya auri ɗiyar sarkin Gobir Ibrahim Babari.
Kafin Babari ya zamo sarki, ai sai da ya yi faɗa da sarkin Zamfara na
lokacin kuma yaci ƙarfinsa. A kan haka sarkin zamfara na lokacin
kuma yaci ƙarfin sa. A kan haka ne kuma sarkin zamfara ya
yi ƙudirin
halakashi, amma sai yayarsa ta dawo da shi ƙasar
mahaifiyarsu watau Gobir, a haka kuma har ya zama Sarki (watau yayi gado ta
wajen uwa). Babari ya roƙi sarkin Gobir ya bashi wuri a yankin Zamfara
inda zai zauna, amma sai aka gargaɗi sarkin Zamfara da cewa kul ya
baiwa Babari gurin zama domin nan gaba zai iya mamaye Zamfara dukan lamari daga
bisani hakan ne ya faru, da yaƙi ya ɓarke a
wajajen ƙarni na 16 zuwa na 17, sai da Gobirawa suka
cinye har Alƙalawa da yaƙi. (abinda
ke nufin inda suke zaune a yau asali ƙasar zamfara
ce).
Makaɗa Sa’idu
Maidaji Sabon birni ya ambaci wannan a waƙarsa inda
yake cewa:
Jagora: Alƙalawa ba
garinku ce ba
Alƙalin Anka
Kunka iske,
‘Yan amshi: Da kunka kasha shi kunka gadi birni.
(Sa’idu
Mai daji Sabon birni: Bachiri Ɗan Baraya)
Sarkin Gobir Abdul’hamid ya ƙara da cewa
“ A lokacin sarkin Gobir Bawa Jangwarzo (ƙarni na 17),
an ruwaito cewa ko zakaru basa cara sabida ƙarfin
tsafinsa, kuma a duk yaƙe-yaƙen da suka
yi, Gobirawa basu taɓa miƙa wuya ba,
shi ya sa ake musu kirari da Gobir ɗiyan faɗa”. Sarkin
yace “ Bawa Jangwarzo bai taɓa yaƙi da Shehu
Usmanu ba. A zamanin jihadin, maganar gaskiya ita ce Shehu ya koyar da ‘ya’yan
Bawa, ciki har da su Yumfa a samu rarrabuwar kawuna a tsakanin su.
Sarkin ya ce “mutanen da ke kusa da
Bawa su ne suka haɗa ƙiyayya a
tsakanin su, wanda ya yi silar Shehu yabar Alƙalawa, daga
baya kuma ya cigaba da jihadi a sassan Sokoto. Dangane da tsagun Gobirawa,
sarkin yace asali basu da tsagu a fuska, amma sabili da yaƙe- yaƙe ne yasa
suka rinƙa tashi daga nan zuwa can, don haka suka ɓullo da
tsagu domin su rinƙa shaida junansu.
Bayan kammaluwar yaƙe-yaƙe, daulolin
Gobir da Kabi su suka yi saura waɗanda suka cigaba da mulkinsu da
gudanar da al’adunsu, walwalarsu da ɗiyaucinsu. A idon manazarta tarihi
da al’ada daular Gobir daɗaɗiyar daula
ce mai tushe daga Gabas. Daga cikin waɗannan daulolin na Gobir da Kabi babu
ɗaya daga
cikinsu da ke iƙirarin a wannan ƙasar ta
tsira. Masana tarihi suna ganin a nan suka tsira, sai dai ba a rasa ɗan surkin
waje, Adamu (2010).
Daular Gobir da takwararta Kabi ne
kaɗai guguwar
jihadin Shehu Ɗanfodiyo ba ta shafe wa tarihin masarautunsu ba.
Abin nufi a nan shi ne, masarautunsu sun ci gaba da karɓa sunan
daulolinsu misalign sarkin kabin Argungu da sarkin Gobir na Sabon Birni, wannan
har yau bai gurɓata ba a
kundin tarihi.
Tsagen Fuska
Tsagen fuska
wata alama ce ta gane dangin juna, da farko-farko Gobirawa bas u da shi sai
daga baya a sakamakon yaƙa-yaƙe sai
Gobirawan suka fara yinsa domin su gane danginsu Jeanboyed (1979). Tsagen
Gobirawa tsage ne wanda ya cike masu fuskarsu cif, kuma wannan wata alama ce ta
cewa su gwaraza ne waɗanda ba su
jin tsoron wahala kowace iri ce. A wani ƙauli kuma an
ce tsagen Gobirawa ya kasu kashi biyu ɗaya na sarakuna ne ɗaya kuma na
waɗanda ba
sarakuna ba. Ga bayaninsu kamar haka:
1. Tsagen
Nan shidda nan Bakwai: shi wannan nau’in tsagen Gobirawa shi ne wanda ake yinsa
a gefe gefen kumatu,
Bunƙasar Daular
Gobir
Garin Alƙalawa a
cikin tarihi garin Zamfarawa ne, kodayake Gobirawa sun ci su da yaƙi sun
ragargaza su sun ƙwace garin, Gobirawa ba su daina hulɗa da
Zamfarawan da suka tarwatsa ba tun a wancan lokacin da yaƙi ya ɗaiɗaita su.
Bayan ragargajewar da Gobirawa suka yi wa Alƙalawa sarkin
Gobir Babari ya sake gina garin inda ya zama garin Gobirawa. Sarkin Gobir wanda
ya shahara bayan Babari shi ne sarkin Gobir Bawa Jan Gwarzo. Bawa wani irin
jarumi ne na gaske ya ƙarfafa daular Gobir ƙwarai da
gaske, ya shimfiɗa
sarautunsa, shi ne na farko sarkin da ya ƙi bada
haraji ga sarkin Borno wanda sauran sarakuna ƙasar Hausa
suke bayarwa, a cewarsa shi ɗa ne ba bawa ba, har ma ya yaƙi ƙasar Zamfara
ya kuma rusa ta. Sarakuna da dama suna tsoron faɗa wa daular Gobir domin gudun
kar ta yaƙe su ta rugurguza su, wannan ne ma ya sa waɗansu
daulolin sukan aika wa sarkin da wasu kyaututtuka don kamun ƙafa. Misali
sarkin Nupe ya aika wa sarkin Gobir da gaisuwa tare da kyautar bayi mata ɗari biyar da
maza ɗari biyar
kowane daga cikinsu yana ɗauke da kuɗi wuri dubu
ashirin. Shi kuma Bawa ya ji daɗin wannan ya aika masa da kyauta wadda ta lunka
tasa don ya aika masa da dawaki masu yawa ingarmu na azbin kuma ya aika masa da
bayi mata biyu masu kyawon gaske, Jean Boyd (1979).
A lokacin Bawa jan gwarzo ne Shehu
Usmanu Ɗanfodiyo ya fara yin wa’azin muslunci a ƙasar Gobir a
lokacin yana ɗan shekara
talatin da huɗu (34),
Sarkin Gobir Bawa Jan Gwarzo ya yi
shirin yaƙar Katsina a wani lokaci amma sai ya juya yaƙin zuwa Maraɗi kuma ya ci
Maraɗin da yaƙi. Bayan
ciye maraɗi da yaƙi sai ya ƙara ƙarfafa buƙatarsa ta
kai yaƙi Katsina don ya cinye su da yaƙin. A wannan
lokacin sai sarkin Katsina ya aiko masa da kyauta ta lallashinsa, amma dai yaƙi jin
lallashin said a suka gwabza yakin a wani wuri da ake kira Dankeci! Wannan yaƙin mai
tsanani ne wanda har tsananin bai misaltuwa, a nan ne aka kasha ɗan sarkin
Gobir Bawa mai suna Ɗan Abu, wannan mutuwar ta sa Bawa baƙin ciki matuƙa.
Sarkin Gobir Bawa ya shahara matuƙa kuma
jama’a suna gimama shi saboda kwarjininsa har suna cewa:
A zamaninsa
* Gara bata cin kayan mutane
* Ƙishirwa bata
kashin mutum,
* Doki ba shi haniniya,
* Maciji ba shi saran mutum,
* Kunama ba ta cizon mutum,
Har an ce wata rana ya taɓa yi wa daji
shela ya ce ko dabaibayin jaki ya koma ɓacewa a cikinsa to zai mayar da shi
karkara.
Rashin Ɗaukar Reni
Gobirawa mutane ne waɗanda ba su
cika ɗaukar reni
ba, suna da saurin fushi da mayar da martini, don haka ne ma suke wasu iri
mutane masu ƙoƙari wajen
neman abin kansu ta hanyar yin sana’a komai wahalar ta. Makaɗa Sa’idu
Maidaji Sabon Birni a waƙarsa ya bayyana Gobirawa a matsayin masu baƙar zuciya
inda yake cewa:
Jagora: Gobirawa kun sha kunun bakar zucciya
‘Yan amshi: Nan cikin duniya babu inda ba a san ku ba.
(Sa’idu Maidaji Sabon Birni: Sarkin Bazai)
Gobirawa sanannun mutane ne a duniya
bakiɗayanta, mafaɗata ne masu
tsare gaskiya ne masu gudun yin abin kunya ta kowane hali, sukan ba duk wata
hulɗa da ke iya
zubar musu da mutunci baya duk abin da ake samu a cikinta, suna kuma iya yin
hakuri da kowane irn hali suka shiga a ciki don kar a rena su.
Gobirawa A Zamfara
Gobirawa sun
sami ɗaukaka a
duniya tun lokacin yaƙe-yaƙen sarakuna,
har ma kawowa yanzu, kowane sarki yana son ya ƙulla alaƙa da sarkin
Gobir domin irin girmansu a duniya, sarkin Gobir bawa Jan gwarzo ya naɗa sarkuna a
cikin wasu garuruwan yankin Zamfara misali a garin Bunguɗu wani
Bafulatani ne makiyayi wanda ke da tarin dabbobi mazaunin wurin ya je ya kai
mubayi’a ga sarkin Gobir Bawa Jan Gwarzo, sai Bawa ya tambaya wane ne ya zo aka
ce wani Bafulatani ne, sai Bawa ya ce sarkin Fulani dai, daga nan ne sarkin
Fulani Muhammadu Zundumi ya sami sarautar garin.
Gobirawa a yankin Zamfara mutane ne
masu matuƙar muhimmanci, kusan kowane gari a cikin yankin
Zamfara akwai Gobirawa, a wasu wuraren ma su ne suke mamaye wurin kuma dukan hulɗoɗin yau da
kullum ana yinsu tare da su, babu wata damuwa a halin yanzu.
A wasu manyan garuruwa ma Gobirawa
suna da sarauta inda suke gudanar da mulkinsu babu wata ja in ja tsakaninsu da
sauran jama’a.
Alaƙar Gobirawa
Da Zamfarawa
Gabatarwa
Mafi yawan
mutane suna sauraren waƙa domin daɗinta ne, wato don nishaɗin da take
samarwa, amma dai su manazarta tare da wasu kaɗan daga cikin jama’a na
lalaben tsokokin da ke cikin waƙa ne domin su amfana da su
wajen magance wasu matsaloli daban-daban. Akwai abubuwan hikimomi birjik a
cikin waƙoƙin Shata
masu jan hankalin manazarta, waɗanda su ba lallai nishaɗi kurum suke
samarwa ba, waɗanda kuma
manazartan kan mayar da hankalisu a kansu, su yi aikin fitowa da su don sauran
jama’a su amfana da su. Waɗannan abubuwan sun shafi jigogi da salo iri- iri
da sauran abubuwan da shi dai mawaƙin bai fito ɓaro-ɓaro ya nuna
su ba a waƙoƙinsa, ko
kuma kamar a ce ba su san sun yi irinsu ba a waƙoƙin nasu, sai
dai kowa yake da sha’awar zaƙulo irinsu ya tsunduma a
cikin waƙoƙin don tsamo
su tare da nuna su ga kowa da kowa. Ni ma a wannan sha’anin hankalina ya
karkata a kan salon koɗa kai wanda
yakan fito a cikin bakandamiyar Shata (Mahadi mai dogon zamani) shahararren
mawaƙin ƙasar Hausa
wanda ya fi gaban a tozarta shi ko garin da
ba a da Hausa.
Gobirawac
Chali - Maru
Gobirawar
Halbau - Maru
Gobirawar
Mal. Inusa - Maru
Gobirawa wajen Bilbis rikon Faskari
Gobirawar
Mai Fulani – Magami Gusau
Gobirawa
Sokoto
Gidan
Gobirawa Zurmi
Gobirawar
Tudub Doka
s/ Gobir
Suru
S/ Gobir
Kalgo
Tudun wada
Argungu akwai Gobirawa
Sabon Garin
Biyabiki duk Gobirawa ne
Gidan
Gobirawa – Wajen Hayin Alhaji
Tungar
Gobirawa – kafin Kwaren Shinkafi
Gobirawa
Hanyar Badarawa
Taƙaitaccen
Tarihin Shata
Mahaifin Shata an ace masa Ibrahim
Yaro Raruma; Bafullatani ɗan asalin
garin Sanyinna ne ta ƙasar Sakkwato. Iyayensa sun baro garin su ne
(Sanyinna) suka doso gabas don neman makiyaya don yin kiyon dabbobinsu, sai aka
haife shi a can. Sunan mahaifiyar Shata Lariya kuma ‘yar Fulata – Borno ce.
Wajajen shekarar dubu ɗaya da ɗari takwas
da goma 1810, a lokacin da ake cikin gwagwarmayar jihadin Shehu Ɗanfodiyo
iyayenta suka taso suka zauna a Tofar Ɗan’adala ta
cikin jihar Kano inda ta zauna tana aiki a gidan sarkin garin. Daga baya sai ta
ƙulle
kayanta ta koma ingawa ta ƙasar Katsina wajen Dije matar
Sarkin ingawar, ta auri wani mahauci ta haifi ‘ya’ya biyu maza. Da aurensu ya
mutu sai ta koma musawa wajen matar sarkin, sai soyayya ta haɗa su da
Ibrahim yaro Raruma, wato mahaifin Shata. An haifi Shata a shekarar 1923 a
lokacin sallah babba, Shata ne ɗan farin ga mahaifinsa amma dai su uku ga
mahaifiyarsu, na farko shi ne Ali na biyu kuwa Muhammadu Lawal wato Shata ke
nan, sai autarsu Yelwa (Amina).
Maroƙin Shata
kandanganta shi da wani sahabin manzon Allah mai suna Sasana a cikin kirarinsa.
Ana ganin ita waƙa ta samo asali ne daga shi wannan mutum Sasana
wanda shi wani mawaƙi ne a zamanin Jahiliya a Madina, wanda ya
musulunta daga baya. To da ya karɓi Musulunci sai ya zama mawaƙin Annabi
Muhammadu (SAW). To wai zuriyar wannan sahabi ne suka watsu cikin duniya suna
waƙa
har Allah ya karkato da su ƙasar Hausa inda aka sami
Alhaji Mamman Shata cikin tsatson wannan Sahabin (Sasana) Abba da Zulyadaini
(2000:3)
Shata ya fara waƙar Asauwara
tun a wajen shekarar 1920 – 1940 kuma ya yi fice sosai. Ya zama cikakken mawaƙi sananne
kuma karɓɓe a ƙasar Hausa
har ma ya sami nasarar yin waƙoƙI da yawa,
da har shi bai sanyawansu ba. Allah ya karɓi ran Shata a ranar Juma’a 18 ga
watan Yuni 1999 da misalin ƙarfe 12:30 na dare, Allah ya
jiƙansa
da rahamarsa, amin.
Ma’anar Salo
Malamai da masana sun bayar da
ma’anar salo ta hanyoyi daban – daban duk da yake abu ɗaya suka
fuskanta.
Sa’idu Muh’d
Gusau a tashi fahimtar ya ce:
“Salo shi ne hanyar da aka bi aka
nuna gwaninta da dabaru a cikin furuci ko rubutu.
Kuma yana nuna yadda mutum ya shiya wani abu ta bin yanayin harshensa da zaɓar abubuwa
da suka dace game da abin da yake son bayyanawa. Daga nan ne za a fahimci salon mai sauƙi ne ko
tsauri, mai tsauri ko mai daɗi ne da
armashi ko mai kasha jiki maras karsashi da sauransu” Gusau (1993:54).
Yahya kuwa
ya ce:
“Salo dabara ce ko hanya mai yin
kwalliya ga abu domin abin ya kwarzanta ko ya bayyana” Yahya (1999:28)
Shi kuma Ɗangambo cewa
ya yi:
“Masana da manarzarta suna ganin
cewa Salo yana da wuyar a gane shi a bisa kansa sai dai ana iya gane wasu
sigogi nasa, dangane da ma’anarsa. To amma muna iya cewa salo shi ne hanyoyin
isar da saƙo “, Ɗangambo,
(2007:34)
A bisa ra’ayin Abdulƙadir Ɗangambo yana
cewa: za a iya karkasa salo kamar haka;
1.
Salo wani ƙari ne da ya ƙunshi zaɓi cikin
rubutu ko furuci.
2.
Salo wani ƙari ne na daraja a cikin karatu ko furuci wanda
ba lalle ne a same shi cikin kowane rubutu ba.
3. Salo ya shafi kauce ma wata
daidaitacciyar ƙa’ida.
4. Salo harshen wani mutum ne, wato
yadda salon wane ya bambanta da na wane.
Haka kuma ya
cigaba da bayyana mana cewa salo yana da nau’o’i har guda biyar,
a.
Miƙaƙen salo:
Wato salon a kai tsaye mai sauƙin ganewa, wannan salo yana
iya zama kamili mai iya isar da saƙo ba tare da
“ado” ko ƙaƙale ba.
b.
Salo
mai armashi ko mai karsashi: Shi ne salon da ya gamsar ta hanyar karsashi, ƙaƙale da
burgewa.
c.
Raggon
salo: Shi ne salo mai kashe jiki kuma marar gamsarwa.
d.
Tsohon
salo/sabon salo: Salon da ke yin amfani da tsofaffin hanyoyi ko sababi don isar
da saƙo, yana iya zama mai gamsarwa ko akasin haka.
e.
Salo
mai sarƙaƙiya ko mai
tsauri. Shi ne salo mai wahalar ganewa saboda tsaurin saƙar manufofi
ko tsauraran kalmomi.
Wani
manazarcin na ganin cewa:
“Salo shi ne yadda mawaƙi ya zana
tunanensa a takarda, za a dube shi a gain shin yana
da manufa, kuma bayaninsa yana da ƙarfi ko
raunana ne ana fahimtarsa cikin
sauƙi
ko kuma sai an yi lalabe kafin a gane manufarsa.(Bashir 2007:21).
Shi kuma Sarɓi cewa ya
yi:
“Salon na
nufin zaɓi cikin
gudanar da wani abu/aiki. Amma fagen nazarin waƙa salo hanya
ce da marubutan waƙoƙi ke bi
wajen isar da saƙonsu ga jama’a” (Sarɓi,2007:11).
A tawa fahimtar, na lura da dukkan
bayanan da waɗannan masana
da manazarta suka kawo suna nufin salo ya ƙunshi hanya
ko hanyoyin da mawaƙi ke bi domin isar da saƙonsa ga
jama’a.
Bakandamiyar Shata
Bakandamiyar wata waƙa ce wadda
Shata yake yi a lokutta da wuraren waƙarsa daban-
daban, wadda yafi maimaita ta fiye da dukkan waƙoƙinsa saboda
jin daɗin tad a
yake yi. Wannan waƙar ita ce tamkar uwar waƙoƙin Shata.
Ma’anar Bakandamiya
Shata ya bayyanar da ma’anar
bakandamiya da kansa a wata hira da suka yi da Adamu Yusuf wani wakilin gidan
rediyon BBC a shekarar 1996, yace bakandamiya ita ce a kandamo komai da komai,
ba a bar kowa dakomai ba, kowa za a ambata komai za a ambata”. Abin nufi dai
anan Shata yana yin komai yaga dama a cikin waƙar, duk abin
da yake son faɗi yak an faɗe shi ne ba
tare da wata shakka ba.
Bakandamiya waƙa ce da
Shata ya yi ma kansa ba wani ya yi wa ita ba, don haka ya fi jin daɗinta da
kowace waƙarsa.
Alhaji Mamman Shata ya fara
yin wannan waƙa ne a wajajen ƙarshen
shekarar 1950 inda yake yabon Sarkin Zamfaran Zurmi Sule, a wancan lokacin
amshinta amshin waƙar shi ne:
Uhm
Uhm Uhm Uhm mai ganga ya gode yaran mai ganga sun gode,
sai daga
baya ne suka riƙa cewa a cikin amshin:
Alo-alo
mai ganga ya gode yaran mai ganga sun gode.
Ya ɗauki tsawon
lokaci yana maimata bakandamiyar kamar yadda take ba tare da wani ƙari ko ragi
ba, sai daga baya ya riƙa sasauya ta a sakamakon samun sababbin iyayen
gida da kuma waɗansu ƙalubalen
rayuwa da ya samu kamar na abokan adawa da sauransu. Misali a shekarar 1960
sababbin baitocin sun fito a cikin waƙar kamar
haka:
Jagora: Ai
yau duk wani mai yin sallah,
Duk
wani mai yin addini,
Kun san babu ya Manzon Allah,
Duk wani wanda yake kafirci,
Duk mai yin saɓon Allah,
Kun san babu ya Fir’auna,
A’a to ashe haka duk wanda ke yin waƙa,
Yara bai yi kamar Shata ba.
‘Yan amshi: Alo
alo mai ganga ya gode, yaran mai ganga sun gode.
Samun nasarar Shata ta fanning waƙa ya janyo
rashin jin daɗI ga wasu
mawaƙan Hausa waɗanda suka riƙa
hassadarsa, sai shi kuma ya yi amfani da Bakandamiya don ya sosa ma kansa duk
inda ke yi masa ƙaiƙai, dibi yadda
yake cewa:
Jagora: Na gane banjo da kukuma,
Wargin
yara ne,
‘Yan amshi: Alo alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode,
Jagora: Su ci abinci kowane yai shakwara
yai jamfa,
‘Yan amshi: Alo alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode,
Jagora: Kowa ya sani kurɗi yai auren
zamani,
‘Yan amshi: Alo alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode,
Mawaƙin ya ɓarje guminsa
a nan domin ya nuna cewa wasu mawaƙan ma saboda
irin tasirin Shata har hana su yin waƙar ya yi!
Wasu kuma day a ɗauka ƙananan
alhaki sai ya bar su don su ɗan sami ‘yan kuɗin yin wasu hidimominsu
saboda ba su tsone masa ido ba. Yin haka Shata koɗa kansa ne ya yi domin nuna
babu wani day a kai shi a fagen waƙa balle ma
ya fi shi.
A wata da Abdul Umar Faruk na gidan
rediyon freedom FM na Kano ya yi da wani ɗaya daga cikin marubucin sanannan
littafin nan wato Shata ikon Allah, a ranar laraba 31/03/2010 da misalign ƙarfe goma sha
ɗaya da kwata
na dare, Dr. Aliyu Ibrahim Ƙanƙara, a cikin
shirin zaɓi da kanka,
inda ya nuna cewa bakandamiya ta karkasu sama da kashi tamanin dangane da
nau’o’inta. Bayan sauye – sauyen da bakandamiya ta samu a lokuta da wurare
daban – daban, saboda dalilai daban – daban, an samu sananniyya kuma karɓarɓiyar
bakandamiyar a shekarar 1972. Wannan Waƙar ce za a
yi amfani da ita a wannan takarda don a fito da ingantattun bayanan da a ke son
fitar wa jama’a.
Salon Koɗa Kai
Kalmar koɗa dai ta
nufin sake kaifafa wani abu da ya dallashe. Duk abin da aka koɗa ana
tunanin cewa ya wuce wani ko wasu waɗanda ba a koɗa ba (dallasassu). Misali a cikin kayayyakin aikin
gona irin su fartanya da galma da kwashe (magirbi) da gatari duk ana koɗa su ne idan
sun daulashe don a fi jin daɗin aiki da su. Haka kuma idan an ga mutum yana wani kuri akan ce ya
cika kaifi, ko bugun gaba (alfahari) da sauransu.
Salon koɗa kai wani
salo ne da mawaƙa ke amfani
da shi a cikin waƙa inda sukan koɗa kansu domin su isar da saƙo ga jama’a.
A cikin wannan salo mawaƙa kan yabi kansu ne har sukan kushe danginsu
mawaƙan domin su nuna sun fi su shahara. Haka kuma
salon koɗa kai wasu
suna ɗaukarsa a
matsayin salon sheƙe ayar da mawaƙa kan yi a
cikin waƙoƙinsu domin
su nuna babu mai iya ja da su. Alhaji Musa Ɗankwairo a
cikin waƙarsa ya ce:
Jagora: Duk makaɗin da at tcahe na jami’i
‘yan amshi: Babu mai shirya waƙa kamat tawa
Jagora:
Ga makaɗi ya shiya
waƙa
tai,
Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
In
niƙ
ƙulla
waƙa
a ƙara
man,
Mu
huɗu duk azanci
garemu,
‘yan amshi: Ka ga mutum
guda ba ya rabje mu,
(Alhaji Musa Ɗankwairo:
shirya kayan faɗa)
Haka kuma wasu mawƙan sun
amfani da wannan salo zuwa ga wasu da suke yi wa waƙarsu, idan
kaji su zaka fahimci cewa ba yabo ba ne ko kambame, domin su wani ake yi wa.
Idan mawaƙi ya faɗi abubuwan da ke yiyuwa a kan wani
ya yi yabo kenan. Idan kuwa ya faɗi abin da bai yiyuwa shi ne kambamar
zulaƙe. Misali:
Garba Ɗandiga ya
kambama matarsa a cikin waƙarsa kamar haka:
“Malunƙui uwar
daka,
Ba mace
mai daka irin ta gidana.”
(Garba Ɗandiga: Malunƙui uwar
daka)
Ko a cikin harkokin mu na yau da
kullum idan mutum ya riƙa yabon kansa da kansa, akan ce yana koɗa kansa ne,
haka kuma idan ya haɗa yabon
kansa da kushe waninsa sai ace ya faye koɗa kansa.
Alhaji Mamman Shata a farko farkon
bakandamiyarsa ya siffanta kansa da wasu abubuwa masu ban tsoro don ya koɗa kansa.
Dubi yadda yake cewa:
Jagora: Gwauron giwa mai ban tsoro na Habu ɗan Ibrahim
Kyalkeci mai wawar kora ɗan Yaro.
Zaki
mai tarin ƙarfi ɗan Iro,
--------------------------------------
‘Yan amshi: Alo –alo mai
ganga ya gode yaran mai ganga ya gode.
Da farko dai ya koɗa kansa ne
ta hanyar kamanta kansa da manyan dabbobi kamar su giwa da zaki da kyalkeci,
kasancewar waɗannan
dabbobin ba abin wasa ba ne, kuma babu wata dabbar da ke iya ja da su. A nan
salon koɗa kan da
mawaƙin ya yi amfani da shi ya isar da saƙo ga mawaƙan da kuma
sauran jama’a, cewa shi fa ruwa ba sa’ar kwando ba ne” don haka duk mai niyyar
ja da shi ya fasa.
A wani wuri kuma Shata yana cewa:
Jagora: Idan
na fara Bakandamiya,
Ji nake kamar malami gwanin tafsiri,
Am malamin amma fa gwanin,
Aja baƙi ya fasa,
Ba
tare da jin tsoro ba,
Don ba a gwaninta da tsoro malan,
Mai tsoro ba shi gwaninta ko wane ne kuma ko ɗan wa,
Allah kau, ma tsoraci ba shi zama gwani ko
wane ne,
To! to!! to!!!.
‘Yan amshi: Alo – alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode.
Mawaƙin a cikin
wannan ɗan waƙar koɗa kansa ne
ya yi domin kowa ya san irin wannan kwatanci da ya yi na gogaggen malami gwanin
tafsiri a fagen tafsiri babu maganar tsoro ko shakkun wani abu, wannan yana
nuna cewa wannan salo na Shata ya isar da saƙon kashedi
ga sauran mawaƙa ta hanyar koɗa kansa da ya yi wajen nuna
cewa shi ba kanwar lasa ba ne.
A wani wuri kuma ya koɗa kansa inda
yake cewa:
Jagora: Matsoraci ba shi zama gwani ko wane ne,
Ka
zama kamar ni filin waƙa,
Sararin waƙa bai san tsoro ba in ni fito Shata ne,
Kun
san shi,
Ya san
ku,
Sai ƙaƙa?
Iye?
‘Yan
amshi: Alo – alo mai ganga ya gode
yaran mai ganga sun gode.
A nan ma saƙon da ke
ciki salon koɗa kan shi
ne: yadda Shata ke nuna bai tsoro
musamman a fagen waƙa har ma yake nuna duk wanda
ya zama kamar shi a filin waƙa ya shahara, wato duk wanda
ya zama kamar Shata a filin waƙa ya wuce ya zama matsoraci.
Haka nan Shata yana cewa a cikin
Bakandamiyarsa:
Jagora: Gurnanin
damisa karen gida ke gudu,
Karen ko na wane ne,
Ko wace karya tah haihwai,
Ɗan kusun
uwa?
Wa ne aura?
To, to, to,
‘Yan amshi: Alo – alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode.
Mawaƙin a nan ya
koɗa kansa ne
da mayar da kansa damisa wadda ƙananan dabbobi ke tsoron
gurnaninta kamar karen gida da sauran irinsa. Su kuma sauran ƙananan
dabbobi su ne a matsayin karen gida. Wato dai Shata ya ɗauki
matsayin mutum wanda sauran mawaƙa ke tsoro,
kamar yadda karen gida ke gudu idan ya ji gurnanin damisa.
Haka kuma Shata ya koɗa kansa inda
yake cewa:
Jagora: Allah
ya yarda,
Yo ai har yau ni ke yi,
Ku kau baku samo canji nab a,
Balle in zauna!
Wai har in ce zan huta,
Ku taya mani ku ‘ya’yana,
Har yau dai ni ke yi,
Allah ya yarda!
Yardar Allah ta fit a kowa na habu Ɗan Ibrahim
Kelkeci mai wawar kora ɗan Yaro,
To, to, to!
‘Yan amshi: Alo – alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode.
A
nan ya tabbatar ma mawaƙa da cewa tun daɗewa babu kamarsa kuma daga
cikinsu babu wani mai iya canjin sa a fagen waƙa, domin shi
Allah ya riga ya yarda da al’amarinsa, daga ƙarshen ɗan waƙar ma ya
siffanta kansa da kelkeci da irin yadda yake korar dabbobi idan zai kama su.
A wani wurin kuma Shata ya koɗa kansa inda
ya ce:
Jagora: Faɗa wa
mutanena:
Kowar rasa Shata ya yi asarar waƙa!
Kowar rasa ni bai sha waƙa ba ko wane
ne,
Kuma ko ɗan wa,
Allah kau!
‘Yan amshi: Alo – alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode.
Wato
a nan mawaƙin na nuna cewa kamar waƙarsa kaɗaice waƙa, domin a
cewarsa duk wanda bai ji waƙar Shata ba to sam bai
saurari waƙa ba! Duk sauran waƙoƙin mawaƙa tamkar
wani shirme ne ba waƙa ba.
Haka kuma mawaƙin ya ce:
Jagora: Kowa
ya ja zare,
Idan ka iske ya tsunke,
Ba ka ja daidai ba!
‘Yan amshi: Alo – alo mai ganga ya gode yaran mai ganga
sun gode.
Jagora: yau
shekaru da yawa zarena nike ja,
Bai taɓa tsunke man ba!
‘Yan amshi: Alo – alo mai ganga ya gode yaran mai
ganga sun gode.
A waɗannan ɗiyan waƙar, Shata ya
koɗa kansa ne
ta hanyar nuna irin dogon lokacin da ya ɗauka yana tafiyar da harkokin waƙarsa lafiya ƙalau ba tare
da samun wata matsala ba, wato shi bai taɓa samun wani cikas ba kamar yadda
sauran mawaƙan suke samu, har ya faɗi cewa duk
wanda ya sami cikas a cikin lamarinsa sai in bai iya tafiyar da shi kamar yadda
ya kamata ba.
A wani wurin kuma Alhaji
Mamman Shata ya ce:
Jagora:
Da makaɗa da mawaƙa da maroƙa suna tsoro
na na gane,
Ciji inji yara!
Abin
tsoro ni!
Sun san ni,
Shata ne,
Sai ƙaƙa,
Iye?
To,
‘Yan
amshi: Alo – alo mai ganga ya gode
yaran mai ganga sun gode.
A nan Shata ya fito ƙarara ya
nuna ma makaɗa da mawaƙa shi fa
abin tsoro ne, kuma ya fahimci cewa suna tsoronsa kamar yadda yara suke tsoron
ciji. Wannan salon koɗa kai ne ya
yi amfani da shi don kuwa ai ba haka mawaƙan suke
tsoron sa ba tun da har suke haɗuwa waje guda, kowa ya fahimci halinsa wasu daga
cikin su har biyayya yake yi masu, domin an ce sai ya durƙusa idan zai
yi gaisuwa ga wasu manyan makaɗa kamar Alhaji Ibrahim Narambaɗa.
Shata ya faɗa wa mawaƙa cewa ya
karɓe waƙa koda yake
bai gade ta ba:
Jagora: Roƙo shigar shi
nai,
Na shige shi duk na gagari
‘ya ‘yan gado,
Suna gain na na gagara!
Abin nan kau nasu ne, na
amsa,
Sun yarda,
Ko don tilas,
Allah kau,
Da dole ciki.
‘Yan
amshi: Alo – alo mai ganga ya gode yaran mai ganga sun gode.
Kammalawa
Shata ya koɗa kansa matuƙa a cikin
Bakandamiya a wurare da dama, waɗanda da makaɗa da mawaƙa da maroƙa har ma da mu
manazarta mun gane hanyoyin day a bi domin koɗa kansa. Misali a cikin
bakandamiyar ya danganta kansa da manya – manyan dabbobin da sauran dabbobi ke
tsoro, har ma yake nuni da cewa shi abin tsoro ne (ciji) kamar yadda yara suke
kiran duk wani abin tsoron. Wannan
takardar dai ta fito da wannan salon ƙarara domin
amfanin manazarta a lokacin nazarinsu. Salon koɗa kai kamr yadda aka kalle shi
a cikin wannan takarda, ba wani sabon salo ba ne wanda aka ƙirƙira a wannan
lokaci, salo ne wanda ya danganci yabo da kuma kambamawa ko zuga. Amma dai sun
sha bamban domin a cikin sa waɗansu kalaman sun wuce yabo, saboda waɗansu kalaman
da an ji suna tsoratarwa ne da mawaƙi kan auno
su ya zubo cikin waƙa don ya
isar da saƙonsa, shi kuma kambame akan yi shi ne zuwa ga
wani ba shi mutum ya yi wa kansa ba. To a wannan takarda an nuna duk lokacin da
mawaƙi ya kambama kansa to ya yi amfani ne da salon
koɗa kai.
Manazarta
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.