Kankare zunubai daga Juma'a zuwa wata Juma'ar ba ya samuwa sai ya
ciki Sharuɗɗan
da aka ambata a cikin
hadisi. Sharuɗɗan su ne kamar haka:
Samun
Gafarar Zunubai na Kwana Goma a Ranar Juma'a
Abu
Aysha
Daga Salmanal Farisy رَضِيَ
اللَّهُ عَنْهُ,
yace;Manzon Allah SAW yace;
(Babu wani mutum da zaiyi wanka ranar juma'a
kuma ya tsarkaka gwargwadon iko na tsarkinsa, kuma ya shafa mai daga mansa, kuma
ya sanya turare, sannan ya fita zuwa masallaci, bai ƙetara tsakanin
mutum biyu ba, sannan ya sallaci abinda aka wajabta masa, sannan yayi shiru a
lokacin da Liman yake Huɗuba,
face an gafarta masa tsakanin wannan juma'ar zuwa wata juma'ar)
@صحيح
البخاري-رقم:(883).
A wata riwar acikin Saheehu Musulim;
(. . . . . Da karin kwana ukku. . . . )
@صحيح
مسلم
ابن حجر
رَحِمَهُ اللهُ
تَعَالَى:-
Yana cewa;
Kankare zunubai daga Juma'a zuwa wata Juma'ar ba ya samuwa sai ya
ciki Sharuɗɗan
da aka ambata a cikin
hadisi. Sharuɗɗan su ne kamar haka:
Yin wankan Juma'a
Yin tsafta da gyaran jiki da tufafi
Sanya turare mai dadin ƙamshi da shafa mai
Sanya tufafi mai kyau
Tafiya masallaci cikin nutsuwa
Kada ka ƙetara tsakanin
mutum biyu
Kamewa daga chutar da wani
Kuma kayi nafilar gaisuwar masallaci
Kuma ka yi shiru ka saurari huɗuba
Kuma ka baryin Lagwu lokacin huɗuba
Ka fuskanci Liman lokacin da yake Huɗuba
@فتح
الباري:(372/2)
Allah ne
mafi sani
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.