Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami'ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Nijeriya
NA
SHEHU MUHAMMAD TAFIDA
BABI NA HUDU; Takaitawa Da Kammalawa
4.0 SHIMFI’DA
A cikin wannan babin na hud’u kuma na k’arshe ne aka kawo tak’aitattun bayanai dangane da aikin da aka yi nazarinsa, Daga shi sai jawabin kammalawa, da k’arshe aka rufe babin da shawarwari.
4.1 TAK’AITAWA
Komai nisan jifa, ance k’asa za ta fad’o. Kamar yadda aka fara wannan aikin ga shi Allah ya kawo k’arshensa. Kamar yadda aka fad’a a baya, an yi nazarin wannan aikin ne a kan zaman gandu musamman a garin Zazzau.
Saboda haka ne ya sa aka tsara binciken ya zuwa babuka hud’u , domin samun sauk’in fahimtarsa. A babi na farko an fi mai da hankali ne ga ayyukan magabata inda suka maganta dangane da zamantakewar iyali a k’asar Hausa. sai dalilin bincike, inda aka nuna cewa anyi shi ne domin zak’ulo wasu muhimman abubuwa da ta yiwu ba a kain gare su ba, ko ba a tsara su yadda ya dace ba. Yayin da farfajiyar binciken ta bayyana yadda Zagi- zage ke kula da rayuwar iyalinsu ko zuriyarsu don ba da gudumuwa ga duk wata al’uma da ba ta da irin wannan fasali da tsari na kula da zuriya. A mahimmacin bincike kuwa aka ce saboda kulla zumunci da kare zuriya daga gurbata daga wata mummunar al’ada. Daga nan sa hanyoyin gudanar da bincike inda aka nuna cewa anbi diddigin ayyukan da suka gabata, musamman wad’anda suka shafi al’adar zamantakewar al’uma.
A babi na biyu kuwa nan ne aka kawo ma’anar kalmar zama, kamar yadda masana suka kalli kalmar haka kuma sun ba da ma’anar gandu bisa ra’ayoyin. Inda aka bayyana ma’anar kalmomin da cewa; zaman tare na zuriya ko al’umma da suke k’ark’ashin jagorancin mutum d’aya, a matsayin shugabansu. Sai zamantakewar Bahaushe da iyalansa, inda aka nuna yadda maigida yake zaune da ‘ya’yansa da jikoki, da tatta’ba kunne, a k’ark’ashin jagorancinsa. Daga nan sai yanayin zamantakewar gargajiya, inda a nan ne aka nuna ingancin da zamantakewar ke d’auke da shi, an bayyaa yadda fasalin zama yake da kuma ire-iren yanayin rayuwa. Kamar jaruntaka da d’a’a, da gaskiya, da rik’on amana, da zumunci da hak’uri a duk wanni halin rayuwa da mutum ya tsinci kansa a ciki. Sai yanayin zamantakewa na zamani, inda aka nuna cewa ; zamantakewar Hausawa ta fara sauyawa ne sakamakon shigowar bak’in Larabawa da suka zo da addinin musulunci. Bayan had’uwarsu da Larabawa sai bak’in Turawa ‘yan mulkin mallaka da suka bar mana gadon al’adunsu, da d’abi’unsu, da ma yanayin zamantakewar tasu.
A babi na uku kuwa sai aka kawo yanayin zamantakewar iyali a garin Zazzau har aka nuna yadda ake aiwatar a shi. Irin wannan zamantakewar a garin Zazzau ana kiranta zaman gandu. An kawo yadda jagoranci yake tare da ayyukan ci gaba da ake samu a zamantakewar gandu. Inda aka nuna zuriya ce kan had’a kai don gudanar da wani aiki da zai kawo wa zuriyar ci gaba. Sai zummunci da matsayinsa a zaman gandu. An bayyana shi da cewa shi ne tushen rayuwa da yake kula da taimakon juna da ayyukan ci gaba na zuriyar wanda ya shafi taimakon kai da kai ta fuskokin rayuwa. Daga shi sai kimar matan ‘yan’uwa, an nuna k’annen miji kan d’auki matan yayyensu tamkar abokan wasa (taubashi), yayin da suke yi masu ba’a da maganganun barkwanci. Amma kuma sukan d’auki matan yayyensu tamkar iyaye yayi da suke neman wani abu na rayuwa, kamar nemar aure ko neman wata shawara da ta shafi wata matsala ta rayuwa.
4.2 JAWABIN KAMMALAWA
‘Dan’Adam ko ina yake a duniya ba ya iya gudanar da zamantakewarsa shi kad’ai, wannan ne ya sa shi neman abokiyar zama, ta hanyar aure. Wannan hanya ita ce tushen kafuwar al’umma, ta irin wannan hanyar zamantakewar ne al’ummar Hausawa musamman na garin Zazzau suka k’irk’ira ma kansu, zamantakewa irin ta gandu domin samun kariya daga abokan gaba, da taimakon juna, da samar da cikakkiyar tarbiyar ga al umma.
4.3 SHAWARWARI
Saboda inganci da muhinmaci zamantakewar Hausawa tare da irin rawar da zamantakewar yake take takawa wajen tsarin shugabanci, da kula da tarbiyar iyali, da cud’anyarsu da sauran jama’a. zai yi kyau a cusa wannan a cikin manhajar karatu, tundaga firamare har zuwa ga jami’o’i. Wannan zai bai wa d’alibai damar fahimtar yadda ake gudanar da zaman tarayya tun daga gida da kuma irin rawar da al’umma kan taka.wannan zai kawo k’arshen zaman daga kai sai ‘ya’yanka, domin a koma ga tsarin zamantakewar da aka gada kaka da kakanni.
https://www.amsoshi.com/tuntubi-masu-gudanarwa/
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.