KUNDIN BINCIKEN KAMMALA KARATUN DIGIRI NA FARKO (B.A HAUSA) A SASHEN HARSUNAN NIJERIYA, JAMI’AR USMANU ‘DANFODIYO, SAKKWATO
NA
MUSA LUKMAN ALƘASIM
BABI NA UKU
3.0 Shimfiɗa
A wannan babi na uku an kawo tarihin
Birnin Yawuri a taƙaice. Bayan nan kuma an
akwo tarihin ƙabilar Kambari da
muhallin da suke zaune. Haka kuma an fito da rabe-raben ƙabilar Kambari dangane da addini. A cikin wannan
babin an ba da ma’anar mutuwa daga bakin masana da kuma alamomin mutuwa. Bayan
haka an yi ƙoƙarin bayanin abin da kalmar Maguzawa ta ƙunsa.
3.1 Taƙaitaccen Tarihin Birnin Yawuri
Birnin Yawuri, wadda aka fi sani da tushen Yawuri, masana
daban-daban a kan ilimin tarihi sun yi bayanai dangane da kafurwar garin. Haris
(1930:42) ya bayyana cewa, garin ya kafu ne kimanin shekaru dubu ɗaya
da suka wuce. Kuma ya ƙara da cewa sarakuna
kimanin ɗari
ɗaya
da ashirin da ɗaya sun yi mulki a ƙasar.
Mahdi (2013) ya bayyana cewa garin Birnin Yawuri ya kafa
tarihinsa ne tun a wajajen ƙarni na 13 zuwa 14, haka
Sahabi na da ra’ayi irin na Mahdi da Haris. Bayan wannan kuma bayanai sun nuna
cewa daga bakin sarki na ɗaya har zuwa na talatin
da huɗu,
duk sun yi sarauta a garin Birnin Yawuri. Garin ya rasa babban masarautansa ne
a wajajen shekaru (1858 – 1878) daga bisani ya koma a garin Yawuri.
Dangane da dalilin barin sarkin wannan zamani zuwa Yawuri,
wani ra’ayin ya nuna cewa Umamru Nagwamutse ɗan sarkin Musulmi Ahmadu
Atiku, a lokacin da yake yaƙan wuraren da ba su da
Musulunci, bayan ya yi yunƙurin zuwa garin Birnin
Yawuri sarkin wannan zamani Suleman ɗan Ado ya yi shakkan kar
da ya riske shi, duk da yake akwai Musulunci a wurin amma bai samu gindin zama
ba. Sai wannan sarki ya yi hijira daga Birnin Yawuri zuwa Ikum. Daga bisani sai
masarautan ta dawo a Yawuri.
Ummaru Nagwamutse ya fito daga Gwamutse a shekaran (1851).
Amma kuma ya shiga ƙasar Birnin Yawuri ne a
shekarar (1864) bayan sarkin ya yi hijira (Adamu, 2000: 209-296). Birnin Yawuri
ya karɓi
sunansa ne saboda shi ne tushen Yawuri. Don haka ake kiransa da garin
birnin Yawuri garin na ɗauke da ganuwa, don haka
akawai ƙoƙfofi guda shida kamar
haka:
1. Ƙofar Adama
2. Ƙofar Katsinawa
3. Ƙofar Muta
4. Ƙofar Durɓi
5. Ƙofar ‘yan Kara
6. Ƙofar Hayin
Dawaki
Adamu (2013: 43) ya nuna cewa kafin Amina na Zazzau ta
ziyarci Birnin Yawuri, garin na ɗauke da ganuwa. Domin
Amina ta zo a tsakiyar ƙarni na 16. Kafin ta zo
mutanen wurin sun gina ganuwarsu.
Bayan haka kuma kasancewar ƙabilar
Kambari, su ne suka fara zama a wurin, wanan ƙabilar
na bautar magiro ne. Domin tabbatar da cewa su ne suka fara zama a wurin, akwai
sunayen unguwanni a cikin garin Birnin Yawuri. Waɗannan suna a kambarce
suke. Haka su ne unguwannin farko a cikin garin. Mafi yawanci babu su a yanzu.
Ga sunayen waɗansu daga ciki:
1. Unguwar Cicinawa
2. Unguwar Dankal
3. Unguwar litaba da sauransu
Haka kuma akwai rafuna, su ma mafi yawancinsu a cikin harshen
Kambarci ne. rafin gwantaci da rafin Madiso da rafin Kwankwami da sauransu. Waɗannan
ƙabilar da suka fara zama a wuri mafi akasarinsu
ba Musulmai ba ne don haka suna aiwatar da tsafe-tsafensu don biyar buƙatunsu na yau da kullun. Sukan je roƙon ruwa a duk lokacin da tari ya addabe su. Bayan
haka kuma suna kai gumba a matsayin sadaka don samun biyar buƙata kamar ta rashin haihuwa da sauransu. Ga
mahallin kamar haka:
1. Kan daka a unguwar Hajin Daulaki
2. Madutsi a unguwar Sharifai
3. Dallafe a unguwar Dankita
Dangane da shigowar Musulunci a Birnin Yawuri, masana tarihi
sun bayyana ya shigo ne a wajajen shekaru (1620-1663). Ga sunayen sarakunan da
suka yi mulki a cikin garin kafin ta bar cikin ganuwar Birnin Yawuri:
Suna |
Shekara |
|
1. |
Tafiraulu |
1411 – 1433 |
2. |
Kamuwa |
1433 – 1450 |
3. |
Bunyagu |
1450 – 1480 |
4. |
Sakazu |
1480 - 1508 |
5. |
Yawuri |
1508 – 1531 |
6. |
Kisagiri |
1531 – 1560 |
7. |
Jarabana |
1560 – 1572 |
8. |
Gimba |
1572 – 1600 |
9. |
Lafiya |
1600 – 1601 |
10. |
Kasafaugi |
1601 – 1620 |
11. |
Jarabana (II) |
1620 – 1663 |
12. |
Gimba |
1663 |
13. |
Kasagurbi |
1663 – 1665 |
14. |
Kana |
1665 – 1660 |
15. |
Janrina |
1660 – 1670 |
16. |
Dutsi |
1670 – 1674 |
17. |
Lafiya |
1674 - 1675 |
18. |
Kada |
1675 – 1689 |
19. |
Gandi |
1689 – 1703 |
20. |
Ɗan Ibrahim |
1703 - 1714 |
21. |
Muhammadu |
1714 - 1723 |
22. |
Lafiya (II) |
1723 - 1745 |
23. |
Yanazu |
1745 |
24. |
Umar Gandi |
1745 - 1748 |
25. |
Suleman Jarabana |
1748 - 1770 |
26. |
Alu Lafiya |
1770 - 1775 |
27. |
Ahmadu Jarabana Jatau |
1775 - 1790 |
28. |
Sha’aibu Madara |
1790 - 1790 |
29. |
Mustafa Gazari |
1790 - 1793 |
30. |
Muhammadu Albashir Ɗan
A’i |
1793 - 1838 |
31. |
Ibrahim Dogon Sarki |
1838 - 1844 |
32. |
Jibrin Gajeren Sarki |
1844 – 1853 |
33. |
Abubakar Jat |
1853 - 1858 |
34. |
Suleman Ɗan
Ado |
1858 – 1878 |
https://www.amsoshi.com/2017/11/05/tanade-tanaden-tsafin-maguzawa-aladunsu-na-aure-da-haihuwa/
Bayan haka da tafiya ta yi tafiya, Birnin Yawuri aka ba ta
uban ƙasa. Ana kiran fadar da sarkin gabas. A yanzu
haka ana aiwatar da mulki a wurin. Ga sunayen saurakunan da suka gabata har
zuwa yanzu:
Sarki |
Shekara |
|
1. |
Sarkin gabas Ɗan
Tsoho Agizo |
1914 |
2. |
Sarkin gabas Isah Uban
Masallaci |
1923 |
3. |
Sarkin gabas Salihu |
1925 |
4. |
Sarkin gabas Yakubu Mai
Saje |
1927 |
5. |
Sarkin gabas Usman Ango |
1950 |
6. |
Sarkin gabas Usman
Malam Gange |
1955 |
7. |
Sarkin gabas Suleman |
1955 |
8. |
Sarkin gabas Attahiru |
1956 |
9. |
Sarkin gabas Abubakar
Karazube |
1977 |
10. |
Sarkin gabas Jibrin Na
Wando |
1986 |
11. |
Sarkin gabas Mannir
Suleman |
2006 |
Wannan shi ne taƙaitaccen
tarihin Birnin Yawuri, domin tarihin garin kandama ne.
3.2 Tarihin Kambarin Birnin Yawuri
Adamu (2013) ya bayyana cewa ƙabilar
Kambari sun fito ne daga Makka. Suna ɗaya daga cikin ƙabilar da annabin rahama ya kora waɗanda
ke bauta wa gunki. Haris (1930) ya bayyana da cewa babu ainihin lokacin da za a
tabbatar da zuwansu. Amma ana hasashen cewa tsakanin lokacin da aka ba annabi
Muhammadu (S.A.W.) annabta (611AD) da kuma lokacin da ya koma ga mahaliccinsa
(632 AD). a wannan lokacin ne suka yi hijira suka samu kansu inda suke a yau.
Wannan ƙabila na Kambari ana
samunsu wurare da yawa a cikin jahar Neja da kuma kudancin Kabi, a cikin
gunduman Ngaski. Kambari ƙabila ce da ke da
harshensu na Kambarci. Kuma mutane ne baƙaƙe amma ana samun farare a cikinsu ta launin jiki.
Haka kuma, ba su rufe jikinsu da tufafi baki ɗaya. Amma bayan tasirin
Hausawa da kirista ya yi naso a gare su, da kuma tasirin addinin Musulunci har
waɗanda
ba su karɓi wannan addini ba, suna amfani da tufafi a
maimakon walki ko kuma ganye.
Matan Kambari ba su ɗaukan kaya bisa kai sai
dai a bisa kafaɗa. Haka kuma suna goyon
‘ya’yansu ne a ƙugu ba saman baya ba
kamar Bahaushe da kuma wasu ƙabilu. Bakambare bai cika
zama cikin gari ba. Rayuwarsu ta keɓanta ne a jeji, kuma ba
su yin kasuwanci. Maguzawan Kambari sun dogara ne a harkan noma da kiwo, a
dalilin haka ne ake bin su da kirari kamar haka:
Kambari dawa ‘yan zaki,
Ga gidanku ga na maciji,
Kun sha rura maciji ya sha.
Dangane da abin bauta kuwa, suna bauta wa gunki ne da farko,
bayan yin hijiransu daga Makka, sai daga bisani suka koma bauta wa magiro.
Wannan magiro iska ne domin ba su ganin shi ido da ido. Kuma sun yi masa ginin ɗaki
ne na laka. Ƙabilar Kambari sun
bayyana cewa sukan gane gittawarsa a wani lokacin da suke yin bauta. Kuma sun
yi imani da shi domin idan fari na rashin ruwa ya addabe su Kambari kan je
wurin ɗakin
don roƙonsa da ya ba su ruwan sama.
3.3 Muhallin Ƙabilar Kambari
Dangane da muhallin ƙabilar
Kambari kuwa, ana samun Kambari a wurare da yawa musamman a cikin jahar Neja, a
ƙasar Kwantagora. Waɗannan ƙauyuka sun haɗa da Ibeto, Auna da
Nasko. Haka kuma ana samun Kambari a Tungan Mangoro da Sulka, da Kura, da kuma
Wando da dai sauransu.
Bayan haka kuma a cikin jihar Kabi a gunduman Ngaski ana
samun ƙabilar Kambari sun yi kaka gida. Kamar a ƙauyukan Ngaski akwai Agwara da Lofa, da tungan
goguwa da sauransu. Bayan wannan kuma a ƙauyukan
Birnin Yawuri ana samun ƙabilar Kambari. Waɗannan
muhallin da ake samun su sun haɗa da Kwana, da Kambuwa da
Kambu da Ƙara Gashi da Tungan
Koruwa, da Laka da dai sauransu.
Bayan haka idan aka dubi taswiran jahar Kabi, a cikin
littafin Adamu (2000) za a ga cewa ƙabilar
Kambari na Ngaski da na Birnin Yawuri duk suna layi na 9042 da 110N daga kudu. Haka kuma suna layin 40 da 50 daga gabas da layin Ikwaito.
3.4 Rabe-raben Kambari
Dangane da rabe-rabɓen Kambari, za a iya
kallon su ta fuskoki guda uku. Da farko rabuwa ta gefen muhalli. Haka kuma
akwai rabe-raben ƙabilar Kambari dangane da
karin harshensu kamar Kambari Akimba da Kambari Abadi, suna da bambancin karin
harshe a tsakaninsu. Haka kuma Kambari Awunci da Kambari Agadi suna da
bambancin karin harshe a tsakaninsu da dai sauransu. Duk wannan bambancin bai hana
su jin maganar junansu ba. Sai dai kawai bambancin kalmomi.
Bayan wannan kuma, sai rabe-raben Kambari ta gefen addini.
Wannan rabe-raben za a iya kallon su gida uku kamar haka:
1. Maguzawan Kambari
2. Kambari Musulmai
- Kambari Kirista
Maguzawan Kmabari, wannan kaso na ɗaya
daga cikin ƙabilar Kambari. Ƙabila ce da ke bautar Magiro (iska). Haka kuma ba
su rufe jikinsu da tufa baki ɗaya. Bayan haka giya bai
zama haramtacce a wurinsu ba. haka suna cin mushe duk al’adunsu na mutuwa da na
aure da haihuwa ya bambanta da Kambari Musulmai da kuma Kambari Kirista.
Kambari Musulmi, dangane da shigowar Musulunci a ƙasar Birnin Yawuri. Masana irin Adamu (2013) da
Sahabi (2000) duk sun bayyana cewa, Musulunci ya shigo ƙasar ne a shekaran (1620-1663). Don haka bayan
Musulunci ya samu gindin zama a ƙasar
Yawuri, sannu a hankali ƙabilar Kambari Maguzawa
suka kama shiga addinin Musulunci.
Wannan kaso na Kambari Musulmai sun bambanta da Maguzawan
Kambari. Da farko suna da bambanci ta gefen tufa, domin sanya tufafinsu tamkar
na Musulmai ne. Haka kuma giya ta haramta gare su. Bayan haka kuma, tsarin
neman aure, da sanya suna bayan an haihu duk al’adun da suke aiwatarwa sun koma
irin na tsarin addinin Musulunci. Bayan haka, a duk lokacin da wani daga
cikinsu ya mutu suna yi masa sallah da duk abin da Musulunci ya tanada.
Kambari Kirista, wannan kaso ne daga cikin rabe-raben ƙabilar Kambari dangane da addini. Su waɗannan
Kambari su ne suka bar addinin gargajiya kuma ba su shiga addinin Musulunci ba.
bayan haka yanayin shigarsu ya koma irin shigar Kirista. Haka kuma, idan wani
daga cikinsu ya mutu suna sanya shi ne a cikin akwati akasin yadda suke yi a
gargajiyance.
Haka kuma al’adun aurensu duk ya koma irin na Kiristanci.
Domin kafin shiga wannan ɓangare hanyoyin mallakan
mace da ɗaurin
aure da zanen suna duk sun canza. Sun koma irin koyarwan addinin Kirista.
3.5 Ma’anar Maguzawa
Dangane da ma’anar maguzawa, masana sun bayar da ra’ayoyinsu
dangane da su wane ne Maguzawa. Abdullahi I.S.S. (2008) ya bayar da ma’anar
Maguzawa da cewa:
Maguzawa: “Hausawan asali waɗanda ba mululmi ba, waɗanda addininsu na gargajiya ke jagorancin
rayuwarsu.”
Don haka idan aka duba\i ma’anar da ta gabata dangane da
Maguzawan Hausawa. Ana iya cewa Maguwazan Kambari su ne, Kambarin asali waɗanda
ke bin al’adun gargajiya, musamman waɗanda suka saɓa
wa addinin musulunci.
3.6 Ma’anar Mutuwa
Bahaushe ya aro kalmar mutuwa ne daga harshen Larabci wato
(almautu). Sai daga baya ya Hausance kalmar ta koma mutuwa. Amma akwai sunayen
da yake yi mata, waɗanda ba su da alaƙa da Larabci. Waɗannan sunayen kuwa sun haɗa
da rasuwa da faɗuwa da wucewa da kau da
tuni da sheƙawa da ƙaura da kuma gangarawa da sauransu.
Waɗannan sunayen su ne
Bahaushe kan kira mutuwa da su kafin ya karɓi addinin Musulunci.
Bayana ya karɓi addinin Musulunci sai lafuzzansa suka sauya ba
kamar da ba. bayan haka sai ya canza mata suna. Waɗannan
sunayen sun haɗa da mutuwa da hariyar gabas da kwanta dama da
kuma hutawa da sauransu. Ma’anar mutuwa daga bakin masana:
Abdullahi, I.S.S. (2008) ya bayyana ma’anar mutuwa da cewa:
“Rasa rayuwa ko barin aiki ga abu mai rai ko
maras rai mutum ne ko dabba ko tsiro ko wata halitta ko kuma wani abu mai
amfani da yadda ake ganin alamun ba zai taɓa dawowa ba, yadda yake a da ba kafin ƙaddarar rasa rayuwar ta auka masa.”
Ƙamusun Hausa na Bayero (2006: 354) ya ayyana ma’anar mutuwa
da cewa:
“Rasuwa ko ƙarshen ran mutum ko dabba, ko kuma duk wani abu mai rai.”
Ta la’akari da ƙunshiayr
waɗannan
ma’anoni a taƙaice ana iya cewa “mutuwa
na nufin, ƙarewar rayuwar dun wani
abu mai rai, dabba ko mutum ko kuma tsiro bayan rayuwar wannan abu.”
3.7 Alamomin Mutuwa
Dangane da alamomin mutuwa, akwai alamomin da ake gani a duk
lokacin da ake tunanin ya kusa mutuwa ko rai ya kusa ɗaukewa.
Wasu daga cikin alamomin sun haɗa da; a dubi idonsa in
aka ga bai motsa ba wato kintSawa. Bayan haka ana duba idadunsa idan aka ga
fari ya rinjayi baƙin ƙwayan idonsa.
Wata alama kuma ita ce sauyawar jiki. Ana aza hannu a jikinsa
idan aka ji zafi ko kuma jikin ya yi sanyi to lallai ana tunanin mutuwa ya
tabbata gare shi. bayana wanann kuma sai yin shaƙuwa
wato za a ga yana yin shaƙuwa bi da bi, har ya kai
ya kama yi kaɗan-kaɗan. Bayan haka kuma ana
duban ramin maƙogoro, ko kuma zucciya
idan aka ga bai halba ba, ba shakka mutuwa ta tabbata a gare shi.
Bayan haka ana duban yatsan ƙafarsa
babba, idan aka ga ba ta motsa ba wanann ba shakka alamar mutuwa ta bayyana
gare shi. A gargajiyance idan duk waɗannan alamomin sun
tabbata za a buga wani abu ko a yayyafa mai ruwa idan kuma aka kira sunan shi
aka ce Tanko, ko Musa bai amsa ba, tolallai ya mutu.
3.8 Naɗewa
Wannan babi na uku babi ne da aka yi ƙoƙarin kawo abubuwa kamar
tarihin birnin Yawuri a taƙaice da kuma tarihin ƙabilar Kambari tare da muhallinsu. Bayan haka
kuma, an kawo ma’anar mutuwa daga bakin masana da ma’anar Maguzawa. Haka an
kawo alamomin mutuwa. Wanann babi na iya zama gudummuwa a wannan bincike.
2 Comments
Assalamu alaikum gaisuwa tare da fatan alhairi zuwa gare ku tabas bude wannan shafi da kukayi domin bunkasa karshen Hausa tabas abin farincikine don haka nema ina matukar sun Hausa da kuma iya rubuta ta.
ReplyDeleteMWa'alaikumussulam. Muna farin cikin kadancewa da kai. Mun gode.
ReplyDeleteENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.