Ticker

6/recent/ticker-posts

Anya Dai! Mu Taka Sannu



Ga alama abubuwan da magabata suka hanga bisa ga nassohin bayyanar ƙarshen zamani sun yi kere a zamaninmu. Manya da ƙananan alamomin tashin duniya sun yi wa zamaninmu dumudumu. Maƙasudin wannan waƙa jawo hankalin masu hankali a kan sake bitar waɗannan abubuwa da idon basira. Ganin irin nisan da muka yi ya sa na kira mu da muryar: Anya Dai! Mu Taka Sannu. Na rubuta ta ranar alata, 28-01-2014, 11:38pm, a Katsina.

Anya Dai! Mu Taka Sannu
Daga


1.                 Na kiri wahidun Ƙawuyun mai yau da gobe,
Mai baiwa dare da rana kuma ba shi zobe,
Mai rani da damina mai manyan gulabe,
Mai bunƙasa talikai bisa manyan gurabe,
              Ba don sun buwaya sun isa ne ba.

2.                 Kurin taliki a ce, yau shi ke iyawa,
Kamin an jima ka iske ya so gazawa,
Gobe a iske ya yi rauni daɗa sai macewa,
Babu abin da yar rage gu nai sai rufewa,
              Allah Ka buwaya ba da musu ba.

3.                 Hauka ce ta gaske kullum fifita kanmu,
Ko doro da taƙamar asalin zuriyarmu,
Ko kuri da hura hanci don ɗan saninmu,
Wai yau mu ka taƙama don kuɗɗin kashinmu,
              Da gadara ga wanda bai samu ba.

4.                 Son rai ya rufe ido mun faɗa ga cuta,
Ba tausai ga zuciya kullum sia mugunta,
Mun ɗebe sani da sabo har gun maƙwabta,
Ma su faɗa a ji su, su ne manyan macuta,
              Fasiƙƙan da ba su ƙyamar zamba.

5.                 Manya sun zamo macuta me zai kasance,
Yara suna gani karatu suka yi duƙunce,
Sannu a hankali ƙasa daɗa ta zan makabce,
Ba jagora dole za a yi mugun maraice,
              Kowa ke cikinta bai tsere ba.

6.                 Yau mai gaskiya cikinmu abin zolaye ne,
Mai son gaskiya cikinmu shi koma tsugunne,
In ya ba da bai, mu bi shi da zagi da nune,
In ya doshi dandali sai ka ga an yi done,
              Cin zarafinsa ba da an fasa ba.

7.                 Mai ƙarya a ba shi tabarma tamatela,
An ƙunso ciki a riga an karye hula,
Kowane dandali da tabarna ga hilalla,
Ƙatti sun yi leme sun zama bayin sulalla,
              Sun bautar da kansu ba da shiri ba.

8.                 Duk maganar da mun ka yo, bar ta a nan a baki,
In ka ce ka bincika, sai mun saka tsaki,
Daɗin baki ne da hila wane maroƙi,
Tsara batutuwan ƙire, ƙulli ko masaƙi,
              Babu shirin da ba da mu aka yi ba.

9.                 In ka ji rantsuwa ka ɗauka duk gaskiya ce,
Sai an kai ka an baro ka ga duk damfara ce,
Duk tsarin da an ka yo ka ga duk tambaɗa ce,
Mai kuri da hankali ka ishe ya makafce,
              Bai sai inda kansa ke ciwo ba.

10.             Masu faɗin a ƙyautata su ke ɓarka cuta,
Mai wa’azi ka iske ya gina ramin mugunta,
Wanda ka taimaka shi yo maka tarkon asuta,
In ka zo gida musibar cutar maƙwabta,
              An shiga ukku ba da an shirya ba.

11.             Kukan kurciya ba zai hana gero tumu ba,
Hurjin dorina ba zai hana jirgi fito ba,
Kushe mutum ba zai hana shi hawa martaba ba,
Zunɗe hasada ba za su tare ɗaukaka ba,
Kun fayakunu na ga sarki babba.

12.             Mai rai in yana tuni da zuwa duniyarsa,
Dole ya girka tagumi ga tunin lahirarsa,
Kwana a tashi gobe ba mai jin ɗuriyarsa,
Sannu a hankali ka iske a bar ambatarsa,
              Ko kabarinsa ma ba za a tuna ba.


13.             Mun za ka zamanin da yaz zo ga gaɓa ta ƙarshe,
Alfasha da munkari duka yau ga su tarshe,
Masu sani da jahilai duka an zan bisashe,
Samun adili amini sai dai hasashe,
              Ƙwarori cikinmu ba da yawa ba.

14.             Yau algussu ta zamo almiskin turare,
Duk wani zaƙuno haramun aka yin kwarare,
Manya, yara, ‘yan samari, hatta budare,
In aka taru dandali ko a bukin amare,
              Ba zancen a gyara gobe ake ba.

15.             Yara su kangare su bar ɗa’a gun iyaye,
Ba aiki dare da rana sai shaye-shaye,
Babu yinin da ba su sa tsofaffi hawaye,
Har an alluhe hawayen duk sun tsiyaye,
              Dole hawna jini musiba babba.

16.             Rowa ta yi kwance kwancin kwana zukata,
Mai abu ya fi son maras abu sai dai shi ƙwata,
Marashi ya ƙi dangana sai ya laɓe ya sata,
An haɗu babu godiya da wadatar zukanta,
              Ba marashi ba, ba ga mai samu ba.

17.             Maganar ɗan’uwantaka yau ta zamto zance,
Yau ‘ya’yan ciki guda babu shiri da zance,
A wajen ‘yan uba faɗa had da ciro itace,
Shi dangin uwa, uba, yanzu a kai shi kwance,
              Kaka na gani ba zai magana ba.

18.             Tobashi ya zan abokin yaƙi da gaba,
Ɗan wa ɗan ƙane ba za a yi auren zumu ba,
Inna ka wanke-wanke matan ɗa bai kula ba,
A ci irlinta ɗa yana kallo bai muɗa ba,
              Bone ya ci mu ba batun waƙa ba.

19.             Yau babba yana gani yaro zai haye shi,
Girmama hurhura da gemu wa ke kula shi,
Muddin babu ta yi ma kanta ka yi gyashi,
Kuma mulki na zamani an san, ba ka, ba shi,
              Ban ga abin da za ka ce a jiya ba.

20.             Wanda ka wa ƙafa ya ruga shi zai taɗe ka,
In kuma ɗalibinka ne ƙwazonai ƙure ka,
In belinsa kay yi sai ya sa an tsare ka,
Ka yi jinyarsa ka yi ciwo shi bai biya ka,
              Bai ƙi a ce da safe ka shure ba.

21.             Suruki bai ganin surukkai natsuwa ta samai,
Yanzu talakka ba su ba sarki martabatai,
Girmama mai gida ga yaro ƙannai da yannai,
Ga a gaba-gaba da yaro zai kau da kainai,
              A yi masa sallama ba zai karɓa ba.

22.             Yau rana kataa ake yin sata da ƙwace,
‘Yan boko ga dukiyar gwannati sace-sace,
Mata babu godiya ga maza sun butulce,
Ga mai hankali ga juji na tsince-tsince,
              Ko ya kuwwata ba za a kula ba.

23.             In kun lura shugabanci ya zan na wasa,
Domin yara an ka ba dama sui ta gasa,
Yau dattibe su ka fada gidajen matasa,
Ɗan iska ya kwaso kaya tsoho shi amsa,
              Shegen bai kula da na gode ba.

24.             Yau samunmu sai ga matanmu ɗiyan tsatsonmu,
Yannai mu ka ƙwadagon dako shagon ƙanenmu,
Sai mun haukace mu ƙwaci abin ɗan cikinmu,
Daɗa samunmu ya zamo kuka zuriyarmu,
              Da takaici da rarrabe a yi gaba.

25.             Mai samun da bai hana wa ubanai bara ba,
Bai hana tsohuwarsa yawon ga-sussuka ba,
Bai ɗebe wa macce yunwar harjin ciki ba,
Bai hana ‘yan ɗiyansa rokon suɗin miya ba,
              Gara rashi da shi idan kun duba.

26.             Masu wa’azu yanzu su ka takaicin mutane,
A tsakaninsu ba shiri sai zagi da nune,
Mabiya an haɗa su dambe da yin ƙone-ƙone,
Kuma su za su ce wa gwannati duk ‘yan tasha ne,
              Wa ka zubin adashi bai kwasa ba.

27.             Mai samu ba zai yi laifi ba ga malumanmu,
Yai zina yai ficen liwaɗi a gaban idonmu,
Ya yi maye ya yo kisan kai mun kau da kanmu,
Ya yi satan kuɗin hukuma kowa shi damu,
              Ba ka taɓa ji a mumbarin huɗuba ba.

28.             Masu rabon faɗa a da, yau su ke haɗawa,
Masu faɗa a ji su da, yau wa ke kulawa,
Masu kashin wuta a da, yau su ke hasawa,
Ƙarshen lokaci musibu ka yawan kitowa,
              Ga mu cikinsu ba da mun tsere ba.

29.             Wa ka musun zamanmu ‘yan tsafi ‘yan ta’adda,
Hausawa, Iyamurai, Yarbawa, Kakanda,
A yi tsafi da ɗan mutum farfesu da ganda,
An tsotse jinin mutum an girke a randa,
              Wai don jarrabara ta tara kwababba.

30.             Ba wasa ba yau ƙabilanci ya kashe mu,
‘Yan gargajiya da masu aƙida dukanmu,
Yau harshenmu ya zamo tamkar annabinmu,
Mu yi yaƙi saboda shi muka fifita kanmu,
              Kalimar laa illah ba za a kula ba.

31.             Imaninmu yau a kai samu yankunanmu,
Tun daga can a mulmula su zuwa ƙanyukanmu,
In aka kai a sa gidajenmu na mallakanmu,
To daga nan gidan a ja su zuwa ɗakunannan,
                   Kowa yar rasa ba za mu kula ba.

32.             Fasiƙƙai da fajirai bisa manyan kujeru,
‘Yan iska da ‘yan daba su ka kira a taru,
Marasa gaskiya ka wa muminnai dabaru,
‘Ya’yan goruba da ‘ya’yan ɗinya da faru,
              Duk ba su kai abarba zaƙin sha ba.

33.             Koma baya yau ɗiya sun ka zamo mahaifa,
Su ka kira a zaburo har a yi sansarefa,
Su yi tsawa mu kasa miƙe ƙafafu a rumfa,
Haka ƙarshenmu zai zamo riƙa sanda da malfa,
              Ba mu haifa wa kanmu albarka ba.

34.             Kai da ɗiyanka ba ka tsawa balle bugawa,
In ka ce ka tsaurara doka za a sawa,
In suka ƙaurace, gida bariki ke tarawa,
Tsufa na kiranmu ‘ya’ya na fandarewa,
              Ba tausanmu za su ji su kula ba.

35.             Mata an ka ba su ‘yancin yawo tsirara,
Aure bai da dole zancen zina babu tara,
Kulle an ka sa gudun hijira tun a bara,
Matan zamaninmu ba kunya ko ta kara,
              Ba a taɓa yin kamar su fajirci ba.

36.             Makarantun biɗar sani ƙatanya da ƙatta,
Ofis kallabi da beje a tsakan macuta,
Ƙarshen gwannatinmu shaggu ke mallakanta,
Dole ƙasa ta durƙusa komai ɗaukakarta,
              Ba ta dace da masu jagora ba.

37.             Tsarin namu mun ke ce Allah bai iya ba,
DokokinSa mun ka ce ba su za a bi ba,
Ɗan ilminmu bai ci sa’ar kare ƙasar ba,
Muka faɗa cikin faɗan basasa da gaba,
              Ba a san lokacin da za shi lafa ba.

38.             Muddin dai abin da kan noma za ka girba,
Dole a mai da sungumi aiki bai yi kyau ba,
Shukar ta suƙe ga tausa ba a bar fari ba,
Ba sauran iri batun noma bai tsaya ba,
              Zancen cin tumu ba a fara ba.

39.             Duk shukar da ta’ tsiro bisa juji ku lura,
Ga yabanyarta ba kama nata kyawon tagara,
Tun ba ta ja kara ba hoge zai tad da ƙura,
Dole a bar tururuwa su yi aiki da fara,
              Kwaj jiri amfalolo bai huta ba.

40.             Duk wani mai jiran ɗiyan yau ƙarshensa hauka,
Balle mai shiga faɗansu ku mai she shi zakka,
Mai kuri da su ina tunsan dambalarka,
Mai bautar da kanka don su ban tufanarka,
              Mai nema ba zai zaton ya rasa ba.

41.             Yau an bar gudunmuwar tayyo ba a jin ta,
Kyauta sai ga ‘yan siyasa a wajen masarta,
Haka gayya da gangamin ajo haɗin zumunta,
An bar ɗegiya tukuici in an yi kyauta,
              Wa ka bukin da bai ciwo riba ba?

42.             Haka muka iske zamani ya raba kan mutane,
Ya gigita masu hankulla sun yi zone,
Wa da suka san abubuwa an ce dambala ne,
An tsiri sabuwar fahimta an kai tsugunne,
              Ba ta fis she mu ɗemuwar hanya ba.

43.             Iya bakinka kakkacin yin zance guba ne,
Kere tsara cikin abin taro dambala ne,
Nuna sani a dandalin jahillai kure na,
Cin zarafi da kushe girman manyan mutane,
              Ba a taɓa yi a ba da labari ba.

44.             Zagin kasuwa mafarinsa ake kulawa,
Ƙandume duniya ga zance ya zan ɓacewa,
Wawa ke bugun gaba da kirarin ƙwarewa,
Duk mai hankali yana jin ƙyamar zaƙewa,
              Ba a taɓa shisshigi a kai ga sago ba.

45.             Bari tsoron kira Alu tuna laifin kiranka,
In ka shaida babu laifi ɓarje guminka,
Ban ci ƙashi ba ban aman tsoka kama kanka,
Tsorona a zamaninmu a fis she ni zakka,
              In ban hau ga godaben sunna ba.

46.             Duk mai hankalin karatu in zai kwatance,
Da fitinnun da ke wakana safe maraice,
Ga yaƙi da zanga-zanga kullum rigince,
Mun za ka lokaci na ƙarshe nassi rubuce,
              Komi yab ɓata ba a gane ba.

47.             Ka da mu bi lokaci mu shafa da ainin nagarta,
In ya tarar da mu muna bisa aikin ƙazanta,
Mu muka gayyato Nakini ga aikin mugunta,
Kowace rai ta ƙuna sai ta yi kuka da kanta,
              Ba aikin waninta za a awo ba.

48.             Mu ka faɗan abin da ba mu nufin aikatawa,
Alƙawalin da mun ka yo ko ɗaya ba cikawa,
Zantukkanmu barkatai babu wurin riƙawa,
Kwaz zaune mu sau guda bai fatar daɗawa,
              Ba ƙoshi mukai da ha’inci ba.
49.             In muka ce a yo gabas, to tarbe mu yamma,
Mu yi cuta da assuba tanzanko da yamma,
Hannu gaisuwa ƙafa sata babu ƙyama,
Bayan mun yaba mu koma tono da galma,
              Ka da Allah Ya kai ka ba furta ba.

50.             Mai ƙaunar ganinmu bai san siffarmu ne ba,
Mai ƙaunar zama da mu bai taɓa jin mu ne ba,
Mai kuri da mu bayani ab bai jiya ba,
Mai gaba saboda mu bai ahumo da kyau ba,
              Matuƙar ya sani ba zai fara ba.

51.             Dakance ni ɗan uwa kar ka ga na tsananta,
Hujjojin da ke gare ni idan na fasalta,
Zai zama arashi da gugar zanar maƙwabta,
Ai ta zato a faɗa giba ɓannan zukata,
              Maƙasudin ya zanto bai nasara ba.

52.             Ita sandar bugun kaɗe ba tada take ba,
Sandar wawa ba ta tsallake yaro da babba,
Bisa kan mai uwa da wabi na yi in ka duba,
Jifa ce ta faɗa kan tsokai ban hana ba,
              Kaina cikinsu ban ɗebe ba.

53.             Kai ko mai zato da tawili can ga kanka,
Kai kuma mai fashin baki ban hana fassararka,
Masana Hausa masu fiɗar waƙa matarka,
Fatata ku ganyato ni mu yo ga-ni-ga-ka,
              A yi sharhin da ba cikin son rai ba.

54.             Imaninmu munzali nasa ba mu kai ga ci ba,
Muddin mun ka kai ga mulki ba zan faɗi ba,
Ba mu taɓa cin karo da banza muka kau da kai ba,
In muka tsundume cikin daula ba mu iya ba,
              Ba ƙaramin kira ka sa mu jiya ba.

55.             Ƙarya ba ta gargaɗar cuta ko gwadawa,
Damben tsegumi da tsince wa ke rabawa?
A yi ɓanna da mu ina bakin tsawatawa?
Taratsin fashin baƙi kanmu yake tsayawa,
              Ba kan fasiƙai da ‘yan bidi’a ba.

56.             Ba mu mun ka fara yin wa’azi duniya ba,
Malamanmu ba hisabi aka sa su yi ba,
In muka ce mu tsabbace kowa bai iya ba,
Shaiɗan zai shigo da tarkon hasada da gaba,
              Har maƙiya su farga ban mu kula ba.

57.             Ta da gaba da alfahar ga fahintar karatu,
Ko kuri saboda samo shahadar rubutu,
Yin ɗanga saboda boko manyan sarautu,
Ai ta cuwa-cuwa tsakanin manyan ƙazantu,
Ba ƙarshen ƙwarai ake samu ba.

58.             Cewa ban da mu ina wani babban kure ne,
Hana mabiyinmu bin waninmu alamun ɓata ne,
Cewa fassrarmu dai aka bi karkata ne,
Tilasta mu bin fahintar wani dambala ne,
              Wane ciwo gare mu ba wannan ba?

59.             Kukan kurciya jawabi ne Bakatara,
Sai mai hankali da mai wayo za shi lura,
In ya ƙiya a lahira shi ji gyaran maƙera,
A buge awwazu da kwanya a kare haƙora,
              Ba su taɓa tausayin bugun ƙato ba.

60.             In don wagga duniya ce tafi kama kanka,
Babu gwani gare ta yaro bari koɗa kanka,
Magabatan da sun ka bi mata ta sa su hauka,
Baƙon duk da yat taho sai ta ba shi jikka,
              In ya zazzage ba zai more ba.

61.             Nai shukura ga Rabbana tammat na cika ta,
Bisa murya ta Ayya Maitashe na’ a za ta,
“Borin Goje” kun ji waznin gindin awonta,
Ali na Bunza ɗalibi shi yai bibiyanta,
              Ku yi gyara wurin da bai dace ba.

                       

Post a Comment

1 Comments

ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.