Ticker

6/recent/ticker-posts

Nazarin Illolin Karya Daga Bakin Makadan Baka

MUSA SHEHU

Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato
07031319454
msyauri@yahoo.com

TSAKURE:


Kasancewar ƙarya  abin ƙyama da Allah wadai ga rayuwar Hausawa, ya sa a koyaushe suke gargaɗi da jan kunne domin hani ga aikata ta. A kan haka ne ya sa Hausawa suke yawaita bayani a kan illar ƙarya da matsayin mai aikata ta  a cikin al’umma ta ɓangarori daban-daban na rayuwarsu da suka haɗa da waƙoƙinsu na baka, da karin magana, da tatsuniyoyi, da kirari, da sauran ɓangarorin adabinsu. Wannan takarda za ta yi nazarin illar ƙarya daga bakin makaɗan baka daban-daban da suke yawan ambatawa a waƙoƙinsu na yau da kullum domin a guji aikata ta saboda matsaloli ko illar da take iya haddasawa a tsakanin masu yin ta ko ma ga al’umma baki ɗaya.


Gabatarwa

        K’arya na daga cikin munanan ɗabi’un da al’ummar Hausawa ke ƙyama a rayuwarsu. Ba ma Hausawa kawai ba, kusan dukkan al’ummu na duniya ba su amince da ƙarya ba da kuma mai aiwatar da ita, wato maƙaryaci. Saboda haka ne maƙaryaci ba ya da ƙima ko mutunci a idon jama’a, hasali ma duk inda ya yi magana ba a ɗagawa da ita nan ake barin ta, don an san maganar banza ce. Kasancewar ƙarya mummunan ɗabi’a da rashin ɗorewarta da zubar da mutuncin mai yin ta ya sa Hausawa sukan bayyana ta a ɓangarori daban-daban na rayuwarsu domin nuna illarta da kuma matsayin mai yin ta, kamar a ɓangaren karin maganganusu da waƙoƙinsu da tatsuniyoyi da kirari da makamantansu. A taƙaice, wannan bincike ya mayar da hankali ne wajen bayanin yadda mawaƙan baka na Hausa ke bayyana illolin ƙarya musamman ga masu yin ta a cikin waƙoƙinsu na yau da kullum. A wasu lokuta ma idan mawaƙan suna son su muzanta  wani ko su aibanta shi, sukan danganta shi da yawan ƙarya domin kawai su zubar da mutuncinsa ko darajarsa a idon jama’a.

   MA’ANAR  K’ARYA

A K’amusun Hausa (2006) an bayyana ma’anar ƙarya da cewa, “maganar da ba ta gaskiya ba ce”. Maƙaryaci kuma “mutumin da ya saba da rashin faɗar gaskiya”. Ga al’ada ƙarya ita ce faɗar abin da ba a yi ba, ko ba a gani ba, ko ba a tabbatar ba, da kuma yin ƙari ga abin da aka ji, ko aka gani, ko yin ragi gare shi idan aka so a ƙarasar (Bunza 2009). K’arya wata ɗabi’a ce da al’adar Hausawa ke ƙyamar aikwatawa da kuma ƙyamar mai aikata ta. K’arya ɗabi’a ce da ke zubar da mutunci da ƙimar duk wani mai aikata ta a cikin al’umma. Kasancewarta  abin ƙyama da Allah wadai ga al’ummar Hausawa ya sa suke yawaita ambaton matsalarta da kuma matsayin mai yin ta a ɓangarori daban-daban na rayuwarsu, wanda suka haɗa da waƙoƙinsu da karin magana da kirari da tatsuniyoyi da makamantansu.

ILLAR K’ARYA A BAKIN MAKA’DAN BAKA


Waƙa dai kamar yadda masana suka bayyana “tsararriyar maganar hikima ce da ta ƙunshi saƙo cikin zaɓaɓɓun kalmomin da aka auna domin maganar ta reru ba faɗuwa kurum ba”(A.B.Yahya 1997). Mawaƙan baka mutane ne da Ubangiji ya ba su wata irin baiwa fitacciya wadda ba kowa ke da irin ta ba. Mawaƙan kan waƙe jama’a a cikin shiryayyun lafuzza masu kama hankali tare da jan ra’ayin al’umma da yin hannunka mai sanda a kan lamurran duniya. Dangane da haka ne a wasu lokuta sukan yawaita ambaton abin da ya shafi ƙarya ko maƙaryaci a cikin waƙoƙinsu na yau da kullum da suke yi wa jama’a domin bayyana mummunar matsayin masu yin ta da kuma illolinta a rayuwa. Sukan yi hakan ne ta hanyar bayyana illar ƙarya da kuma  muzanta mai aikata ta. A wasu lokuta ma idan suna son su muzanta wa mutum sukan ambaci cewa mutum ne mai yawan ƙarya domin mutane su ƙyamace shi. A kan haka, za mu iya kallon illolin ƙarya daga bakin makaɗan baka daban-daban kamar haka:

 

Zubar da Mutunci


        Kamar yadda gaskiya ke ɗaukaka darajar mutum da samar masa mutunci da ƙima a idon jama’a, hakazalika ƙarya ke ƙasƙanta darajar mutum da zubar masa da mutunci da ƙima a wajen jama’a. A Hausance, duk wani ka soka da abu biyu ƙarya da zina ka zubar masa da mutuncinsa ga jama’a. Duk inda maƙaryaci yake za ka iske mutane suna yi masa kallon hadarin kaji, wato kallon maras mutunci. Haka ma duk inda ya faɗi magana nan ake barin ta ba a ɗagawa da ita kasancewar sanin kashi tis’in cikin ɗari na maganarsa babu ƙamshin gaskiya a cikinta. A wasu lokuta ma ko da gaskiyar ya faɗa ba a aminta da ita saboda sanin halinsa. Makaɗa Mailauni Bakura ya shigo cikin sahun mawaƙan bakan da ke yi wa maƙaryaci dubin uku saura kwata. Ga dai abin da yake cewa a kan maƙaryaci a waƙar da ya yi wa Bafarawa kamar haka:

Jagora: Ga wane na azan ɗan sarki na ɗan kabsu

In ya yin an da ƙarya

Shi yin an shi ruga ƙarya

Ita jiddun a’ aikinai

Yara:  Duk abin da kac ce

Ni ban yadda busa ta.

 

1.     waƙa: Bafarawa ko can bai ɗau reni ba

 


Alhaji Attahiru jikan Sarkin Rafi

 

Wannan ɗan waƙa na Mailauni Bakura yana bayyana cewa idan mutum ya kasance maƙaryaci mutuncinsa kan zube a idon jama’a, duk maganar da ya yi ba a amincewa da ita, inda ya faɗe ta nan ake barin ta.  A wani lokaci ma ko da gaskiyar ya faɗa ba za a ɗauka ba saboda an san halinsa na sabo da rashin faɗar gaskiya. Don haka ne mawaƙin ya bayyana maganar maƙaryaci da busar iska, wato magana ce wadda ba ta da tushe balle makama.

Narambaɗa ma ya taɓo irin wannan illa na zubur da mutuncin maƙaryaci na kasancewa abin gudu da ƙyama da rashin dattako ga maƙaryaci a waƙar day a yi wa Sarkin Tudu Bala, inda mawaƙin ya bayyana cewa babu mai son zama da maƙaryaci a wuri ɗaya hatta ma waɗanda ke ƙarƙashin kulawarsa. Ga dai abinda mawaƙin ke cewa:

Jagora:      Na wuce ƙarya ko ina kiɗi

Na bar ƙarya ko ina kiɗi

Nai sittin saba’in ka hwaɗa

Yara:         Mai saba’in yai ƙarya

Ana ta zunɗe nai

Ko yaran da ag garai

Duk warwatse mishi sukai

Shina yawo shi ɗai ɓaran-ɓaran

 

1.     waƙa: Ya ci maza ya kwan shina shire

 


Gamda’are sarkin Tudu Bala

A wannan ɗan waƙa, Narambaɗa ya nuna ƙarya ba abin ƙwarai ba ne ko da kuwa ga bakin makiɗi wanda da man an san shi da wasa. Haka ma ya nuna yadda mutuncin maƙaryaci ke zubewa warwas na yadda mutane ke gudu da ƙyamarsa saboda mummunar ɗabi’arsa ta ƙarya.

Abdu Kurna Maradun ya yi wa Sarkin K’ayan Maradun Abubakar wata waƙa inda ya fito da illar ƙarya na zubar da mutuncin mai yin ta a idon jama’a. Ga dai bayanin da mawaƙin ya yi kamar haka:

 

Jagora:        Mai bogaza nika tsoro

Na raina dattakunai

Yara:           In yag guma maka ƙarya

Sai ka ji mamakinai

 

1.     waƙa: Jikan Hassan ɗan Iro

 


Sarkin K’aya mai gayya

Na Magaji ba togewa

Shi yay yi damben girma

Haɗuwa da Fushin Ubangiji


Haƙiƙa Allah subhanahu wata’ala ya yi hani da aikata ƙarya kuma yana fushi da mai aikata ta. Saboda haka ya yi tanadin azaba na musamman ga masu aikata wannan mummunar ɗabi’a. Narambaɗa bai gushe ba a waƙarsa bakandamiya yana bayyana mummunan matsayin maƙaryaci da shiga cikin fushin Ubangiji, da kuma  rashin tasirin maƙaryaci na ɗorewa a rayuwa. Ga abin da mawaƙin ke cewa:

Jagora:     Na hore ki gaskiya bari tsoron ƙarya

Yara:       Mai ƙarya munahuki Allah shi Yaƙ ƙi

Har yau ba mu ga inda anka yi mai ƙarya ba

Amma ita gaskiya gari da mutane tay yi

 

1.     waƙa: Gwarzon shamaki na malam toron giwa

 


Baban dodo ba a tamma da batun banza

Idan aka yi nazarin wannan ɗan waƙar bakandamiyar za a ga cewa ya bayyana ƙarya a matsayin abin da bai da ƙarfi ko kwarjini, don haka ba abin tsoro ba ne. Narambaɗa ya ƙara da cewa maƙaryaci munafuki ne da ke haddasa fitina, don haka Allah ya yi tir da halinsa. Bugu da ƙari, ɗan waƙar na ƙara bayyana cewa, ba a taɓa samun wani ya shahara har ya samu ɗaukaka ga jama’a ba saboda ƙaryarsa, amma gaskiya ita ke dawwama a rayuwar ‘yan Adam.

Rashin Samun Taimako


Da yake ƙarya ta kasance abin ƙyama da Allah wadai ga masu yin ta a cikin al’umma, wannan ya sa masu yin ta ba su da ƙima ko mutunci a idon jama’a. A kan wannan muguwar ɗabi’a ma ko da an ga maƙaryaci cikin wani yanayi na buƙatar taimako za ka iske kowa ya ja da baya ya sa masa ido. Sani Aliyu ‘Dandawo ba a bar shi a baya ba wajen taɓo bayanin da ya shafi maƙaryaci na rashin samun agaji da ɗauki ko gudummuwa ga jama’a yayin da ya shiga wata musiba ta neman taimako. Mawaƙin ya kawo bayanin wannan illa da ƙarya ke haifarwa ga maƙaryaci na rashin samun taimakon jama’a a waƙar da ya yi wa Madawakin Yauri, yana cewa:

Jagora:      Mai ƙarhin halin hwaɗa

Bana an ba shi kashi

Hay yat tsaga kuka

Yara:         Han na yunƙuro rabo Sai nij ja da baya

Nit tuna ƙaryad da yai yi min

Gara a ba shi kashi

 

1.     waƙa: Mu zo mu ga Madawaki

 


Bai ɗau wargi ba Audu

A wannan ɗan waƙa, Sani Aliyu ‘Dandawo ya nuna cewa, babu mai ceton maƙaryaci ko da ya shiga cikin wani hali na neman taimako saboda tsananin tsanarsa da mutane suke yi na mummunar ɗabi’arsa.

 

Wawantarwa

A duk lokacin da mutum ya kasance bai da aiki sai yawo da ƙarya, za ka taras mutane na yi masa kallon jahili maras ilimi ko wawa wanda basira ta ɓace masa. Alhaji Musa ‘Danƙwairo ya tofa albarkacin bakinsa dangane da tunaninsa a kan ƙarya da maƙaryaci a waƙar da ya yi wa sarkin Daura Bashar ɗan Musa, inda ya fito da bayani a kan illar ƙarya a rayuwa da kuma yadda take ƙasƙantar da mutum har jama’a su riƙa yi masa kallon wawa mara wayo ko hankali, yana mai cewa:

Jagora:      Shi ɗan sarkin ga ya ɓakalce

Yara:         Kai ku ji yawo yakai da ƙarya

Jagora:      Shi ɗan sarkin ga ya kacace

Yara:         Kai ku ji yawo yakai da ƙarya

Jagora:      Ko jiya na ganai gidan abokinai

Yara:         Na iske shina ta yi da sarki

Jagora:      To sheri ba abin ƙwarai ne ba

In ka gane ka bash shi ya hi

 

1.     waƙa: Babban jigo na Yari

 


Uban Shamaki, tura haushi

Idan aka dubi wannan ɗan waƙa za a ga cewa, ‘Danƙwairo ya siffanta maƙaryaci da cewa ya tagayyara ya koma wawa maras basira, wato ya ɓakalce, ya kuma kacace, saboda mayar da ƙarya sana’a. Bugu da ƙari, mawaƙin ya ƙara da  cewa, ƙarya ba abu ce mai kyau ba, don haka barin ta shi ne alhairi ga mai aikata ta, ba don komai ba sai don a zauna lafiya a kwantar da fitina ta yi bacci.

Zaɓen Tumun Dare

Ko shakka babu, al’ummar Hausawa na ganin duk wanda ya maid a ƙarya sana’a ya jingine gaskiya gefe ɗaya, to, kamar wanda ya yi zaɓen tumun dare ne, wato ya ɗauki mara ‘ya’ya ya bar mai ‘ya’ya, ma’ana ya bar hanya madaidaiciya ya kama muguwa. Makaɗa Aliyu ‘Dandawo ya taɓo bayanin ƙarya a waƙarsa da ya yi wa Sarkin Kabi Muhammadu  inda ya bayyana cewa, kowa ya saki gaskiya ya kama ƙarya haƙiƙa ya yi aikin banza wanda ba shi da amfani. Saboda haka yake cewa, kowa ya riƙi ƙarya a matsayin madogara ba shakka ya sai rariya kuma tilas ne ta yi zuba. Ga dai abin da mawaƙin ke cewa:

Jagora:        Kway ya da gaskiya yaɗ ɗau ƙarya

Shina sanin abin banza yay yi

Godiya Tafidan maiduka

 

1.     waƙa: ‘Dan Hassan madogara

 


Mai dama da hauni ka yi jinkiri

Ka gadi Muhammadu shirinka ya zo daidai

Rashin Tabbas

Hausawa na cewa, ƙarya hure take ba ta ‘ya’ya, haka ma komai nisan jifa ƙasa za ta sauka. Ba shakka ƙarya abu ce da ba ta tabbata, komai daren daɗewa gaskiya za ta bayyana kowa ya fahimce ta. Makaɗa Aliyu ‘Dandawo ya kawo wani ɗan waƙa da ke ƙara tabbatar da illar ƙarya na rashin tabbas a rayuwa, don haka kauce mata da riƙon gaskiya shi ne kawai mafita, yana mai cewa:

Jagora:        Wakilin magani Abubakar ya gwada hali

Haƙiƙa ba ya son wani sai kai

Ya riƙa da gaskiya, ya san ƙarya ba ta tabbata

Yara:           Don shi ya ƙi ta yab bi gaskiya

Bai san kowa ba duniyag ga bayan sarki

Narambaɗa ya kawo irin wannan illa ta ƙarya a wasu ɗiyan waƙoƙinsa da ya yi wa Alƙali Abu na rashin tabbata da kuma warwarewa a duk lokacin da aka ƙulla wani al’amari da ita. Ga abin da mawaƙin ke cewa:

Jagora:      A ɗauki batun mai gaskiya

Yara:        Mai ƙarya komi yah hwaɗi

Kamin a jima ta walwale

G.waƙa:   Ya ɗau girma ya ɗau yabo

Mu zo mu ga Alƙali Abu

Haka ma a waƙar da ya yi wa Tudu ƙanen Amadu yana cewa:

Jagora:    Kyawon al’amari inda gaskiya ciki

Komi a kai duniya

Yara:       Ita ƙarya ba abin yi ba ta

Ramen ƙarya ƙurewa yakai

G.waƙa:   Tudu madogara

Tudu maza-maza

Gawartacce ƙanen Amadu

 

Rasa Rayuwa

Kasancewar ƙarya mummunar ɗabi’a da haddasa gaba da fitina a cikin al’umma da kuma zubar da mutunci da darajar mai yin ta, ya sa wasu ke ganin illarta har ya kai ga iya salwantar rayuwar masu aikata. Sarkin kotson Kano Alhaji Abdurrahman ya rera wa Sarkin Musulmi Alhaji Abubakar III wata waƙa, inda mawaƙin ya nuna tsananin aibin ƙarya da cewa har ma kisa tana yi ga mai yin ta ya rasa rayuwarsa baki ɗaya. Ga dai abin da mawaƙin ke cewa:

 

Jagora:      Mai ja da kai ƙarya ta kashe shi

Sarki mai ja da kai ƙarya ta kashe shi

Yara:         Mai ja da kai ƙarya ta kashe shi

G.waƙa:    Abubakar ya i da nuhinai

Sarkin Musulmi ya wuce wasa

KAMMALAWA


A lokacin da al’amurra suka sukurkuce a tsakanin al’umma musamman abubuwan da suka shafi lalacewar zamantakewa da tattalin arziki da tarbiyya da gaskiya da makamantansu, za a ga cewa tushen zaman rayuwar jama’a ne ya sukurkuce. Saboda haka, wannan takarda ta mayar da hankali ne wajen bayyana wa jama’a illolin ƙarya a rayuwar Hausawa ta yau da kullum daga bakin makaɗan baka daban-daban na ƙasar Hausa da suka haɗa da zubar da mutunci da rashin samun taimakon jama’a da rashin tabbas a rayuwa ko warware duk wani abu da aka ƙulla da ƙarya, da wawantar da mai yin ta da zaɓen tumun dare da ma salwantar rayuwa idan ba a yi hattara ba. Saboda haka, Hausawa su farga su kauce wa sharrinta na ire-iren waɗannan musibu ko illoli da ka iya biyowa bayanta domin rayuwarsu ta zauna lafiya.

 

MANAZARTA


Abba, M, da Zulyadaini, B.   (2000) Nazari kan waƙar baka ta Hausa. Gaskiya

Corporations Limited, Zaria.

Bunza, A.M. (2005)  “Arashi shi gogi baƙauye: Nazarin karin maganar arashi da

ke jikin motoci”.Takardar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani, sashen

koyar  da  harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu ‘Danfodiyo, Sakkwato.

Bunza, A.M. (2006) Gadon Feɗe Al’ada. Tiwal Nigeria Limited Surulere Lagos.

Bunza, A.M. (2009)  Narambaɗa. Ibrash  Islamic  Publications  Centre  Limited

Surulere Lagos.

Birniwa, H.A. (2005) “Tsintar  dame a kala: Matsayin  karin  Magana  a  cikin

waƙoƙin siyasa”. Cikin ‘Dunɗaye Journal of Hausa Studies, No 2, Jami’ar

Usmanu ‘Danfodiyo Sakkwato.

‘Danyaya, B.M. (2007) Karin maganar Hausawa. Makarantar Hausa, Sokoto.

Gusau, S.M. (1996) Jagorar nazarin waƙar baka. Fisbas Media Services Kaduna.

Gusau, S.M. (2003) Jigon nazarin waƙar baka. Benchmark Publishers Kaduna.

Gusau, S.M.  (2008)   Waƙoƙin   baka  a  ƙasar   Hausa: Yanaye-yanayensu  da

          Sigoginsu. Benchmark Publishers Limited, Kano.

Nahuce, M.I. (2008) “Karin Maganar  Hausa a rubuce”. Kundin  digiri  na  biyu,

Jami’ar Usmanu ‘Danfodiyo, Sakkwato.

Tudunwada, Y.Y.  (2006)  Hausa  a  Dunƙule  na  ɗaya. Triumph  Publishers       Company Limited, Kano.

Yahya, A.B. (1997) Jigon nazarin waƙa. Fisbas Media Services, Kaduna.

www.amsoshi.com

Post a Comment

0 Comments