Daga
Aliyu Muhammadu Bunza
Sashen Koyar da Harsunan, Nijeriya
Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua, Katsina
Jahar Katsina, Nijeriya
Bismilaahir Rahmaanir Rahiimin
Wa sallal laahu alan nabiiyil karim.
Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai. Tsira da aminci su dawwama ga fiyayen
masoyin Allah shugaban bayin Allah Muhammad ɗan Abdullahi (SAW) da iyalan
gidansa da sahabbansa da waɗanda suka yi koyi da su ya zuwa ranar sakamako.
Gabatarwa:
Da Allah na nufin bayinSa da rahamarSa da baiwarSa sai Ya turo musu manzaninSa
da littattafanSa cike da saƙonSa domin raya zukatan waɗanda suka yi imani. Yin
haka wata ishara ce ta kwaɗaitar da mu, da mu duƙafa ga koyo da neman sani mu
da iyalanmu da ‘yan uwanmu domin idan ba ilmi hankalin tuwo kaɗai bai isa
shiryar da mai shi zuwa ga tafarkin tsira ba. Fafitikar karance-karancen da
almajirai da malamai da ƙungiyoyin addini daban-daban ke gudanarwa shi ya
haskaka zukatan mutane suka yarda da wajabcin neman ilmi. Samun kai ga nasarar
wannan faɗakarwar ita ce ta tara mu yau a garin Yabo, Allah Ya yi muna jagora.
Fa’idar
Karatu:
Babbar fa’idar karatu ga ɗan Adam ita ce, ya gano ba shi ya yi kansa ba yin sa
aka yi. Dalili kuwa komai toroƙan da yake yi da sunansa da ya ɗaukaka a fagen
karatu kowace iri cikin tazara yake ga abubuwan da ilminsa bai kai can ba.
Tabbas! Allah kaɗai ya gewaye komai da ilmi. Sanin mutun ya gane wani ɗan abu
kawai ya sani wasu bai san su ba, wani karatu ne cikin faɗar mahaliccinmu cewa
komai Ya sani. Duk kururuwan da ɗan Adam ke yi na ci gaban fasahar karatu da
rubutu da sarrafa shi cikin nasara a fannonin rayuwa daban-daban, masani komai
cewa ya yi bai ba mu komai daga cikin saninSa ba face ɗan kaɗan. K’a’idar ilmi
ke haska wa ɗan Adam cewa dole akwai manufa ga wanda ya halicce shi a kan
halittar da ya yi masa. Wannan tunanin zai yi canjaras da nassin ba mu halicci
aljanu da mutane ba, don komai face don su yi wa mahaliccinsu bauta. Idan
zuciyar karatu ta yi nasarar tabbatar da wannan ba za ta musanta saƙon
mahaliccinta ba ta hannun kowa ya turo shi. Yadda ba ka san lokacin da aka yi
ka ba, ba dole sai ka san wanda za a turo da saƙon yadda za a yi bautarsa ba.
Cikin wannan haske muka gano a kowace irin al’umma Allah Ya turo manzanninSa da
saƙonSa na a kaɗaita shi ga bauta a kafirce wa masu fito-na-fito da dokokinSa ɗagutai.
Ba don hasken karatu ba, abu ne mai wuya wata dabba daga cikin dabbobin bangon ƙasa
ta yi imani da abin da ba ta taɓa gani ba, ba ta taɓa jin labarin wanda ya yi
ido-ido da abin ba, kuma a zamaninta ba ta taɓa ganin wanda ya ga abin ya ba ta
labari ba. Wannan shi ne kirarin da Allah ke yi bayinSa muminai a farkon “Surar
Raƙuma”.
Allah Akbar! Cikin wannan martabar ne aka zaɓa muna Musulunci ya zamo
addininmu. Aka zaɓa muna Muhammad (SAW) manzaonmu. Aka saukar da Alƙur’ani ya
zama muna jagora. Aka cusa hikima da basira da wadataccen hankalin a ƙirjin
Manzonmu Muhammadu (SAW) domin ya yi muna fashin baƙin kuramen nassoshin zancen
mahaliccinmu. Aka arzuta Muhammadu (SAW) da mabiyan da ba a taɓa samun irinsu
ba gabaninsa, a bayansa har ya zuwa yau ba mu ji labari ba. Ilminsu ya sa suka
yi adawa da duk wanda ya yi adawa da ilmin da Manzo (SAW) ya zo da shi komai
kusancinsa gare su a jini ko soyayya ko siyasa. Bisa ga haka aka yabe su ga
tsanantawa ga makafirta da rahama ga juna. Aka ɗebe tausai da jinƙai a
zukatansu zuwa ga duk wanda ya yi adawa da Manzo (SAW) da saƙon da ya zo da shi
yana a raye ko a mace! Waɗannan su ne ɗaliban ilmi na sunna na farko a haka
suka rayu, a haka suka yi shahada.
Fa’idar
Karantarwa:
Allah da Ya saukar da hasken karatu shi Ya ba da umurnin a yi tunatarwa domin
koyar da bayinSa. Ba don koyarwa ba da ilmin addininmu ya tuƙe daga sahabbai.
Mahaliccinmu Ya umurce mu da mu je gun masana mu koyi abin da Ya sanar da su.
Wanda ya koyar da alheri zai samu sakamakon duk wanda ya aikata alherin. Don
haka, ladar iyaye da suka tarbiyartar da ‘ya’ya da malaman da suka koyar da su
Allah ɗai ke iya ƙididdige ta. Koyarwa kamar haihuwa take, idan ba haihuwa
duniya ta gama ƙarewa tun gabanin wannan ƙarni. Haka yake idan ba a koyarwa da
koyo da jahilci ya isa ya ƙare al’umma a yi zuwan sunge duniya. Alƙur’ani ne
babban manhajar koyarwa domin Allah Ya ce, ba a ‘boye komai a cikinsu ba. Ta
tabbata shi littafi ne wanda ya bayyana komai. Mai son ya san komai dole ya
tunkare shi. Wanda bai san Alƙur’ani ba a wajen Allah ko da haƙora yake rubutu
saboda ilmi jahili ne. Wanda duk aka koyar ba da Alƙur’ani ba an wahalar da
shi. Wanda duk aka koyar da Alƙur’ani ya huta an huta da shi. Ilmin duk da bai
yi canjaras da na littafin Allah ba, jahilci ne mai kai mai shi ga hauka
tuburan.
A Gyara
Yau Don Gobe:
Irin garaɓasar da ke tattare da ilmin da amfanonin da ke ƙunshe ciki ga wanda
ya yi sa’ar samunsa, ya zama dole mu tashi tsaye ganin yaranmu sun same shi.
Musibar da ke ci muna tuwo a ƙwarya ta fifita boko da addininmu ga yaranmu ita
ta kai mu ga halin da ƙasarmu take ciki. Wautar da magabata da muka yi da
girmamar da baƙin haure ‘yan ta’adda shi ne tushen ta’addanci da ke wakana a
yau. Miƙa tarbiyar yaranmu ga hannun waɗanda suka ƙaurace wa tarbiyar da Allah
Ya zaɓa musu su, shi ne musabbabin ɗurƙushewar tarbiyarmu da ta yaranmu.
Tsinkayar haske cikin ɗakin da Allah Ya ce duhu ke ciki shi ne dalilin
dunduminmu da yaranmu a yau. Kyautata hanyoyin da Allah ya ‘bata shi ya kai mu
ga faɗa wa hanyoyin ‘bata a yau. Zaton da muke yi na ganin wayonmu ya isa ya
tsirar da mu, shi ya sa aka sallaɗo muna abin da muka haifa da kanmu su zama
fitina ga rayuwarmu.
Yadda za mu sha kan duk waɗannan musibu shi ne, mu gyara yau don gobe. Yadda za
a gyara yau, shi ne a shagaltar da yara ga karatun addininmu da yi wa littafin
Allah hidima da hardace shi da lugude shi a zukatansu ya yi langaɓu a
harsunansu su samu abin yin munajati da Ubangijinmu domin Ya tausaya muna cikin
tausayinSa. Da kwalayen digiri da manyan takardun shaidar boko ke gyara al’umma
da Amerika da Ingila da Rasha da Jamus da ƙasashen Asiya ba su koka a kan
tarbiyar yaransu ba. K’arni ɗaya da ya gabace mu a Nijeriya ta Arewa babu mai
dogiri. Ku gaya mini ta’addanci nawa aka samu a lokacin?
A ƙarninmu hatta da karen ‘buki da biri da buzuzu an ba digirin digirgir amma
zama lafiya ya buwaya safe duk gara jiya da yau. Yaran jiya su ne manyan yau.
Na yau manyan gobe. Na gobe, su ne sabbenen jibi. Na jibi, a gata, su ne ranka
ya daɗe. Na gata da citta, kama-kunnen na shekaran jiya ban da jiya ne, kun ko
san duk gefen da sanuwar gaba ta sha ruwa nan ta baya za ta tsoma bakinta. Ku
bar rena shekarun yaranku da wayonsu, idan ba ku ilmantar da su littafin Allah
ba sai sun zama muku barkonon tsohuwa. Ku tambayi raƙumi da ya rena kunama ya
take ta me ya ji? Shi da kansa ya ce: “Ana shaggu ƙasa”. Allah Ya tsare mu Ya
tsaras muna. Amin!
Lokacin
Abu A Yi Shi:
Hausawa sun ce, lokacin abu a yi shi. Duk ƙwazon koyar da yaranmu addini da
tarbiya da gina ƙasa, ba zai ci nasara ba idan maƙiyansu sun rinjaye su. Halin
da muke ciki a yau ƙasarmu na buƙatar addu’a ga kowa da kowa. A fagen zaman
lafiya tura ta riga ta kai bango. Ko ba a faɗa ba mun kai ƙarshen tika-tika
tik! Haƙiƙa mun shiga halin ɗaka zufa, waje sanyi, gado kazunzumi zani ga ƙyeya.
Manyanmu sarakunanmu da malamanmu da shugabaninmu na siyasa da sana’a sun
tabbata allonmu ya cike da rubutu, mun kai gaɓa ta ƙare karatu a fagen zaman
lafiya an kai sin-waw-raa-taakuri. Yau ko muna son a ci gaba da karatun zama
lafiya mun tabbata an kai, walan waladaina walaa malam na ƙiya. Me ya rage gare
mu, mu ‘yan saura da ke raye gabanin a turo muna ‘yan uwanmu a laƙume mu, a
tarwatsa wuraren ibadojinmu, a yi wa kaburan iyayenmu da kakaninmu fitsari, a
shiga farautarmu ana kisa irin na CAR. Ga dukkanin alamu yaƙin BOKO HARAM yanzu
aka sa hannu. A fashin baƙin kalmar BOKO HARAM duk wanda ya kaɗaita Allah ya yi
imani da ManzonSa (SAW) ya miƙa wuya ga dokokinSa, a fassarar Nijeriya shi ne ɗan
BOKO HARAM. Don haka, ruwa na ƙasa sai ga wanda bai tona ba. Gabanin a fito wa
kusa Hausance, dole ne duk wanda ya yi imani da kalmar laa ilaaha illal laahu
Muhammadur rasuulullaahi ya fara tunani yin hijira gabanin zaɓen 2015 domin ga
dukkanin alamu manyan yau sun ce:
Cikin biyu sai a zaɓi guda a ɗauka
Walau tashi walau a bi Annasara.
In dai mu zaɓi tashi bayan ƙarni ɗaya mu dawo in da sauran zuriya. In ko mu
zauna zaman bayi da baƙin haure a cikin ƙasarmu ta gado. In ba haka ba, mu
tashi tsaye mu ga an ba kowa ‘yancinsa da haƙƙinsa da mutuncinsa na zama ɗan ƙasa.
Ni a ganina zama lafiya ya fi zama ɗan sarki. Da a yi ƙunar baƙin wake, gara a
yi twa-da-twa wankin ɗan kanoma mashaya a hura wuta kowa ya ga rabonsa. Yaya za
a hura wuta? Ku biyo ni.
Naɗewa:
Idan ba a ɗatu da yaro to a ba shi daddawarsa. ‘Yan siyasarmu da ke da sauran
hankali da suka ga an mayar da Arewa mayanka. Masalatanmu sun koma maƙabatar.
Kasuwanninmu sun koma fagen arbatu. Gidajenmu sun koma kangaye. Ma’aikatunmu
sun koma maɓuyar ƙadagaru da macizai. Yankinmu an yi kusan a kore shi daga ƙasarmu
mu san inda dare ya yi muna sai suka fara tunanin sauya sheƙar siyasa abin kuwa
ya fara tasiri. Irin wannan yaƙi shi ne yaƙin ilmi, yaƙin fahinta, yaƙin
zamani, yaƙin kifi na ganin ka mai jar homa. Wanda duk ya ɗaura ɗamarar irin
wannan yaƙi a yau ya cancanci mu naɗa shi kwamandan ƙwato wa masu haƙƙi haƙƙinsu.
A kan wannan nike cewa, yau a Sakkwato ba mu da zaki da makaye da garnaƙaƙi da
zagi da jagora irin mai girma Gwamnan Jihar Sakkwato, Alhaji Dr. Aliyu
Magatakarda Wamakko Sarkin Yamma Sakkwato da ‘yan majalisarsa na gida da na
tarayya. Fatarmu Allah ya ba ku nasara, ya ƙarfafa ku, ya jiɓinci al’amarinku.
Mun gode. Dalilin wannan hasashe nawa shi ne falsafar malamin kiɗa Naranbaɗa da
ya ce:
Jagora: Da mai hashin wuta
: Da mai kashin wuta
: Da mai rabon hwaɗa
: Da mai haɗin hwaɗa
: Su duk huɗu sun taru sun game
: Ba mu samu guda wanda yaf fi ba.
Yara: Narambaɗa komo ga gaskiya
: Mai kashin wuta ya fi mai hashi,
: Mai rabon hwaɗa ya fi mai haɗi,
: Ni kan ga irin wadda nag gani,
: Ka san jimina ta fi zarɓi
: Babban guru ko tai masassara.
Jagora: Ta tababta gwarzon uban gida
: Namijin jiya ka zarce ‘yan uwa.
Na gode, Allah Ya yi muna jagora ƙasarmu ta zauna lafiya. Amin!
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.