KUNDIN BINCIKEN NEMAN DIGIRI NA FARKO (B.A HAUSA) WANDA AKA GABATAR A SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR USMANU ‘DANFODIYO, SAKKWATO.
SATUMBA, 2016
BABI NA UKU
TSARIN GUDANAR DA BINCIKE
3.0
Shimfiɗa
Wannan aiki an yi amfani da muhimman hanyoyin gudanar da
bincike da aka amince da su, a tsarin gudanar da bincike irin wannan. Kashi na
farko na waɗanda ake aiki a kan su, su ne ‘yan siyasar jam’iyyu da magoya
bayansu, sai Ƃangare na biyu masu goyon bayan jam’iyyunsu tare da sojojin baka.
Hakan ya haifar da amfani da waɗannan hanyoyi kamar haka:
3.1
Wuraren da Bincike ya Shafa
Harshen Hausa shi ne harshen hulɗa a arewacin Najeriya tun zamanin turawan
mulkin mallaka. Harshen ya daɗe yana taka rawa matsayin ya fi yawan jama’a da
samun gatan kayayyakin karatu da amfani da shi wajen koyarwa a makarantu da
amfani da shi a gidajen rediyo na ciki da wajen ƙasar nan. Bugu da ƙari an daɗe
ana gudanar ayyukan gwamnati a majalisun dokokin jahohi na arewacin ƙasar nan
da shi. Wannan ne ya sa dole ‘yan siyasa daje neman shugabacin jama’a gudanar
da yaƙin neman zaƂensu a cikin harshen. Bayan tasirin harshen akwai kuma yawan
al’umma masu jefa ƙuri’a daga jahohi sha tara (19) na arewacin ƙasar nan baya
ga Hausawa da suka watsu a kowanne saƙo da kungu na ƙasar. Ko a jahohin da ba
Hausawa ba ne gaba ɗaya a arewacin Najeriya, harshen Hausa ya kasance shi ne
harshen hulɗa a tsakaninsu al’ummomin, domin kyautatuwar jagoranci na wani
muhimmin makami ne na samar da ci gaban al’umma a ƙasar, musamman a arewacinta.
Kamar yadda taken bincikenmu ya nuna muhallin da za a gudanar da aikin, wato
Arewacin Najeriya mai ɗauke da jahohi goma sha tara (19) wanda a cikinsu yankin
da ake kira ƙasar Hausa yake shimfiɗe. Don ƙara sannin inda aikin ya gaba yana
da kyau mu kawo wuraren daa ake cewa ƙasar Hausa a arewacin Najeriya, da ke
binciken ya ƙunshi Hausa ne da Hausawa na Arewacin ƙasar nan kan irin Karin
harshen ‘yan siyasa wurin. ƙasar Hausa gungun ƙasashe ne daban-daban da suka
kasance ƙarƙashin sarkuna daban-daban waɗanda ke ƙunshi mutanen da suka
babbanta ta fuskoki da dama Harshe kawi da suke amfani da shi ya haɗa su. A
arewacin Najeriya wuraren da suka zama cikin ƙasashen Hausawa su ne Daura da
Kano da Rano da Zamfara da Kebbi da Katsina da Zazau da
Gobir da Garin Gabas waɗannan ƙasashe ne da akaa fara samun Hausawan asali haka
kuma, daga nan ne al’adun Hausawa suka fara samuwa suke yaɗuwa ƙabilu da
garuruwa waɗanda suke da’awar Hauawa ne ayau (Adamu 1978: 1-2).
Sakamakon rarraba jahohi ne waɗannan garuruwa na sama suka kasance a cikin wasu
jahohi na Arewa ke nan.
Daura da Katsina = Katsina
Rano da Kano = Kano
Zamfara = Zamfara
Gobir = Sakkwato
Zazzau = Kaduna
Garin Gabas = Jigawa
Sakamakon wannan bayani daga masana da yadda taken aikin mu ya nuna waɗanna
wurare sune muhallin gudanar da binciken mu tunda ya
ƙunshi Hausa ne da Hausawa kawai.
3.2
Adadin Bayanan da Aka Tattara
A wannan Ƃangare za mu duba yawan irin maganganun da ‘yan siyayar arewacin
Najeriya aka samu nasarar tattarawa a yayin gudanar da wannan bincike wajen
amfani da aro da ƙirƙira a cikin kalmomi ko kalami da jimloli ko sashin jimla
don cimma burinsu da yaɗa manufarsu da tallata gwanayensu na siyasa a wannan
rukini.
Yawan kalaman ‘yan siyasar da wannana bincike ya iya samowa a wuraren da aka
samu damar ziyarta na arewacin ƙasar nan, an raba su zuwa gida uku kashina na ɗaya
waɗanda aka faɗaɗa ma’anar Kalmar asali, kashi na biyu kuma wanda aka ƙirƙira
daga kalmomin asali, kashi na ukun kuma wanda aka sarrafa kalmomin aro. A kashi
na ɗaya wato wana aka faɗaɗa ma’anar Kalmar asali muna da guda goma (10), a
kashi na biyu da aka kira ƙirƙira daga kalmomin asali akwai guda goma sha
takwas (18), kashi na ukun kuma mai laƙabin sarrafa kalmomin aro na guda
ashirin da ɗaya (21). Adadin wuraren da aka fara amfani da su a arewacin
Najeriya ya shafi jahohin Kano da Sakkwato da Zamfara da Jigawa, wato a inda
aka fara amfani da su kafin su watsu zuwa sauran jahohin arewa gaba ɗaya ko ma
ƙasar gaba ɗaya.
3.3
Hanyoyin Tattara Bayanai
Wannan aiki an yi amfani da muhimman hanyoyin gudanar da
bincike da aka amince da su, a tsarin gudanar da bincike irin wannan. Kashi na
farko na waɗanda ake aiki a kan su, su ne ‘yan siyayar na Arewaci Najeriya.
Hakan ya haifar da amfani da waɗannan hanyoyi kamar haka:
3.3.1 Hira/Tattaunawa
An gudanar da hira da tattaunawa dam asana masu hulɗa da kuma masu harkoki da
suka danganci rukunin jama’ar da ake aiki akai musamman sojojin baka da suka fi
taka muhimmiya rawa wajan samar da waɗannan kalamai a rukunin, wasu an gana da
su ta ido na ganin ido wasu kuma ta hanyar waya domin neman ƙarin bayani a kana
abin da ya shige mana duhu. Ga jerin sunayen waɗanda aka yi hira da su:
1. Ali Baba Agama Lafiya Fagge, a ofishinsa da ke Fagge layin bola ranar 2 da 3
ga watan Afrilu, 2016 (Asabar da Lahadi)
2. [an Bilki Kwamanda, a ofishin Ali Baba dake Fagge layin bola ranar 9 da 10
ga watan Afrilu, 2016 (Asabar da Lahadi).
3. Aminu Black Gwale, a jan bulo gidan Sani Dawaki Gabasawa ranar ranar 16 da
17 ga watan Yuli, 2016 (Asabar da Lahadi).
4. Abdulrashid Sani Dawaki, magatakardan jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar
Gabasawa a duk lokacin da ake neman ƙarin bayanin abin da ya shige duhu.
5. Hajiya Binta Sayyadi a ofishin Ali Baba da ke Fagge layin bola ranar
9 ga Afrilu 2016 (Asabar).
3.3.2 Lura ta kai-Tsaye
An ƙara samun tattara bayanai ta hanyar kura da irin yadda sojojin bakan nan da
‘yan siyasa suke gabatar da wani bayani a filin yaƙin neman zaƂe ko a wata hira
da ake yi da su a kafafen yaɗa labaru, an lura da yadda abubuwan da suke gudana
kai tsaye na daga jama’ar wannan rukuni.
3.3.3 Karanta Wallafaffun Ayyuka
An yi amfani da bayanan da aka samo ta hanyar karance-karance daga littattafai
da mujallu ko maƙalu da kundaye da aka samu a ɗakunan karatu.
3.3.4 Kafar Yaɗa Labarai
An tattara bayanai masu yawa ta hanyar sauraren zantukan ‘yan siyasa a rediyo
da talabijin, kafin zaƂuka da bayan zaƂuka daga 1999 zuwa 2016 a jahohin arewan
ƙasar. Haka an kalli kalmomi wasu mawaƙan siyasa suka yi amfani da su a wannnan
rukuni da suka shafi aikin mu, bugu da ƙari mai binciken ya yi amfani da
masaniyar da yake da ita na wasu kalmomi dan kasncewarsa Bahaushe kuma mazaunin
wani yanki na
Areawcin ƙasar nan.
3.4
Yadda Aka Tatatro Bayanai
An tattaro bayanai ta hanyar zuwa da kai wuraren da aka gudanar da binciken,
wato jahohin Kano da Sakkwato da Zamfara da Jigawa an samu wasu kuma ta hanyar
bayan na ziyarci wuraren da aka ambata daga baya aka samu saƙonus.
Haka kuma an tattara bayanai ta amfani da wallafaffun ayyuka a ɗakin karatu
wajen gudanar da wannan binciken, daga ciki akwai ɗakin karatu da ke jami’ar
Usmanu [anfodio a Sakkwato da na jami’ar Bayero da ke Kano. An duba kundayen
bincike na neman digiri tun da na ɗaya har zuwa digiri na uku waɗanda suke da
alaƙa da ta kusa da nesa da wannan aiki da amfani littafai da mujallu da ƙasidu
dam asana daban-daban suka rubuta musamman waɗanda suke da nasaba da wannan
aiki.
Sannan anyi amfani kafar sadarwa ta intanet wajen tattaro bayanai masu alaƙa da
aikin mu.
3.5
Yadda Aka Sarrafa Bayanai
Ra’in da za a yi mafani da shi don sarrafa bayanai shi ne wassafawa, ta hanyar
yin amfani da hanyoyi uku fitattu da ke kawo bayanai dalla-dalla, kuma a cikin
jadawali.
3.5.1 Kalma ko Kalami
A cikin wannan tsarin jadawalin ƙarƙashen kalma ko kalami za a samar da irin
kalmomin da kalamai na ‘yan siyasa da suke amfani da su a rukunin su na ‘yan
siyasa tsakaninsu da juna kai tsaye. A taƙaice wannan sashe ya ƙumshi Hausar
‘yan siyasa da za a nazarta.
3.5.2 Ma’ana ta Asali
A ƙarƙashin wannan jadawali ne kuma za a faɗi asalin Kalmar ko kalamin don nuna inda ta samo asali
Bahausheya ce ko ƙirƙirar ta akai ko a’a faɗaɗa ma’anar akai a wannan rukuni na
‘yan siyasa . Wannan ma’ana ta asali tana nufin ma’anar da kowa na iya fahimta
ko wadda ake amfani da ita yau da kullum.
3.5.3 Sabuwar Ma’ana
A ƙarƙashin wannan kuma za a kowa sabuwar ma’anar da wannan rukuni na ‘yan
siyasa suke amfani da ita wadda ta babbanta da ma’ana ta asali da kuma yadda
aka saba amfani da ita a cikin sadarwa ta yau da kullum.
3.6 Naɗewa
A cikin wannan babi mai taken tsarin gudanar da bincike an duba adadin bayanan
da aka tattara da hanyoyin tattara su da kuma yadda aka yadda aka tattaro
bayanan da yadda aka sarrafa su a cikin wannan aikin na mu.
2 Comments
[…] HAUSAR ‘YAN SIYASA A AREWACIN NIJERIYA (BABI NA UKU) […]
ReplyDelete[…] ci gaba da karatu […]
ReplyDeleteENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.