𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam da fatan an wayi gari lafiya? Shin mutum zai iya kashe tsaka da ruwan zafi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa
rahmatullahi wa barakatuhu.
Tsaka dabba ce mai nau'in ƙadangare amma ba takai kadangare girma
ba, kuma tafi rayuwa a cikin ɗakuna.
Ya halatta a kashe tsaka
saboda illolinta ga lafiyar Ɗan
Adam da kuma zamantakewar yau da kullum, kuma saboda Annabi (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya kirata da suna "FASIQAR HALITTA". Kuma ya yi umurni da
kasheta ta hanyar bugu ko sokewa da mashi.
Imamu Muslim ya ruwaito
hadisi acikin Sahihinsa (hadisi na 2,238) ta hanyar Nana A'ishah (radhiyallahu
anha) cewa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi umurni da kashe
tsaka.
Hakanan acikin Sahihul
Bukhariy hadisi na 3359 wanda aka ruwaito ta hanyar Ummu Shareek (radhiyallahu
anha) ta ce "Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi umurni arika
kashe tsaka ya ce "Domin ta kasance ita ce ta hura wutar nan (wacce
kafirai sukayi nufin Qone Annabi Ibrahim da ita).
Addinin musulunci Addini ne
mai tsafta da son zama lafiya, don haka ne ya shar'anta mana wasu ababe da suka
halatta mutum ya kashe su daga ciki ma akwai wanda idan ka kashe kana samun
lada, daga cikin waɗannan halittu akwai tsaka!
Wacce Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kira ta da cewa lallaifa ita tsaka
algun-guma ce wacce kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya tabbatar mana
da cewa lallaifa dukkan wanda ya kashe tsaka a duka guda ɗaya
rak! To yana da lada ɗari (100).
Amma dangane da hukuncin
kashe tsaka ko duk wani kwaro ko dabba ta hanyar amfani da ruwan zafi, wannan
kam bai halatta ba, saboda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya hana
yin amfani da wuta domin azabtar da wani abu ko kashewa. Shi kuwa ruwan zafi
tamkar wutar ne.
Daga cikin hujjoji akwai
hadisin Sayyiduna Abu Hurairah (radhiyallahu anhu) wanda Imamul Bukhariy ya
ruwaito akan lamba ta 3016. Abu Huraira ya ce "Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya ce "BABU MAI YIN AZABA DA WUTA SAI ALLAH".
Sannan Imam Abu Dawud ya
ruwaito hadisi acikin Sunanu nasa akan lamba (2675) cewa watarana Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) yaga wani gidan tururuwa wanda wani daga cikin
Sahabbai ya Qoneshi da wuta, sai ya ce "KADA WANI YA YI AZABA DA WUTA SAI
UBANGIJIN WUTAR"
Don haka abin da ya yafi kyau
kuma yafi daidai da addini shine duk abinda akayi umurni da kisansa, to ka
kasheshi ba tare da amfani da wuta ko ruwan zafi ba. Misali kamar maciji,
kunama, tsaka, kudin cizo, kwarkwata, rina, shanshani, cinnaka, da sauransu.
Yazo acikin wani hadisi
wanda Imamun Nawawiy ya kawoshi a cikin Arba'una hadeethan Annabi (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya ce "IDAN ZAKUYI YANKA TO KU KYAUTATA YANKAN, HAKANAN
IDAN ZAKUYI KISA KU KYAUTATA KISAN".
Domin korar tsaka a gida, ka
nemi gishiri ka gauraya da garin tafarnuwa ko danyar tafarnuwa sai ka watsa a
duk inda kake yawan ganin ta a gidanka, tsaka za ta bar wajen a cikin gaggawa.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.