Ticker

6/recent/ticker-posts

Tsakanin Sufaye Da Tauhidi

Duk wanda ya san Alƙur'ani ya san cewa; Tauhidin da Alƙur'ani ya yi umurni da shi, kuma Manzanni suka zo da shi, suka kira mutane zuwa gare shi, shi ne kaɗaita Allah da bauta, a magana da aiki, a bayyane da ɓoye.

Allah ya ce:

﴿۞ وَٱعۡبُدُوا۟ ٱللَّهَ وَلَا تُشۡرِكُوا۟ بِهِۦ شَیۡـࣰٔاۖ ﴾ [النساء ٣٦]

Kuma ya ce:

﴿وَمَاۤ أَرۡسَلۡنَا مِن قَبۡلِكَ مِن رَّسُولٍ إِلَّا نُوحِیۤ إِلَیۡهِ أَنَّهُۥ لَاۤ إِلَـٰهَ إِلَّاۤ أَنَا۠ فَٱعۡبُدُونِ ۝٢٥﴾ [الأنبياء ٢٥]

Ya ce:

﴿وَلَقَدۡ بَعَثۡنَا فِی كُلِّ أُمَّةࣲ رَّسُولًا أَنِ ٱعۡبُدُوا۟ ٱللَّهَ وَٱجۡتَنِبُوا۟ ٱلطَّـٰغُوتَۖ﴾ [النحل ٣٦]

Allah ya aiko Manzanni da yawa zuwa ga mutanensu, kowanne daga cikinsu cewa yake yi:

﴿یَـٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُوا۟ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَـٰهٍ غَیۡرُهُۥۤۚ﴾

"Ya ku mutanena, ku bauta ma Allah, don ba ku da wani abin bauta wanda ba shi ba".

 

Don haka haƙiƙanin Muslunci shi ne kaɗaita Allah da bauta. Ma'ana; bayi su kaɗaita Allah da aiyukansu, na addu'a, roƙo, neman taimako, neman biyan buƙata, neman agaji, neman yaye bala'i, da yanka, bakance, tawakkali, soyayya, tsoro da "raja'i", da sauran aiyukan bayi na ibada, kada su yi su ma kowa sai ga Allah shi kaɗai, ba tare da sanya masa kishiya da abokin tarayya ba.

Amma idan ka kalli aiyukan Sufaye, na roƙon matattu, da neman agaji a wajen waliyyai, da rataya zukata da shehunnai da duƙufa a ƙabarbura, za ka tabbatar da cewa; lallai waɗannan mutane ba su ma san amfanin zuwansu Duniya ba.

To wannan duka abubuwa ne da suke nuni zuwa ga saɓawar Sufanci ga Addinin Muslunci.

✍️ Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)

 Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Post a Comment

0 Comments