Article Citation: Aliyu Muhammadu Bunza (2020). Wane Ne Farfesa A Farfesance? (Hannunka Mai Sanda Ga Magabata, Hayya! Ga Mabuƙata, Kashedi Ga ‘Yan Kallo). DEGEL: The Journal of the Faculty of Arts and Islamic Studies, Vol. 18, No. 2. ISSN 0794-9316
WANE NE FARFESA A
FARFESANCE? (HANNUNKA MAI SANDA GA MAGABATA, HAYYA! GA MABUƘATA, KASHEDI GA ‘YAN KALLO)
Na
Aliyu Muhammadu Bunza
Tsakure
Muƙamin Farfesa shi ne, mataki na ƙarshe da ɗalibin ilmi zai kai ya yi fice cikin fagensa.
Muƙami ne da sai an ratsi farfajiyar duniyar karatu mai
tsawo gabanin a same shi. Wannan takarda ta yi yunƙurin lalubo fassarar kalmar
ita kanta daga harshen da aka samo mata sunan “Ingilishi”. An ɗan yi bayanin daɗa juna sani da masana Hausa suka yi gabanin su tsayar da
kalmar “Farfesa” a Hausance. An mayar da hankali gadan-gadan a kan yadda
Bahaushe ke son ya ga Farfesa, ya ji Farfesa. Haka kuma, an kalli Farfesanci a
matsayin ire-iren abubuwan da ya kyautu a ce, Farfesa ya sa ƙwazo a kansu domin tabbatar
da martabar kujerar Farfesa. Aka sake ɗauraye takardar da ɗan ƙaramin fasalin da ya yi daddage sosai a kan tabbatar da
muƙamin kujerar ita kanta. A yunƙurin kafa hujjoji da
tabbatar da su, an gayyato fitattun mawaƙan baka 7, marubuci 1, an sarrafa ɗiyan waƙa 11, an narka ƙissoshi 10, kirari 1,
da ƙaƙale 1, domin nagartar da hujjojin da aka sussuka. Haƙiƙa, yadda aka san kujerar
Farfesa a da, a yanzu, kama da wane ba wane ba ne. Matsalar durƙusawar ilmi ruwan dare game
duniya ne, kowa na da hannu a ciki, sai an taru a gyara. Da dai za a kafa wasu
mujalloli na tarayya da za a keɓe wa Farfesoshi kawai, kuma
a tilasta ganin shawagin kowa a ciki da dole nakiya ta yi zaƙi. Idan aka ƙara da keɓe wa farfesoshi rana ɗaya kowace shekara, da za su gabatar da
gagarumar lacca da za ta fito da ɗan wani abu sabo da suka hango, da abu ya yi. Matuƙar hukuma ba ta tuba da yi
wa ilmi ta’addanci a kasafin kuɗi ba, manyan kujerin ilmi
ba za su kafu da ƙafafunsa ba. Ga alama, rashin hasken fitar ba laifin
gwalab ba ne, laifin batir ne.
Gabatarwa
Buƙatar kowace rayuwa ta kai matuƙa ga muradin sha’awarta.
Labudda kowane mutum akwai abin da ya gada, ko abin da ya yi haye, ko abin da
ya koya. Gurin ɗalibin Alƙur’ani ya kai ga “dogon
alif maƙarar basin”. Kowane uba fatarsa ɗansa ya gaje shi. Matuƙar ba a ce wa ɗan galadima “sarki” ba, buƙata ba ta biya ba. Babu
wani ɗan sana’a da ba ya burin ya
yi wa tsara fintinkau ya sarauce su. Lallai yin nasarar kai buri ke sa a
tattaro ‘yan’uwa da abokan arziki a yi bukin mun gode. Shekarar da Narambaɗa ya samu muƙamin malamin waƙa (wato kamar Farfesan Waƙa) ya ƙago bakamdamiyarsa ga yadda
ya yi walimarsa:
Jagora:
Ko waz zaka kallo ya karkaɗe kunnenai,
Yara:
Ga makandamiya za ni yi cikin manyan waƙoƙi
Jagora:
Na jiya Jankiɗi
Yara:
Ya yi tai uwar waƙa sai nai tau
Jagora:
Na jiya Zamau
Yara:
Ya yi tai uwar waƙa sai nai tau
Jagora:
Na jiya Gurso
Yara:
Ya yi tai uwar waƙa sai nai tau
Jagora:
Na jiya Akwara
Yara:
Ya yi tai uwar waƙa sai nai tau
Jagora:
Na jiya Ɗandawo
Yara:
Ya yi tai uwar waƙa sai nai tau
Jagora:
Na jiya Nagaya
Yara:
Ya yi tai uwar waƙa sai nai tau
Jagora:
Dodo malamin waƙa kundumin magajin Ɗanɓaidu
Yara:
Ya yi tai uwar waƙa sai nai tau
Jagora:
Kullum ji nikai azanci na hudo min
Yara:
In wani ya hi ni martaba ni kau na hi wani
Jagora:
Ai kyan mafarauci
Yara:
Ya ɗau kare ya kiyaye yah hi
Jagora:
Shi dillali
Yara:
Da an saya ya hwaɗi ad daidai
Jagora:
Shi ko arne
Yara:
Ya kama noma daidai an nan
Jagora:
A sai mai kwando
Yara:
Ya barbaɗe taki ad daidai
Jagora:
Shi makaɗi kau
Yara:
Shi gyara turu daidai an nan
Jagora:
Ni kan kun gane ni
Yara:
Na gyare turuna
Jagora:
Sai zuba waƙa nikai
Yara:
Kama da ta Alfa Zaazin[1]
Gindin
Waƙa: Gwarzon shamaki na Malam toron giwa
:
Baban Dodo ba a tamma da batun banza.
A ma’aunin malaman addinin Musulunci na
Afirka ta Yamma, duk wani yabo baya ga na Annabi Muhammadu (SAW) yake. A fagen
yabon Annabi (SAW) “Ishiriniyar” Alfa Zaazi ta cancanci kujerar Farfesa. Don
haka, kowane mawaƙin Hausa ke burin zama Alfa Zaazi.
Zubin Karatun Allo Da Boko A Ƙasar Hausa
Karatun boko a ƙasar Hausa cikon sunna ne
makaho da waiwaya, domin ko da iska ya zo ya tarar da kaba na rawa. Boko ya
tarar da mu da iliminmu na addini da duniya da littattafai da fasahar karatu da
rubutu da bincike cikin harsunanmu. A tsarin karatun addininmu, idan yaro ya
iya Fatiha zuwa “Alam Tara” a baki da ƙidan baƙi, sai a dafa wake a yi
walima. Idan ya turza ya kai “Sabbi” sai a yi masa walima da tuwo. Idan yana
fara wa kansa rubutu kowane hizo za a yi masa walima da tuwo. Da ya kai “Ƙuluhiya” sai a yanka
bunsuru. Idan likkafa ta ci gaba ya kai “Ƙaala” rabin Alƙur’ani sai a yi babbar
walima ta cikin gida. Da ya soma dafa “Bara’atu” sai babban bunsuru na a zo a
gani. Idan ya kai dogon “Alif” sai zayyana da gangamin bukin babbar sauka
muradi ya samu, ya samu lasisi karatun Alƙur’ani sai a naɗa masa babban rawani, digiri ya samu[2]. In ya hardace
ya zama “Alaramma”.In ya rubuta da hannusa ya zama “Gwani”. In ya goge ya kai
matsayin gyara wa Gwani rubutu ya kai “Gangaram”, kwatankwacin Farfesa ke nan a
karatun biɗar tuwo. Na so a ce wa
Gangaram “Shakundun” da Hausa ya zamo shi ne ƙarshen mukamin karatu na
addini da na boko.
Da gaba ta koma baya, boko ya yi wa karatun
addini idon marurugiya, e-bi-ci-di ta yi wa a-ba-ja-da wayo da sunan gurgusa in
zauna abu ya koma gurguza ba ni wuri. Da yaro ya kai shekara bakwai za a kai
shi aji ɗaya har shekara bakwai. A
yi bukin ba shi takardar iya karatu da rubutu. Daga nan sai makaranta ta gaba,
a shekara biyar, a ba shi takardar shaidar sanin gari da ƙara karatu. Daga sanin gari
yana da zaɓi uku: in dai ya je Jami’a,
ko Kwalejin Koyan Koyarwa, ko Kwalejin Kimiyya da Ƙere-Ƙere. Ɗayan biyun ƙarshe duk ya je zai share
shekara uku gabanin a yaye shi. Idan Jami’a ya je kai tsaye tsakanin shekara
(4-5) a ba shi digirin farko. Komai saurinsa sai ya shekara (1-2) ya je
digirin ƙwarewa (Masters). A al’adance za a yi shekara (1-3) a
samu digirin. Daga nan in a yi zagege (ta Ɗanfulani) in ko a tsaya a
huta. Duk yadda aka yi sai an shekara (3-5) za a samu digiri na uku (PhD). Da
samun digirin PhD komai ƙwazo ana share shekara (6-10) gabanin a hau kujerar
Farfesa.[3] Matuƙar kowace tasha ana tsayi a
huta, sai an share shekara (40-45) ana wasan kura da takardun boko gabanin a
hau kujerar Farfesa.
Ma’anar Farfesa
Malamanmu sun yi kai da kawo wajen fassara
wannan kalma cikin Hausa. Na tabbata ɗan share fagen da ya gabata ya ɗan ba mu haske yadda wahalan noma gandun yake. Wasu
masana suna fassara kalmar da “Shaihin Malami”. Masu taka tsan-tsan ga shiga
cikin kadadar addini su fassara ta da “Shehin Masani” . Da baya-bayan nan wasu
masana suka hausantar da ita zuwa “Farfesa” kawai. Rashin kalmar a ƙamusoshinnmu na Hausa ba
zai rasa alaƙa da cewa baƙuwa ce ba.
A Turanci asalin kalmar daga “Profess” yake
wadda ke da harshen damo a fassara. Tana ɗaukar ma’anar bayyanar da wani abu (da ya shafi mai
bayyanarwa) shi kansa, ko iƙirarin samun wani horo ko koyo ga wata sana’a ko abin
sha’awar mutum. A fassarar fannu sun ce:
Ingilishi: “A teacher of the higher grade in a
University or College, or in an institution where professionals or technical
studies are persued; usually an officer holding a chair in some particuler
branch of higher institution”. (The New International Webster’s Comprehensive
Dictionary of the English Language)
Hausa: “Malami mai gawurtaccen matsayi a Jami’a ko
kwaleji ko wata Cibiya (-r karatu) da ake horar da ƙwararru ko karatun
fasahohin hannu;musamman (ana fassara shi) ma’aikaci mai riƙe da wata kujerar alfarma a
wani sashe na musamman a manyan cibiyoyin zurfafa karatu”.
A bisa bayanin masu abu Farfesa shi ne,
fitaccen malami, sananne, gawurtacce wanda ke saman kujerar shakundum a
farfajiyar da ya yi artabon karatu da bincike. In ya kai babin murabus ba ya da
abokin gwada tsawo, daga ɗa sai jika, sai kama kunne,
bai fasa ba, bai kasa ba, sai a ƙara wa kujerarsa ƙwari zuwa “Emeritus”. Masu
abu cewa suka yi:
Ingilishi: Emeritus[4]: Retired from
active service (as an account of age), but retain in an honorary position,
postor Emeritus. (Webster’s Comprehensive Dictionary of the English Language)
Hausa: Kartagi shi ne wanda ya yi murabus don rage
nauyin aiki (musamman idan shekaru sun fara karɓar shara) amma aka ci gaba da riƙe shi bisa ga martaba shi,
kartagin Pasto.
Ga alama kujerar Farfesa ba a son gara ya ci
ta, matuƙar yana raye, ko da idanu da ƙafafu sun yi masa tawaye,
muddin yana ji ana jinsa, da shi da hankali ba su fara hararar juna ba,
kujerarsa na nan daram! Mannanu ƙuda ya faɗa ƙwaryar alewa.
Farfesa A Farfesance
Hausawa na cewa, kowa ya ci zomo ya ci gudu.
Don haka wasu ke ƙara wa batun gishiri da faɗar zomo ba ya kamuwa daga kwance. Duk Bahaushen da ya ji
irin shekarun da ake sharewa ana kokuwa da boko kafin a zama farfesa, dole ya
ce, ba a wane bakin banza. Matuƙar ƙwazon ya dace da sunan to za mu ce, Farfesa:
i. Soja ne tsakanin mazaje, namiji ne a ko’ina ake zancen
maza, su ma mazan da kansu za ka ji sun ce: “Soja maza”. Ga yadda wani soja ya
fassara batun:
Sannun
ku soja maza tsakanin mazaje,
Sannunku
masu kashi da wawan gidaje,
Ku ɗai ka kwanci kan ƙasa ba gadaje,
Sauro
shi ciza ga kiyashi, ƙudaje,
Manya
wajen ladabi, wajen bin umurni.
(Kaftin
U.D. Suru: Nijeriya Ina Muka Dosa (1986) b+24)
ii. A fagen suna da fice, Farfesa kwatancin “Shago” ne a
fagen fama. Da an gilma sunan “Shago” babu namijin da za ya sake kirari. Yadda
duk Shago ya zama:
Jagora: Samji irin hakin da ka ramno,
: Burundumi abin zuba shara,
: Kutuɓi abin aza ma ruhewa,
: Lahira a kai maki gawa.
(Ɗan’anace: waƙar Shago)
A fassara Bahaushe haka farfesa yake, kuma
haka yake son ya ga ya kasance. Da ya zo a wuri gardama ta ƙare.
iii. A fassarar Bahaushe farfesa uban ‘yan boko ne, da ya zo
al’amari ya kai ƙarshe, kamar yadda Ɗanƙwairo yake ce wa, Sir
Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato:
Jagora: Namiji uban ‘yan boko,
: Amadun Amadu mai tawakkali gun Allah,
: Baban mai saje,
Gindi : In ba ka nan maza suka ƙarya su ce, “maza ne”,
: In ka taho uban Ajiya kowa bai motsawa,
Gindi : Mai dubun nasara tarnaƙaƙi Sardauna,
: Ba a kai maka wargi....
(Musa Ɗanƙwairo: Waƙar Sardauna)
iv. Na tabbata Bahaushe abin da yake kallo
farfesa a farfesance shi ne, wata “aya” ta ƙarshe ga boko. Haka kuma,
yana kallon ta wata irin kadada ga ilimin boko da an kai gare shi an tuƙe, idan ganɗon ya fashe kuwa sai kowa ya yi ta kansa. Na
kwatanta shi da irin hangen da Narambaɗa ke yi wa sarkin Gobir Amadu yana cewa:
Jagora: Ganɗo kake ran da kaf fashe,
: Rannan sai ka iske kowa na dawara,
: Ruwa sun cika karkara,
Gindi: Na rabu da ganin amali yau na zaka in
ganai
: Daɗin Tudu ya kamata daɗin Tudu hanƙuri.
Babu wai, irin yadda Bahaushe ke kallon
farfesa kamar yadda ya ke kallon limamin garinsu ne ko unguwarsu. A boko, yana
ganin farfesa liman ne domin shi ne ƙarshen e-bi-ci-di. Na tuna, wata shekara, mun
je garin Ƙaurar Namoda ɗaurin auren ‘ya’yan Khalifa Maahi. Liman na zuwa tare da
jama’arsa kowa na a bayansa sai maba/sanƙira ya hau baki da yi wa liman kirari:
“Dudduƙe Maguzawan Allah,
Azumi babbar gayya,
Komi girman mutum guda yaka ɗauka,
Allahu akbar! Haka muƙamin Farfesa yake, komi
tsufan mutum guda aka bashi.
A Ji Farfesa A Ga Farfesa
A wajenmu ɗalibai koyaushe muna son mu ga mai suna irin na karatu
da ɗalibta ya karɓi sunansa da muƙamin da aka ba shi. Ba dole
ne sai ya gamsar da kowa ba, amma ko da ba a samu gamsuwa daga gare shi ba, ba
za a yi wa maganarsa turbuɗar mushen jaki ba. An so
Farfesa ya ɗan siffantu da waɗannan siffofi da ake zaton a samu a wajensa.
i. Ya san da cewa, muƙamin Farfesa fara karatu ne aka yi, yanzu aka
sa ƙafa, ka ce dai manomi ne ya haɗa babban gona ga taki da iri da sungumi na shuka yana
jiran a samu ruwa a yi shuka. An ce, wani malami ya ce, ya zama farfesan sanin
halin mata, ya kwashe shekara (40) yana bincike ga sakamakon da ya samu:
Bayan ya kwashe shekara arba’ain yana
binciken sharrin mata ya rubuta kundaye manya-manya. Ya zo wani ƙauye, ya je rijiya ya sha
ruwa. Ya tarar da wata ‘yar yarinya ko budurci ba ta fara ba. Ya nemi ta ba shi
ruwa, ta yi masa kallon raini. Malam ya husata ya ce: “Ke tun ba a haifi uwarki
ba nake binciken makircin mata, karɓi kundayen nan ki kai wa kakanki ya fassara miki”. Ta ce:
“In gani baba!” Ya miƙo mata gafakar tana gefe ɗaya na rijiyar. Yana sakar mata ta jaye hannu kundayen
suka yi alkafura cikin rijiya tsundum! Ta ce, wayyo! Baba ka iya wannan[5]? To, Farfesa a
lura. Ashe dai cika baki da bugun gaba da karatu bai hana jahili ya ribace ka
ya dabirta karatunka. In mun san da haka ga kowa muna koyo kuma ba mu ce wa
kowa mun iya.
ii. Yarda da cewa, ga kowa ana koyo. Kana koyo ga ɗanka da abokinka da yayanka da ƙanenka da ɗalibinka da ɗalibin ɗalibinka. Samun kujerar ba
hujja ba ce ta rufe karatu ba da cewa an fi kowa. Dubi ka-ce-na-ce tsakanin
yaran Firamare da ƙwararrun injiniyoyin hanya:
An ce, wasu injiniyoyi suka je wani gari da
motar cire itace. Ƙofar ganuwar garin ta hana su shiga domin motar ta yi
tsawo. Suka share wuni suna tunanin yadda za su yi, can suka yanke shawarar a
fashe ƙofar ganuwar motar ta wuce, in an ƙare aiki a gyara. Lebarori
na batun fara aiki sai ga yara ‘yan Firamare sun taso ƙwallo, suka ce: “Ah!Ga mota
ba wurin wucewa”, sai wani ya ce: “In ni ne, zan fasa ƙofar”, wani ya ce:
“Ni ɗaga motar zan sa a yi”. Can
sai wani ya dube ta da kyau ya ce. “In ni ne zan sace tayoyinta ta huce (sace),
a nemo mai faci ya sa iska”[6]. Ƙwararrun injiniyoyin na jin
haka suka bi shawarar yaro suka ci nasara. Farfesa a kula. Ashe Farfesa matakin
sanin yadda ake bincike ne, da ɗurkusa wa wada a tashi da cikakken tsawo. Kushe abokan
aiki da hana wa ɗalibai bin fassarar kowa
sai taka alamun rashin sani ne.
iii. Farfesa ya sani cewa, saninsa ba hujja ce ta ƙaryata wani ko wasu ko da a
kan kuskure suke. Abin sani ga Farfesa shi ne, amfani da saninsa ya gyara kuren
wani cikin nishaɗi da annashawa da tawali’u.
Dubi yadda Sarkin Wawan Sarkin Katsina ya yi da telansa:
Wawan Sarkin ya ba tela ɗinki an sha yi masa ƙarya, ya zo ya karɓa in ya zo ba a ƙare ba. Da aka yi masa alƙawalin ƙarshe ya dako sabko, tela
na hangensa sai ya shige cikin kayan da aka kawo ɗinki aka jibga masa su aka lulluɓe shi. Ashe an manta ba a rufe yatsun ƙafarsa ba. Da Wawan Sarki
ya shiga ɗakin ɗinki suka ce: “Baba tela ya je kasuwa ya nemo
zaren da zai yi maka aiki ka je an jima ka dawo”. Ya tsaya ya dubi kayan ɗinki ya ga ƙafar tela a waje ya ce: “To
babu laifi, a dai cika alƙawali, kuma in ya dawo ku gaya masa ba ya da kyau dattijo
na tafiya da ƙafa ɗaya a kasuwa, ya dinga zuwa
da ƙafafunsa biyu mana”[7]. A gaida
Farfesa Wawan Sarki. Ta tabbata gani a ƙi gani, ji a ƙi ji, wata babbar sifa ce
ta ma’ilmantan duniya, Ƙure mutum a tozarta shi, ba karatu ba ne tashanci ne a
dai bi a hankali, da wasa aka gaya wa wawa gaskiya.
iv. Dole Farfesa ya san, ana dafa kafaɗarsa a fi shi tsawo. Wanda ka koyar ya zo da wata basira
cikin basirar da ka koyar da shi, kai Allah bai ba ka ba. Godiya ya kamata ka
yi ba ɓata rai da kuka za ka yi
ba. Dubi ƙissar malami da matarsa da almajirinsa ka ƙara karatu:
Malami ne ya fita zuwa zauren karatu bai ci
abinci ba. Ya bayar a gasa masa zakara. Zakara ya gasu, ga jama’a sun taru, ga
malam na jin yunwa. Matarsa ta ce wa ɗalibansa: “Wa zai yi dabarar gaya wa maigida zakara ya
nuna”? Ɗaya daga ciki ya ce, zai yi. Ya je zaure ya tarar jama’a
tinjim, kuma duk irinmu ne almajirai masu tambaya. Sai yaro ya durƙusa ya aje allo a gaban
malam ya ce:
Yaro: Malam Zakarutu ya nun naam!
Malam: To, a sarkafe shi ga tankallazii,
: Hatta jama’atu Watseem![8]
Farfesa a nan wane ne malam? Wane ne ɗalibi? Haka ake son mu kasance, ba mu dinga
tunzuri idan ɗalibi ya zo da hazaƙa ba. Ai da riga da abinda
ke aljihun riga, duk na mai riga ne. Da kara da dagumi duk albarkar farautar
kura ce.
v. Zuga da kirari da yabo ba su sa Farfesa ya wuce saninsa.
Duk abin da ba ya iyawa zai yi tsaye ya zama ɗalibi sai ya san shi. Da yabo da kushewa duk ba su sa ya
ci mutunci martabar ilimi. Karatun malam Gambo da Farfesa Manu Dahin Gumbire
abin lura ne. Manu ya shahara ga sata. Ga abin da suka yi da Gambo:
Jagora: Ɗan Dahi Manu,
:Wanga da ag Gumbire dauri,
: Ko bataliyas soja tas shiga daji,
: In gaya maka Manu Dahi na ɗan taya ta,
: Yac ce min:“Mis samu Gambo?”
: Nac ce, “Tudu Tsoho yat taɓa ni,
: yac ce: “Maganar banza da yohi”,
: In akwai ta da daɗi ka je da kanka
: Ai ba mu tsar ma tambaya ba”.[9]
Farfesa Manu ya yarda gaba da gabanta ya rufa
wa kansa asiri, yau ga mu muna amfana da fatawarsu. Haba Farfesa! Duk mai ganin
iliminsa ya kai yana gwada tsawo da kowa ba Farfesa ba ne farfesu ne. Hattara
da kayan Allah! Da zarar ka ga abin da ya zarce ɗan abin da ka sani, tsaya nan ka sauke kayanka ka ɗalibce shi sai ka iya shi ka yi magana kansa.
vi. Ya kasance mai hankalin amfani da ilimi wajen gyaran
matsalar ilimi, ba da cin fuska da cin zarafi da muƙabala da bugun gaban wa
mutum nan. Ya kyautu Farfesa ya san tunatar da ɗalibi da mai ilimi cikin ilimi, wani haske ne na karatu
da ke amfanar mai gyara da mai kuskure.
An ce, wani cikakken malami a Masar ya je
aikin Hajji da ɗalibansa. Ba su taɓa ganin Ka’aba ba. Da ka’aba sai suka rungume
ta suna kuka. Suna shafarta suna sumbata. Abin ya koma bautar ɗakin ba bautar Allah ba. Da wani ƙwararren shaihin malamin
tauhidi ya gan su sai ya ɗauki Alƙur’ani, ya je gun shaihin
neman a koya masa karatu da fassara; ya ce: “Allah Ya taimaki malam, a taimake
ni da fassara wannan aya”: “Fal ya’abuduu Rabbu haazal baiti.” Shehi ya fassara
masa da cewa: “Ku Bauta wa Ubangijin wannan ɗaki”. Sai Shehin ya ahumo ya kira ɗalibansa ya ce: “Ku zo mu gyara” “Rabbu
haazal baiti” aka ce, ba “haazal baiti ba”. Daga nan suka daina abin da suke,
suka ci gaba da ɗawafi yadda shari’a ta
tanada[10]. Tabbas!
Muna da aiki baya. Fatar Farfesa koyaushe a gane, a gyara, a ci gaba, ba a
tabka muƙabala da gardandami ba. Wanda duk ya ce, kowa bai iya ba,
shi ne bai iya ba.
vii. Ƙwararren Farfesa shi ne mai yarda da
fassararsa da ta waninsa, matuƙar ba su ci karo da sawaba ba. Wanda ya yarda duk abin da
ya sani wani ya san saɓaninsa ya huta da ɗirkaniya, mota cikin randa. Wani Shehi ya yi
wa jama’a nasiha da su riƙa kyauta da sadaka. Ya gaya masu cewa: “Ku sani rubuce
yake, in ka ci ya ƙare, in ka ba wani ya ƙare, in ba ka ba wani ba
ya ƙare”. Jama’a kowa ya gamsu sai Ɗankama ya ce: “Akwai gyara
ga hadisin malam, fassarar nan ba ta lugudu ba”. Malam ya so ya yarda sai
jama’a suka yi caa kamar su cinye Ɗankama. Sarkin gari ya ce: “To, kai kawo taka
fassara mu jiya” Ɗankama ya ce: “In ka ci ya ƙare, in ka ba wani ya ƙare, in ba ka ba kowa ba ka
daɗe kana cin abinka”[11]. Me za ka ce
da wannan Farfesa? Matuƙar da hankali za a yi aiki, Farfesa a taka sannu.
viii. An so Farfesa ya kasance mai cikakken wayo da ƙoshin ilimin tunkarar
kowane ilimi ya bijiro masa. Da iliminsa zai yi amfani ya kuɓutar da kansa da wani ya ceci al’umma.
Labarin ɓarawon maƙullin mota da direba abin
lura ne:
Wani fitaccen ɓarawo ne ya dami mutanen Arkilla Federal low coast,
Sokoto. Ya sha sace wa direbobi maƙullan mota da dare ya je ya buɗe ya sace abin da ke ciki. Wata rana ya ɗauki maƙulli wani yaron Alwasa. Yaron mai wayo ne, da
ya tabbata yaron ne ya sace maƙulli, kuma ya gan shi cikin aljihunsa. Idan aka ta da
rigima zai iya jefa shi wani wuri ya ɓace. Tsoro haka ya sa ya kira ɓarawon gefe ɗaya. Ya zaro naira hamsi ya ba ɓarawon ya nuna masa wata kwana ta unguwar mai nisa ya ce:
“Ga yaron da ya sace min maƙullin motata can ya shiga kwanar can, je ka ƙwato min abina ka ci goron
naira hamsin”. Da jin haka sai ɓarawon ya ruga da gudu ya shiga kwanar ya dawo da maƙulan a hannunsa ya ce: “Ga
su, su ne waɗannan? Abdullahi Alwasa ya
ce: “Su ne na gode”[12].
Da ƙasar Turai ne aka yi haka,
ba abin mamaki ba ne a kira direban a ba shi kyauta ko wata jami’a ta ba shi
digirin girmamawa. Madalla! Ashe a tasha ma akwai masana da manyan Farfesoshi.
A kowane lokaci Farfesa ya shiga wata matsala ya nemo masu hannu a abin, ya
nemi ilmi wurinsu kana iya sa tasa basira abu ya je tangam.
ix. Koyaushe a dinga tsantseni wajen yanke hukuncin ilimi.
Wannan wata dama ce da za su daina nuna wa mutane sun iya ko da sun sani. A
al’adance gwani ko ya san abu yana so ya ji ta bakin abokin tattaunawa. Domin
Hausawa cewa, suka yi.“Ko ɓata ƙara sanin daji ne”. Ƙissar wani malami da ya
bugi ƙirjin cewa, in yana raye ba a ƙara musun kwanan wata wani
babban darasi ne:
Musu ya kaure a masallaci kan kwanan wata
domin a tantance tsayuwar Ramalana. Da musu ya tsananta, sai wani malami ya
tashi ya gaya wa jama’a cewa, in yana raye ya ɗauke wa kowa ganin wata da tantance kwanakinsa. Bayan an
yi ittifaƙin yau ɗaya ga wata, ya je gida
ya ɗauko burgamensa ya rataya
shi a rumfar ƙofar ɗakinsa. Kowace rana ta
Allah sai ya ɗauko tsakuwa ɗaya ya jefa a ciki. Ashe ɗiyarsa ta lura da cewa, kowace asuba malam in
ya dawo da salla sai ya jefa tsakuwa ɗaya burgame. Halinka da yaro, sai ta dinga taya shi, a
koyaushe ta lura ya jefa sai ta laɓaɓo da nata cike da ɗan hannunta ta jefa. A kwana a tashi gardama ta sake
tashi kan tsayuwar wata. Malam ya ce: “Ku bari in zo an gama”. Ya je gida ya
sauke burgami ya ƙyarga ya ga wajen (80-100), ya sake rairayewa ya tsame
(50-60) ya sake ɗebe wasu ya fitar da
(30-40) ya zo masallaci ya ce wa jama’a:“Yau kwanan wata (35)”, aka bushe da
dariya. Ya ce:“Da na gaya maku abin da burgamina ya faɗa ai za ku sha mamaki[13].
Danƙari! Ashe gaskiyar Bahaushe da ya ce: “Kowa
ya ce, ya ce, sai ya ce, bai ce ba”. Idan haka karatu da bincike suke, don me
ba za mu rage doro da taƙama ba? Da duk aka yi bugun gaba da ilmi sai ya ba mai
shi ruwa.
x. Farfesa ilimi amana ce ka daina ɓoye wa mai koyo shi, kada ka yaudare shi da
shi. Duk abin da za a koyar ga ɗalibai ka tabbatar da gaskiya ce, a gaban kowa ya ambace
shi ba za a muzanta shi ba balle a yi masa dariya. Na tuna da labarin wani
Resdan Bature da yaronsa mai kula masa da dokinsa:
A kowace rana Resdan na cire kuɗi ya bayar domin a kula masa da dokin da yake
hawa. Yaro yakan je ya ce: “A kawo kuɗin ciyawa, a kawo na gyaran linzami, ko ƙaimi ko na gyaran turke da
na tur!” Duk Bature ya bayar. Da Bature ya ji Hausa sosai sai ya je fadar sarki
ana cikin taɗi ya ce, yana son a gaya
masa abin da ake ce wa tur!” Kowa ya kasa, ya gaya wa sarki cewa, a kira masa
yaron da ke kula da dokinsa ya san kalmar, aka kira shi a fada. Ya faɗi ma’anar kalmar “tur!” Sai turu-turu da
idanu[14]. Da aka gano
yaudara ce sai aka dinga yi masa kirari, “Adaɗe ana yi” sai ya ce: “Sai gaskiya”. Dukkanin abin da ya
koyar da Resdan a nan ya zuba saboda samun cin amanar ilmi ɗaya na kalmar “tr” da ba ta a Hausa. A kula
duk abin da aka koyar da yara girma zai zo musu kuma za su tuna da shi. In
gaskiya ce a koyaushe girmanka na a zuciyarsu. Idan kuwa na akasin ta ne, kai
ka zubar da girmanka da kanka.
xi. Farfesa masani ne mai ilimin hangen nesa tare da kiyaye
karatun yau a tunkari na gobe. Wannan ce ta sa a koyaushe ba a girshinsa a
fagen karatu, domin da tambaya yake tunkarar mai tambaya, har sai tambaya ta
fito da amsar wata tambaya a kasa wata tambaya ta gaba. Saƙon Yakubu Gawon zuwa ga
Sarkin Musulmi Abubakar III da tambayar sarkin Gwandu Haruna wani babban kundin
karatu ne.
A zamanin mulkin Yakubu Gawon ya samu labarin
ana son a yi masa tashintashina a hamɓare gwamnatinsa. Ya aika wa Sarkin Musulmi Abubakar III
cewa, a tara sarakuna su shirya talakawa a yi zanga-zangar goyon bayan gwamnati
domin a samu damar kama masu son su yi ba-mu-so a hukunta su. Sarkin Musulmi ya
kira taron sarakuna, wakilan gwamnatin tarayya suka hallara a taron, da sarki
ya karanto saƙon shugaban ƙasa, sai ya ce: “Abdullahin Gwandu (cewa da
sarkin Gwandu Haruna) me kuka gani?” Sarkin Gwandu Haruna ya ce: “A gaya wa
shugaban ƙasa cewa, Mai Martaba Sarkin Musulmi ya ce:“In suka sa
talakawa zanga-zangar ‘muna so’ idan wata rana talakawa suka yi masu
zanga-zangar ‘ba mu so’,. Wa zai kwantar da tarzomar?[15]”
Wannan tambaya har yau gwamnatin Yakubu Gawon
ba ta ba da amsar ta ba. Haka malamanmu suka ce, a koyaushe Farfesa ya yi
magana a ji ta a yi tangam, mai zuwa hajji ya gamu da Annabi (SAW).
Ba Fankam – Fankam ne Kilishi ba, Tsomi
Hausawa sun ce, “Maza tamkar gyaɗa ne sai an ɓare, za a san mai ƙwaya”. A al’adance, ba
kowane mutum ke cin sunansa ba. Babbar buƙata ga kowane mutum ita ce, idan aka ga mutum
sunansa na ɗaukaka, a ga ayyukansa da
halayensa na ɗaukaka. Ba abin mamaki ba
ne a irin ƙarshen zamaninmu a tarar da Farfesa bai cika mudun da ya
kamata a ce ya cika ba a fannin karatu. Wanda duk Allah Ya nufi aka naɗa wa wannan rawani, ya sani cewa:
1. Rawanin karatu ne na har abada babu ranar hutu har sai an
kwanta kushewa. Sunanka da rawanin da aka ba ka ba su yi wa jahili barazana sai
dai a yi taho- mu-gama. Ba a wa ilimi kwalo-kwalo da dabarar da wayon sanin
gari na shekaru. In an san abu, an san shi, in ba a san shi ba, ba a san shi
ba. A zage dantsen neman a san shi. Na yarda da hangen Marigayi Ɗantalata Maiduma Bunza,
makaɗin tauri da yake cewa:
Jagora: Ba wayo aka wa yuƙa ba,
: Ba ta da ban magana sai tauri.
Gindi : Gara da kaz zaka baban Idi,
: Dajin namu da zabbin gumbi.
Wane wayo za a yi wa kujerar Farfesa in babu
karatu kuma ba a yi shi ba? Ai sai dai karatun Baru uwa uba ga maraye, wa in
bari bari, wa in kasada kasada”.
Kama da Wane ba Wane ba ne
Kujerar Farfesa ba ita ce ilimi ba, sannan
kuma Farfesa ba shi ne ilimi ba. Zama Farfesa ba ita ce hujjar gogewa da ƙwarewa ba. Babbar hujjar da
babu makawa a kan ta ita ce, “Karatu” a tabbata an yi shi, an san shi, an saba
da shi, karatun ya zama tobashin zuciya abokin baki. Ina amfani a ce wane ya
kai, a zo da ɗan ma’auni a tarar bai kai
ba. A sake bitar tunanin Narambaɗa:
Jagora:
Ai An wa wani Alƙalin ƙasa,
Yara :
Da babu sani taw walwale,
Jagora:
Bai san amma ba, bai san sabbi ba,
Yara :
Shi dai shi tsare “min nun guda,
Jagora:
Can gaba ko “ra baguje”[16],
: Iya
kas sanin an nan.
Gindi:
Ya san girma ya san yabo,
: Mu
zo mu ga Alƙali Abu.
Ba Sunan Ba Aikin
Malaman ƙasar Hausa idan aka ce wane
ya sauke Alƙur’ani sukan ce, “ Allah ya ba da karatun tsoron Allah”.
Abin da suke nufi shi ne, ba karatun za a yi wa hisabi ranar Alƙiyama ba, mai karatun za a
yi wa. Idan an hau kujerar Farfesa ana son a ga ayyuka na ɗa’a da biyayya ga gabaci da rahama a magana
da rubutu da ƙauna da soyayya ga wanda aka sani da wanda ba a sani ba.
Da muƙamin da sunan Farfesa ke ɗaukaka mutum ba za a jin suna wani a bangon ƙasa ba face Farfesa. Aiki
mai sunan shi ke ɗagar da sunan da aiki a ji
su a duniyar zamaninsa. Wani mawaƙin mashaya giya ya yi wa wani Shaihin malami wa’azi
lokacin da Shaihi ya ce masu: “Yan wuta masu saɓo”. Shi kuwa ya mayar da raddi da cewa:
Jagora: Dan nan sai nak kada baki,
: Nac
ce malam ka yi saɓo,
: Ɗan laifinmu na shan giya
na,
:
Wansu da sata, wansu maita,
:
Wansu had da biɗar matan maƙwabta,
: Ba
allo ka ganin Ma’aiki ba,
: In
allo ka ganin Ma’aiki?
:
Shekarar bana danya ba ta toho,
: Dud
da ni sai na yi bakwai ba.[17]
(Kwara
Mairuwa: Waƙar ‘yan Birni ku yi tamataila, 1975)
Wai in don ta alluna ne kawai ke sa a ga
Annabi (SAW) ba a yi aiki nagartacce ba, to shi zai sassare itatuwan danya
gaba ɗaya, (da ita ake yin allo)
ya yi wa kansa bakwai ya ga mai hana masa ganin Manzon rahama (SAW).
Farfesanci
Farfesanci wata babbar daraja ce da ɗaukaka wadda ke tabbata wa duniya cewa,
lallai kujerar da jami’a ta ba mutum bisa cancanta aka ba shi. Daga lokacin da
aka saka ƙafa a jami’a, har lokacin da aka samu hawa kujerar
Farfesa, duk nema ake yi. Duk wani aiki da ake yi don a kai ga kujerar nan ne.
Hausawa cewa suka yi, “Ba a san maci tuwo ba sai miya ta ƙare”. Idan an hau kujerar
ana buƙatar a ga :
1. Wani sabon ƙwazonka na bincike da rubuce-rubuce da za su
tabbatar da cewa, lallai ƙwazonka ne ba kirarin matsoraci ba. Duk wata takarda ko
littafi ko bincike ya fito daga gare ka a tabbata ƙwazonka ne sabo ba ɗaurayar baya ba ce, ba damben wada ba ne.
2. Farfesanci shi ne a samu fannin da aka ce ka cancanta,
hatta da Mala’iku su shaida Allah Ya hore maka shi. Jami’arka ba ta fargaban sa
ka gaba, ka wakilce ta domin ta san ko an daka cikin turmi da ku cikin masu
fita. Ƙasarku da jiharku ba su fargaba wajen neman taimakonka a
fanninka saboda an san zancenka, nashin ƙasa ne babu kure.
3. Duk yadda zamani ya juya, in dai kana raye, ba a tababan
tura ku gaba wajen saka wa jahilci takumkumi da yi wa ilimi talala na sai baba
ta gani. Kuna zaune gida a nemo wasu ƙwararru waje kunya ne a
kanku. Ku yi tsari ya kasa karɓuwa zance ne. Ku yi nuni a
kasa ganin haske labari ne.Ku sa hannu a ce a dakata shirme ne. Ai ku ne igiya
maɗaura kaya, kowa ya yi ba da ku ba ta tsinke.
4. Hankali ba zai yarda da a ba ka tsani/kwaranga ka hau
rumbu ka ɗebo abinci ka ci, kai da
iyalanka, da ‘yan uwanka, da masoyanka, sai kun ƙoshi ka ɗauke tsanin ka ɓoye wai kar a sake amfani da shi. Ɗalibbai nawa ka yaye kuna
tare ana fafatawa? Nawa ka yi wa mafarin samun kujera irin taka? Nawa an nan
kana raino da kake son su hau munzalinka gabanin ka yi murabus ko duniya ta
kore ka da aiki? Me ka rubuta ka ajiye wa na baya domin su karanta su shahara
kamar yadda ka yi? A ɗan namu gani na ɗalibbai, Furofesanci ya fi Farfesa wuya,
domin Farfesa nawa aka fesa wa turare har suka kai ga kujerar sai sun haye su
fesa wa ɗalibai barkonon tsohuwa?
Hankali ka Gani ba Ido ba
Amfani ilimin ya saka wa mai shi hankalin da
zai iya zama da kowa, a yi hulɗar arziki da mutunci. Da
yawa, hankali na koya wa ilimi karatu, sai dai idan ilimi ya yi tambaya a raba
‘yan kallo. Da magabatnmu da mabuƙatanmu da mu ɗalibbai da ‘yan kallo mu kiyaye sosai da sanin:
· Kujerar Farfesa ba ta tsira hasada ba ce da
abokan gwagwarmaya. Tir! Da hassadar ka a ke ana barin ta kai gareta? Don me za
ka yi hasadar wani?
· Ba ta girman kai ba ce, na ganin dole sai an
duƙa maka
· Ba ta sauke karatu ba ce a dangane allo, wai
an kai walawaladaina, walam malam na ƙiya.
· Ba ta soke ƙwazon magabata ba ce, ka
fito da naka salo da sanin gari.
· Ba kujerar neman muƙamai ba ce, kujera ce ta
nema wa masu neman kujerun girma girma, mai ita sai gyashin Alhamdulillah.
· Ba kujerar kafa wata sabuwar mazhaba ba ce,
don duniya ta ji kai ma ka kai. Assha! Babu ƙira me ya ci gawai?
· Ba kujerar kirari ba ce, wai girma ya kawo
tsoro ya ɗebe. Kash! Da wa ka yi
kokuwa ka ƙwato ta.
Sakamakon Bincike da Shawara
Kowane ilimi na duniya yana da tsarin da aka
hau aka same shi. Muƙamin Farfesa da a Arewacin ƙasarmu sai ƙwara-ƙwara. A yau, saboda
yawaitar jami’o’i a yankinmu sun fara yawaita. Ina ɗan hasashen taɓarɓarewar ilimi a ƙasarmu da mummunar aƙidar nan ta cin hanci da
rashawa da maguɗi babu fannin da ya tsira
ciki a ƙasarmu. Babu laifi a samo wani tsanin da zai riƙa zaburar da Farfesoshi
su ƙara amfanin ƙasa da jama’a. A fafutukar rubuta wannan
takarda na gano cewa:
· Mafi yawan farfesoshin ƙasar nan sun manyanta
shekaru na yi masu barazana. Wane lokaci ne suka samu na kulawa da lafiyar
jikinsu da farfesanci?
· Jingar da aka biya ba ta taka kara ta karya
ba, kuɗaɗen bincike da ake bayarwa ko kuɗin rangadin bincike ba su biya, balle a tsaya a yi aiki a
wallafa shi.
· Yawan ɗalibban da ake bai wa masanan masu digirin B.A da M.A da
PhD sun yi yawa. Abin takaici an daina biyan tallafi ga masu duba ɗalibai da yawa. Wannan kisan mummuƙe ta’addanci ne ga ilimi.
· Siyasa ta shiga jami’o’i haiƙan musamman jami’o’in
jihohi da sababbi, in ba a kula ba za su ragaita kujerar Farfesa ta koma ƙarƙashin ofishin gwamna ko
ofishin Pati
· A fito da wasu gawurtattun mujallu na ƙasa da za su riƙa wallafa ayyukan
farfesoshi kawai. A yi tsaye ganin dole kowane farfesa sai an ji muryarsa a
ciki. A fito da matakan ladabi ga masu daƙilewa.
· Bayan laccar shimfiɗa Buzun karatu (Inaugural lacca) a fito da laccar
shekara-shekara ta manyan masana da kowane masani zai baje kolin wani sabon abu
da ya hango a shekara.
· Hukuma ta sa hannu ga wallafa ayyukan
farfesoshi da tallafa musu da biyansu na goro, in ana ta ciki da wane hankali
za a yi bincike.
Naɗewa
Haƙiƙa ba a san maci tuwo ba sai miya ta ƙare. Ga kowane ɗalibin sani mai ƙwazo da naci da kishin kai,
samun kujerar farfesa gare shi da al’ummarsa babbar nasara ce. Hawan kujera da
rashin cancanta wani tonon silili ne, da zubar da mutunci ga ɗan ƙuƙe-na-ƙuƙe. Ilimin da ladabi da
biyayya da hankali maƙwabtan juna ne, amfanin sani aiki da shi. Daga cikin
sirrin ilmi akwai riƙon gaskiya da fake amana da gode wa ga wanda ya azurta ka
da shi. Narambaɗa ya ce a gaya muna:
Jagora:
Duk ɗan malamin,
: Da
yaƙ ƙi biyan Allah,
: yak
kiɗe baƙi,
Yara :
To, Allah yana watse kayanai.
Jagora:
Ya kama yawo,
Yara :
Yannan gidan har ya zan kango.
Gindi :
Gagarau mai buge kangara Ali ‘Yandoto,
: Ba
shi son wargi ba a kai mai batun banza.
Manazarta
Bunza,
A. M. (1996). Baki Abin Magana, ANLAT Publishers.
Bunza,
A. M. (2009). Narambaɗa: Jerin Littatafan Cibiyar Nazarin Al’adun Hausawa,
Sahen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato. Lagos:
Ibrash Islamic Publication Center Limited.
Ɗangambo, A. (1981). Ɗaurayar Gadon Feɗe waƙa, Kano.
Ɗangambo, A. (1984). Rabe-raben Adabin Hausa da
Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa, Kano: Triumph Publishing Company.
Ɗangambo, A. (2007). Ɗaurayar Gadon Feɗe waƙa, (Sabon Tsari) Zariya: Amana Publishers
Limited.
Ɗangambo, A. (2011). “Waƙa da Rawar da Take Takawa A
Rayuwar Hausawa” (Domin tunawa da cikar shekara gomasha biyu da rasuwa
Alhaji Mamman Shata yana da shekara 76), Kwalejin Ilimi ta Tarayya da
ke Kasina ta Shirya.
Ɗanjuma, S. (1982). Rabe-raben Waƙoƙin Hausa da Tasirinsu ga
Rayuwar Hausawa:
Kano: Triumph Publishing Company.
Ɗanjuma, S. (1982). Rabe-raben waƙoƙin Hausa da Tasirinsu ga
Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph Publishing Company. The New International Webster’s
Comprehensive Dictionary, of the English Language.
Suru, K. U. D. (1986). Najeriya Ina Muka
Dosa? Rubutacciyar Waƙa da ya rera a Garmaho.
[1] Fitattun waƙoƙin Madahun Manzon Rahama
(SAW) da suka samu karɓuwa sosai a ƙasar Hausa su ne: Alburda da Ishiriniyya.
Alburda Balarabe ya rubuta ta Shehu. Ita kuwa Ishiriniya baƙar fata ya rubuta
ta ɗan Afirka da aka fi sani Albuusiirii mutumin Masar da Alfaa Zaazi. Kalmar
‘alfa’ Yarbawa da Zabarmawa na amfani da ita a madadin ‘malam’. Suna ‘Zaazii’
ya fi kusa da Zabarmanci, don haka ake kirdadon cewa, Alfa Zaazii Bazabarme
ne. Allah
masani.
[2] . Tattaunawa ta musamman da Malam
Usmanu Birnin Kabi asali Malam Usman haifaffen garin “Buma” ne ta wajen garin
Gulumbe. Karatu da karantarwa ya kawo shi Birnin Kabi tare da ƙanensa
Malam Aliyu. Na yi hirar da shi a wajen shekarar 1993.
[3] . A wasu lokuta na musamman, ana zama
Farfesa da digiri ɗaya
kacal ko ma babu digirin idan mutum ya gawurta. Waɗanda na san an ba kujerar ba su da digiri akwai: Farfesa
Neil Skinner na Jami’ar Wisconsin Amerika, ya rasu 2016, da Farfesa Haliru
Binji a Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Sashen Shari’a. Masu digiri ɗaya akwai: Farfesa Abdullahi Smith a Jami’ar Ahmadu
Bello, da Farfesa A.M.H. Kirk-Green, na Jami’ar Oxford, London; da Farfesa
Na’ibi Swaid na Sashen Larabci Jami’ar Bayero, Kano; da Farfesa Wole Soyinka na
Jami’ar Legas, waɗannan masana gudunmuwar da suka bayar ta keta
hazon duniyar ilmi sosai, ko cancnta ta san sun cancanta.
[4] . Ni na fara kiran sa da suna “Kartagi”
a garin Yakawada ta ƙasar Zazzau. Gogaggen ɗan caca idan ya manyanta ba
ya da abokin wasa, za a naɗa masa
rawanin “Kartagi uban ‘yan caca”. Wani muƙami ne na
nuna an manyanta cikin abu, an yi murabus, amma an ƙi rabuwa
da shi domin da tsohuwar zuma ake magani. Ban ce, sunan shi ya fi dacewa ba, ɗan yunƙuri ne na ɗalibai, ina son masana su taya ni gyara mu fito da sunan
da zai fi dacewa.
[5] . Na saurari wannan ƙissa
ga marigayi Sheikh Sidi Ibrahim Attahiru Sokoto, a tafsirin Alƙur’ani
da yake yi a masalacin jumu’ar da ke gidansa, a shekarar 1982.
[6] . Ina godiya ta musamman ga Dr. Nasiru
Aminu Kalgo na Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Sakkwato. Na samu
wannan bayani a yayin tattaunawarmu da shi a wajajen shekarar 2012/2013 a
ofishina.
[7] . Hira da ɗaliban makarantar malamin da na ambata a lamba ta 2.
[8] . Na ƙaru da
wannan bayani a wajen wani ɗalibina
Bakatsine da ya yi kundin digirinsa na B.A. kan Wawan Sarkin Katsina.
[9] . Da Manu bai kai matsayin Farfesa ba a
sana’arsa, zai hau tulin ƙasar da makaɗa Gambo ya tara masa, a ƙarshe
ta rutsa da shi.
[10] . Tattaunawa da wasu ɗaliban ilmi a masalacin jumu’a na garin Bunza, Masalacin
Jumu’a na 2, a shekarar 1990.
[11] . Hira da Liman Khidir bin Saleh,
Limamin Unguwar Malamai Bunza shekarar 2015.
[12] . Tattaunawa da Abdullahi Alwasa
ma’aikaci a Asibitin Masu Taɓuwar
Hankali, Kware, a gidan Alhaji Suleiman Umar Tunga Arkilla Federal Lowcost,
Sokoto.
[13] . Ina godiya ta musamman da roƙon
gafara ga marigayi Malam Yusuf Kantu Isa da ya ba ni wannan labarin a garin
Argungu, 1982.
[14] . Na samu wannan labari a fadar mai
martaba Sarkin Musulmi ga wani Yaro daga cikin yaran da ke yi wa gidan hidima,
1990.
[15] . Na yi matuƙar
godiya ga Farfesa Ibrahim Mukoshy na sashen Nazarin Harsunan Nijeirya, Jami’ar
Usmanu Danfodiyo Sokoto, ya ba ni labarin a ofishinsa, 2015.
[16] . Idan aka haɗa harufan “min” da “nun” da “raa” da “baa” za a sami “min
rabbi”. Haka, marigayi Alhaji Garba Gwandu Bazza ya fassara mini baitin a
gidansa, 1980. Sun shaidi waƙoƙin Narambaɗa kuma sun sha zama da shi da tambayarsa ma’anonin wasu
kalamai na cikin waƙoƙinsa.
[17] . Wannan fasahar ce makaɗa Gambo mai ɓarayi
ya ara ciki waƙoƙin
hululuwa, Gambo fice ya fi su. Kwara mutanen ƙasar
Geza ne, a garin Geza, ƙaramar Hukumar Dandi, Jahar Kebbi, gundumar
Argungu.
The official website of the DEGEL Jounal is https://www.degeljournal.com

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.