Jagora: Di'i Bello uban Amadu,
Alhaji Bello sadauki kake
Y/Amshi: Di'i Bello uban Amadu,
Alhaji Bello sadauki kake
Jagora: Di'i baban Talatuwa da
Amina
Y/Amshi: Sani saboda kai yaz zaka,
Alhaji Bello sadauki kake,
Di'i Bello uban Amadu
Jagora: Muhammadu ƙanen
Muhammadu Tori
Y/Amshi: Di'in da yah hi Turai
sani,
Jagora: Muhammadu ƙanen
Muhammadu Tori
Y/Amshi: Di'in da yah hi Turai
sani,
Alhaji Bello sadauki kake,
Di'i Bello uban Amadu
Jagora: Gwanjata na Birnin Kabi,
Can nika komawa in hwake
Y/Amshi: Ga manyan ma'aikatan
gwamnati,
Alhaji Bello sadauki kake,
Di'i Bello uban Amadu
Jagora: Gwanjata na Birnin Kabi,
Can nika komawa in hwake
Y/Amshi: Ga manyan ma'aikatan
gwamnati,
Alhaji Bello sadauki kake,
Di'i Bello uban Amadu
Jagora: Allah shi yima gambun
tsari,
Allah sa ka gama lafiya
Y/Amshi: Amin saboda Ɗanhodiyo,
Alhaji Bello sadauki kake,
Di'i Bello uban Amadu
Jagora: Allah shi yima gambun
tsari,
Allah sa ka gama lafiya
Y/Amshi: Amin saboda Ɗanhodiyo,
Alhaji Bello sadauki kake,
Di'i Bello uban Amadu
Jagora: Tashin ka Yalwa yai muna
zafi,
Ban san wanda zashi canjin ka ba
Jagora /Y/Amshi: Don ka gyara
gari yayi kyau,
Dakat tashi gargada tai yawa,
Alhaji Bello sadauki kake,
Di'i Bello uban Amadu.
Za mu tsaya a iya waɗannan ɗiyan waƙa ☝️☝️☝️da
muka ciro daga waƙar Injiniya Bello wani mutumen Sakkwato da ya yi aiki a
matsayin Injiniyan ayyukka a yankin Yauri wato DE/District Engineer a Turance a
cikin shekarun 1970 zuwa shekarun 1980. Wannan waƙa Makaɗa
Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri (1943-2016) ne yayi masa ita. A
maimakon DE /District Engineer sai ya hausantar da kalmar zuwa Di'i.
Duk da yake ba akan wanda aka
yiwa waƙar
bane zamu tattauna, mun dai yi amfani da ɗiyan
waƙar
ne domin fitowa da wani batu akan wani bawan Allah da za a san ko shi wanene
kuma me ya sa aka alaƙanta shi da waƙar ko mai waƙar.
Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo Yauri yayi amfani da kaifin
basirarsa wajen nuna ƙwarewar Injiniya Bello a fagen aiki inda yake cewa
"Muhammadu ƙanen Muhammadu Tori, Di'in da yah hi Turai sani".
Ya ƙara da rashin sanin makomar garinsu
Yalwa/Yauri ta fannin kikkimta masu titunan mota dake cikin garin saboda an ɗauke shi daga Yauri zuwa
Birnin Kabi a lokacin da ya yi masa wannan waƙa.
Shi ne yake cewa "Tashinka
Yalwa yai muna zafi, ban san wanda zashi canjin ka ba, don ka gyara gari yayi
kyau, dakat tashi gargada tai yawa", wato babu maintainance kenan inji
Turawa na titunan Yalwa/Yauri kamar yadda ya saba😁. Kuma bai san ko wanda
zai canje shi ya iya aiki kamar yadda ya iya ba.
Sai yayi masa roƙon
tsari da kuma wanyewa lafiya " Allah shi yima gambun tsari, Allah sa ka
gama lafiya, amin saboda Ɗanhodiyo".
Aikin mayar da titin gwamnatin
tarayya da ya taso daga Zaria ta Jihar Kaduna ya zo Funtua /Yankara a Jihar
Katsina ya zarce zuwa Tsafe/Gusau /Talata Mafara /Bakura dake Jihar Zamfara
zuwa Tureta /Dange/Shuni a Jihar Sakkwato zuwa tagwayen hanyoyi da ake aiwatarwa
a halin yanzu shi ne dalilin kawo waɗancan
batutuwa ☝️☝️☝️dake cikin wannan waƙa ta Injiniya Bello ta
Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri.
Bawan Allahn da ya kawo wannan
aiki na biliyoyan nairori ba Injiniyan tituna bane, shi ma'aikacin kuɗi ne da kishin al'ummarsa
yayi masa katutu a zuciya, yayi tsayin gwamin jaki a inda yake aiki har sai da
ya tabbatar da wannan buƙata ta samu amincewar hukumomin dake da alhakin aiwatar da
ita, aka kuma soma gabatar da aikin kafin ya ajiye aiki.
Ba kamar Di'i Bello uban
Amadu da aka canzawa wajen aiki ba, shi
kam ajiye aiki yayi gaba ɗaya.
A namu gefen ba zamu tsaya ga abin da Makaɗa
Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri yace ba, zamu yi kira da roƙo ne da babbar murya zuwa ga masu daraja
gwamnonin jihohin Kaduna da Katsina da Zamfara da Sokoto da dukan masu muƙamai
dake waɗannan jihohi
musamman Ministoci da 'yan majalisar dattawa da 'yan majalisar wakilai dama
sarakuna da sauran masu faɗa
aji su matsa ƙaimi a duk inda ya dace domin tabbatar da kammala wannan aiki
a cikin lokaci domin In Shaa Allah za a daɗe
al'umma na amfana dashi.
Tsohon ma'ajin kamfanin man fetur
na ƙasa
wato NNPCL, ɗan asalin
Jihar Sokoto ne ya zaƙulo wannan aiki domin
al'ummomin Jihohin Kaduna da Katsina da Zamfara da Sokoto musamman da
sauran masu zirga -zirga akan wannan titi su amfana daga
kwatarnin/kwatarnen/akushin gwamnatin tarayya kamar yadda ya lura takwarorinsu
na sauran sassan Nijeriya na kwankwaɗawa.
Wannan bawan Allah shi ne Alhaji
Umaru Ajiya Isa (Ajiyan Isa) gundumar Isa Jihar Sokoto. Ɗan
Ajiyan Isa Muhammadu Sada ne, shi kuma ɗan
Tafarkin Isa Aliyu ne (Tafarki Aliyu ya riƙe sarautar Ajiyan Isa kafin wafatinsa).
Gidansu na daga cikin gidaje 12
da aka kafa garin Isa tare dasu a lokacin mulkin Amirul muminina Muhammadu
Bello ɗan Mujaddadi
Shehu Usman Danfodiyo Tagammadahullah Birahamatihi wanda ya yi mulki daga
shekarar 1817-1837. Kenan tun sarautar
Sarkin Gobir na Isa na farko Malam Muhammad Fodiyo ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo.
Tun a wancan lokaci ne ake
sarauta guda 3 a gidan nasu wato Tafarki da Magagari da kuma Ajiya ya zuwa yau.
A lokacin mulkin Sarkin Gobir na
Isa Malam Umaru ɗan
Sarkin Musulmi Aliyu ƙarami ɗan
Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan
Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo ne ya umurci Tafarki Aliyu da ya zayyana sabon wurin
zama ga mutanen wani gari da ake kira Magarya zuwa inda suke a halin yanzu wato
Bargaja saboda wasu dalilai na zamantakewa, haka kuma aka yi Tafarki Aliyu
kakan Alhaji Umaru Ajiya yayi wannan aiki a cikin nasara.
A zamanin mulkin Sarkin Gobir na
Isa Muhammadu Na'ammani (yayi sarauta daga 1925-1935) aka dawo da hedikwatar ƙasar
Badarawa zuwa garin Shinkafi(a lokacin suna a ƙarƙashin gundumar Isa ne). Tafarkin Isa
Aliyu na daga cikin jagororin da suka tsara yanayin garin na Shinkafi domin ya
dace da buƙatun
zamantakewar al'umma a wancan lokaci.
Da wannan muna iya cewa Ajiya
Umaru Sada jikan Tafarki/Ajiya Aliyu duk da ba kamar Di'i /DE Bello uban Amadu
da ya karanci wannan aiki na Injiniyanci, yayi amfani da hikimar magabata wajen
ƙwato
muna aikin mayar da titin Zaria/Funtua /Gusau/Talata Mafara /Dange/Shuni
/Sokoto na gwamnatin tarayya zuwa tagwayen hanyoyi ta hanyar amfani da muƙaminsa
na Darektan kuɗi
/Ma'aji /Ajiya a hukumar kula da harkokin man fetur ta ƙasa NNPCL. Allah SWT ya
saka masa da mafificin alherinsa duniya da lahira, amin.
Daga Ajiyan Isa, Alhaji Umaru ya
samu amincewar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji (Dr) Muhammad Sa'ad Abubakar
CFR mni wanda ya naɗa
shi sarautar Ajiyan Sakkwato /Cibiyar Daular Usmaniyya. Ya hau halifar Marigayi Alhaji Muhammadu Sani Dingyaɗi wanda ya yi sarautar
Ajiyan Sakkwato a cikin shekarun 1950 kafin daga bisani ya zama Makaman
Sakkwato da kuma Marigayi Alhaji Garba Gummi wanda ya riƙe wannan matsayi na
Ajiyan Sakkwato kafin wafatinsa.
Jami'ar Jihar Sakkwato wato
Sokoto State University (SSU) ta bashi digirin digirgir na girmamawa saboda
abin da ta kira "aiki tuƙuru da sadaukarwasa a ayyukan cigaban
al'umma".
Kamar yadda Makaɗa Alh. Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri ya ce ma Di'i Bello uban Amadu muma mun ce ma Ajiyan mai alfarma Sarkin
Musulmi "Allah shiya ma gambun tsari, Allah sa ka gama lafiya, amin saboda
Ɗanhodiyo".
A wannan hoto maigirma
Alhaji(Dr.) Umaru Ajiya, Ajiyan Isa/Ajiyan mai alfarma Sarkin Musulmi ne. Allah
SWT ya ƙara
lafiya da nisan kwana mai albarka, amin.
Daga Taskar:
Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin
Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.
16/08 /2026.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.