Ticker

6/recent/ticker-posts

Injiniya Bello Sakkwato

Jagora: Di'i Bello uban Amadu,

Alhaji Bello sadauki kake

Y/Amshi: Di'i Bello uban Amadu,

Alhaji Bello sadauki kake

Jagora: Di'i baban Talatuwa da Amina

Y/Amshi: Sani saboda kai yaz zaka,

Alhaji Bello sadauki kake,

Di'i Bello uban Amadu

Jagora: Muhammadu ƙanen Muhammadu Tori

Y/Amshi: Di'in da yah hi Turai sani,

Jagora: Muhammadu ƙanen Muhammadu Tori

Y/Amshi: Di'in da yah hi Turai sani,

Alhaji Bello sadauki kake,

Di'i Bello uban Amadu

Jagora: Gwanjata na Birnin Kabi,

Can nika komawa in hwake

Y/Amshi: Ga manyan ma'aikatan gwamnati,

Alhaji Bello sadauki kake,

Di'i Bello uban Amadu

Jagora: Gwanjata na Birnin Kabi,

Can nika komawa in hwake

Y/Amshi: Ga manyan ma'aikatan gwamnati,

Alhaji Bello sadauki kake,

Di'i Bello uban Amadu

Jagora: Allah shi yima gambun tsari,

Allah sa ka gama lafiya

Y/Amshi: Amin saboda Ɗanhodiyo,

Alhaji Bello sadauki kake,

Di'i Bello uban Amadu

Jagora: Allah shi yima gambun tsari,

Allah sa ka gama lafiya

Y/Amshi: Amin saboda Ɗanhodiyo,

Alhaji Bello sadauki kake,

Di'i Bello uban Amadu

Jagora: Tashin ka Yalwa yai muna zafi,

Ban san wanda zashi canjin ka ba

Jagora /Y/Amshi: Don ka gyara gari yayi kyau,

Dakat tashi gargada tai yawa,

Alhaji Bello sadauki kake,

Di'i Bello uban Amadu.

Za mu tsaya a iya waɗannan ɗiyan waƙa ☝️☝️☝️da muka ciro daga waƙar Injiniya Bello wani mutumen Sakkwato da ya yi aiki a matsayin Injiniyan ayyukka a yankin Yauri wato DE/District Engineer a Turance a cikin shekarun 1970 zuwa shekarun 1980. Wannan waƙa Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo Yauri  (1943-2016) ne yayi masa ita. A maimakon DE /District Engineer sai ya hausantar da kalmar zuwa Di'i.

Duk da yake ba akan wanda aka yiwa waƙar bane zamu tattauna, mun dai yi amfani da ɗiyan waƙar ne domin fitowa da wani batu akan wani bawan Allah da za a san ko shi wanene kuma me ya sa aka alaƙanta shi da waƙar ko mai waƙar.

Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo Yauri yayi amfani da kaifin basirarsa wajen nuna ƙwarewar Injiniya Bello a fagen aiki inda yake cewa "Muhammadu ƙanen Muhammadu Tori, Di'in da yah hi Turai sani".

Ya ƙara da rashin sanin makomar garinsu Yalwa/Yauri ta fannin kikkimta masu titunan mota dake cikin garin saboda an ɗauke shi daga Yauri zuwa Birnin Kabi a lokacin da ya yi masa wannan waƙa.

Shi ne yake cewa "Tashinka Yalwa yai muna zafi, ban san wanda zashi canjin ka ba, don ka gyara gari yayi kyau, dakat tashi gargada tai yawa", wato babu maintainance kenan inji Turawa na titunan Yalwa/Yauri kamar yadda ya saba😁. Kuma bai san ko wanda zai canje shi ya iya aiki kamar yadda ya iya ba.

Sai yayi masa roƙon tsari da kuma wanyewa lafiya " Allah shi yima gambun tsari, Allah sa ka gama lafiya, amin saboda Ɗanhodiyo".

Aikin mayar da titin gwamnatin tarayya da ya taso daga Zaria ta Jihar Kaduna ya zo Funtua /Yankara a Jihar Katsina ya zarce zuwa Tsafe/Gusau /Talata Mafara /Bakura dake Jihar Zamfara zuwa Tureta /Dange/Shuni a Jihar Sakkwato zuwa tagwayen hanyoyi da ake aiwatarwa a halin yanzu shi ne dalilin kawo waɗancan batutuwa ☝️☝️☝️dake cikin wannan waƙa ta Injiniya Bello ta Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo Yauri.

Bawan Allahn da ya kawo wannan aiki na biliyoyan nairori ba Injiniyan tituna bane, shi ma'aikacin kuɗi ne da kishin al'ummarsa yayi masa katutu a zuciya, yayi tsayin gwamin jaki a inda yake aiki har sai da ya tabbatar da wannan buƙata ta samu amincewar hukumomin dake da alhakin aiwatar da ita, aka kuma soma gabatar da aikin kafin ya ajiye aiki.

Ba kamar Di'i Bello uban Amadu  da aka canzawa wajen aiki ba, shi kam ajiye aiki yayi gaba ɗaya. A namu gefen ba zamu tsaya ga abin da Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo Yauri yace ba, zamu yi kira da roƙo ne da babbar murya zuwa ga masu daraja gwamnonin jihohin Kaduna da Katsina da Zamfara da Sokoto da dukan masu muƙamai dake waɗannan jihohi musamman Ministoci da 'yan majalisar dattawa da 'yan majalisar wakilai dama sarakuna da sauran masu faɗa aji su matsa ƙaimi a duk inda ya dace domin tabbatar da kammala wannan aiki a cikin lokaci domin In Shaa Allah za a daɗe al'umma na amfana dashi.

Tsohon ma'ajin kamfanin man fetur na ƙasa wato NNPCL, ɗan asalin Jihar Sokoto ne ya zaƙulo wannan aiki domin  al'ummomin Jihohin Kaduna da Katsina da Zamfara da Sokoto musamman da sauran masu zirga -zirga akan wannan titi su amfana daga kwatarnin/kwatarnen/akushin gwamnatin tarayya kamar yadda ya lura takwarorinsu na sauran sassan Nijeriya na kwankwaɗawa.

Wannan bawan Allah shi ne Alhaji Umaru Ajiya Isa  (Ajiyan Isa)  gundumar Isa Jihar Sokoto. Ɗan Ajiyan Isa Muhammadu Sada ne, shi kuma ɗan Tafarkin Isa Aliyu ne (Tafarki Aliyu ya riƙe sarautar Ajiyan Isa kafin wafatinsa).

Gidansu na daga cikin gidaje 12 da aka kafa garin Isa tare dasu a lokacin mulkin Amirul muminina Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo Tagammadahullah Birahamatihi wanda ya yi mulki daga shekarar 1817-1837. Kenan tun  sarautar Sarkin Gobir na Isa na farko Malam Muhammad Fodiyo ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo.

Tun a wancan lokaci ne ake sarauta guda 3 a gidan nasu wato Tafarki da Magagari da kuma Ajiya ya zuwa yau.

A lokacin mulkin Sarkin Gobir na Isa Malam Umaru ɗan Sarkin Musulmi Aliyu ƙarami ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo ne ya umurci Tafarki Aliyu da ya zayyana sabon wurin zama ga mutanen wani gari da ake kira Magarya zuwa inda suke a halin yanzu wato Bargaja saboda wasu dalilai na zamantakewa, haka kuma aka yi Tafarki Aliyu kakan Alhaji Umaru Ajiya yayi wannan aiki a cikin nasara.

A zamanin mulkin Sarkin Gobir na Isa Muhammadu Na'ammani (yayi sarauta daga 1925-1935) aka dawo da hedikwatar ƙasar Badarawa zuwa garin Shinkafi(a lokacin suna a ƙarƙashin gundumar Isa ne). Tafarkin Isa Aliyu na daga cikin jagororin da suka tsara yanayin garin na Shinkafi domin ya dace da buƙatun zamantakewar al'umma a wancan lokaci.

Da wannan muna iya cewa Ajiya Umaru Sada jikan Tafarki/Ajiya Aliyu duk da ba kamar Di'i /DE Bello uban Amadu da ya karanci wannan aiki na Injiniyanci, yayi amfani da hikimar magabata wajen ƙwato muna aikin mayar da titin Zaria/Funtua /Gusau/Talata Mafara /Dange/Shuni /Sokoto na gwamnatin tarayya zuwa tagwayen hanyoyi ta hanyar amfani da muƙaminsa na Darektan kuɗi /Ma'aji /Ajiya a hukumar kula da harkokin man fetur ta ƙasa NNPCL. Allah SWT ya saka masa da mafificin alherinsa duniya da lahira, amin.

Daga Ajiyan Isa, Alhaji Umaru ya samu amincewar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji (Dr) Muhammad Sa'ad Abubakar CFR mni wanda ya naɗa shi sarautar Ajiyan Sakkwato /Cibiyar Daular Usmaniyya. Ya hau halifar  Marigayi Alhaji Muhammadu Sani Dingyaɗi wanda ya yi sarautar Ajiyan Sakkwato a cikin shekarun 1950 kafin daga bisani ya zama Makaman Sakkwato da kuma Marigayi Alhaji Garba Gummi wanda ya riƙe wannan matsayi na Ajiyan Sakkwato kafin wafatinsa.

Jami'ar Jihar Sakkwato wato Sokoto State University (SSU) ta bashi digirin digirgir na girmamawa saboda abin da ta kira "aiki tuƙuru da sadaukarwasa a ayyukan cigaban al'umma".

Kamar yadda Makaɗa Alh. Sani Aliyu Ɗandawo Yauri ya ce ma Di'i Bello uban Amadu muma mun ce ma Ajiyan mai alfarma Sarkin Musulmi "Allah shiya ma gambun tsari, Allah sa ka gama lafiya, amin saboda Ɗanhodiyo".

A wannan hoto maigirma Alhaji(Dr.) Umaru Ajiya, Ajiyan Isa/Ajiyan mai alfarma Sarkin Musulmi ne. Allah SWT ya ƙara lafiya da nisan kwana mai albarka, amin.

Daga Taskar:

Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.

16/08 /2026.

Post a Comment

0 Comments