𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Mallam Khamis. Allah ya karɓa wa Malam lafiya, Malam, mene ne ne hukuncin macen ta take neman saki a wajen mijinta ba tare da wani dalili ba? Mace ce ake zaman aure, ba cuta ba cutarwa, amma kullum burinta shi ne Mijinta ya sake ta.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Asali dai a shari'ance a na
yin aure ne da nufin sai dai mutuwa ta raba auren ba wai da nufin a rabu ba,
shiyasa idan ya kasance Ma'aurata suna irin zamanda a shari'ance babu wata
cutuwa a tsakaninsu, to baya halatta ga Mace tanemi saki a wajen Mijinta kamar
yadda Mαnzon Allαh (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya faɗa
cewa: DUK MATAR DA TA NEMI A SAKE TA BA TARE WANI DALILI BA. BA ZA TA JI
KAMSHIN ALJANNAH BA. SHI KUMA KAMSHIN ALJANNAH ANA JIN SA KAFIN A TARAR DA ITA
NA TSAWON TAFIYAR SHEKARA ƊARI
BAKWAI.
Sabida Haka Hadisin Yana
Nuni Akan Idan Mace ta Nemi a sake ta ba tare da Wani dalilin na Shari'ah ba.
Ko Kusa da Aljannah ma ba za ta je ba, bare ma ta Shiga Cikin ta. Sabida Haka
Wannan Al'amarin Akwai Hadari, Ya Kamata Mata Sudinga Kiyayewa. Musamman Ma Irin
Matar da Zaka Samu Kowanne irin Hakki Mijinta yana Fitar Mata. Amma Dan
Shedanci Abu Kaɗan Na Kuskure, Wanda Bai Kai
ya Kawo ba, Sai ta Ɗora
Hannu Akai ta Rufe Idanuwan ta, tace Sai Miji ya Sake ta. Ko kuma ta je ta yi
Wa Mijinta Karya a Wajen Iyayenta. Su Kuma Su Ce Sai ya Sake ta. Duk Matar da
ta Tirsasa Mijinta ya sake ta haka Kawai Sai ta Haɗu da
Jarrabawa a Rayuwarta ta Duniya.
Danhaka asali a shari'ance
Mace ba ta da ikon ta nemi saki a wajen Mijinta, to amma idan ya kasance akwai
wani sababi ko wata larura da shari'a ta yarda da su to babu laifi idan Mace
tanemi saki a wajen Mijinta ba tare da ta biya shi wata fansaba, akwai yanayin
ma da yake iya zama wajibi akan Mace ta nemi a sake ta ɗin.
Idan har mace ta takura wa
mijinta akan sai ya sake ta ba tare da Wani dalili ba, sai ya a sake ta ɗin
amma dole za ta biya kuɗin KUL'I. Ma'ana za ta Biya
ka Kuɗin
da zaka sake yin wani Auren. Wannan Shi Ake Cewa KUL'I a Musulunci.
Akwai Hadisi daga Abdullahi
dan Abbas cewar Matar SABIT IBN ƘAIS
ta zo wajen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ta ce. Ya manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) Bana dorawa SABIT Lefin Matsala Akan kula
Addininsa ba, haka akan Iya Mu'amular sa ba. Sai dai ina Tsoron bijire Masa.
(Ma'ana ba za ta Iya Yimasa Biyayya ba. Sabida ba ta son Shi ) Sai manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce da ita "zaki biya shi gonar sa da ya
baki a matsayin gado? Sai ta ce Eh, zan maida masa. sai Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ba shi umarni akan ya sake ta.
Sabida haka kenan, idan irin
wannan ta faru. Wajibi ne zai lisaafa Abinda ya kashe ta Biya shi. Tinda ita ce
ta nemi ya sake ta. Sabida Sau da yawa, matan da aka Yiwa Saki Ukku, suna Samu
Su Auri Wani daban, daga baya Sai su Tayar Musu Da Fitina Akan sai Sun Sake su.
Sabida su sami Dama su Koma Gidan Mazajensu na Baya. Sabida haka Idan Haka ta
Faru, za ta Biya ka duk Abinda ka kashe sai ka sake ta. Sai Ta yi tafiyar ta.
Wata Matar Kuma ta Rabu da
Mijinta Akan wani Abu da bai Kai ya Kawo ba. sai daga baya idan ta yi wani
Sabon Auren. Sai kuma ta ji cewar wannan sabon Mijin Baya Iya gamsar da ita a
shimfida kamar Wancan Na baya ɗin. Anan kuma zai Haɗu da
Sharrin Mace. Sabida ya Dinga ganin Fitina Kala-kala akan sai ya saketa. Don ta
samu ta Koma Gidan Mijinta na Baya. Wasu ma Har waya za ta dinga Yiwa Mijinta
na Baya Akan Ita fa ba ta sami wurin zama ba. Wanda kuma ba Mamaki shi ɗin
ma ba daɗi
bane ya sa ya Rabu da ita ba. Sabida Hankalin ta ya dawo gare shi. Ko kuma
Bayan ta Aureka sai take tunanin Yaranta da ta Bari a gidan Mijinta na Baya. A
haka sai Tace sai ka sake ta. Ka ga Nan ma za ta biya ka duk Abinda ka kashe
mata. Ko ta yi maka wani Auren. Domin zama da ita ba zai yiwu ba.
Sabida haka Mata ku
Kiyayewa. Aure ya Wuce Yadda Muke Kallon sa. Domin Shari'ah ne. Ba Wasan Film
Bane.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.