𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Aassalamu alaikum mln ftn kn lpy Allah ya ke mln lpy da nisan kwana. Mln tambayata kafin zuwan Annabi S A W Annabawa sun gabache shi toh mln shin lkcn Daman Ansaukar Da sallah ko sai da Annabi S A W yazo Aka saukar masa da sallah Kafin lkc Ana yin sallah koh saida bayyanar Annabi S A W Aka fr yin sallah
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Atakaice ba Annabi
Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) ne ya fara kawo sallah ba. Annabawa da
suka gabace shi ma sun kasance suna yin ibada da sallah bisa umarnin Allah, kodayake
yadda ake yin sallarsu da lokutanta ba lallai su kasance daidai da tsarin
sallolinmu biyar ba. Misali, Allah Ya ambaci Annabi Ibrahim عليه
السلام
yana addu’a cewa:
رَبِّ اجْعَلْنِي مُقِيمَ الصَّلَاةِ وَمِن ذُرِّيَّتِي ۖ
رَبَّنَا وَتَقَبَّلْ دُعَاءِ
Ya Ubangijina, Ka
sanya ni mai tsayar da sallah, da kuma daga zuriyata.Ya Ubangijinmu Kuma ka karɓi addu'ata."
(Suratul Ibrahim ayata 40).
Haka kuma Allah Ya ce
wa Annabi Musa (عليه السلام):
إِنَّنِي أَنَا اللَّهُ لَا إِلَٰهَ إِلَّا أَنَا فَاعْبُدْنِي
وَأَقِمِ الصَّلَاةَ لِذِكْرِي
Lalle ni, Ni ne Allah,
babu abin bautawa da gaskiya face Ni, sai ka bauta mini, kuma ka tsai da salla
domin tuna Ni (Suratul Taha ayata 14).
Haka Annabi Isma’il عليه
السلام
da sauran annabawa sun kasance suna umartar iyalansu da sallah.
Sbda haka, sallah ta
kasance tun kafin zuwan Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam), ba a fara
yin sallah ne sai bayan bayyanarsa ba. Abin da ya kebanta da al’ummar Annabi
Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) shi ne cewa a daren Mi’iraji Allah Ya wajabta
salloli biyar na yini da dare a kan wannan al’umma, bayan da aka fara wajabta
su hamsin sannan aka rage su zuwa biyar, amma lada ta kasance kamar hamsin. Don
haka, idan aka ce “yaushe aka saukar da sallah?” sai a bambanta: asalin sallah
da ibadarta sun kasance tun zamanin annabawa kafin Annabi Muhammad (Sallallahu
Alaihi Wasallam), amma sallolin farilla guda biyar da tsarin da muka sani a yau
Asuba, Azahar, La’asar, Magariba da Isha’i an wajabta su ga al’ummar Muhammad
(Sallallahu Alaihi Wasallam) a daren Isra’i da Mi’iraji kafin hijira.
WALLAHU A’ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.