Ticker

6/recent/ticker-posts

Nason Kirari a Wakokin Baka: Nazari a Cikin Wakokin Alhaji Musa Danba’u Gidan Buwai

Citation: Malami, U. T. (2026). “Nason Kirari a Waƙoƙin Baka: Nazari a cikin Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanbau Gidan Buwai In Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies, Vol. 04, No. 01, Pp. 49 – 56. www.doi.org/10.36349/djhs.2026.v04n01.007.

NASON KIRARI A WAƘOƘIN BAKA: NAZARI A CIKIN WAƘOƘIN ALHAJI MUSA ƊANBAU GIDAN BUWAI

Na

Malami, Umar Torankawa
Sashen Gudanar da Shirye-shirye,
Rima Television Sokoto

Tsakure:

Sunan wannan maƙala shi ne nason kirari a waƙoƙin baka: nazari a cikin waƙoƙin Alhaji Musa Danba'u Gidan Buwai. Manufar maƙalar ita ce nazarin waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanbau Gidan Buwai tare da fito wa da baiwa da hikimomi da zalaƙar harshe da Allah ya ba shi wadda yake amfani da su wajen sarrafa kirari a cikin waƙoƙinsa. An gudanar da binciken ta hanyoyi daban-daban, waɗanda suka haɗa da tattaunawa da abokan hulɗarsa, musamman waɗanda suke taimaka masa, da kuma duba littattafai da kundin waƙoƙi. An kuma ziyarci gidajen rediyo da talabijin kamar Rima Radio, Rima TV, da NTA Sokoto don tattara bayanai. An dora binciken ne bisa ga littafin Farfesa Sa'idu Muhammad Gusau mai taken Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Sakamakon bincike ya nuna akwai Kirari mai yawa a cikin waƙoƙin nasa. 

Gabatarwa

An tsara wannan maƙala ne da niyyar kallon yadda makaɗa da mawaƙa suke sarrafa harshe cikin hikima da zalaƙa don su kambama ko kwanzarta uwayen gidansu ta nuna  fifiko a tsakanin  su da abokan adawa ko kuma nakasa wa ga abokan hamayya. Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai ɗaya ne daga cikin shahararrun mawaƙan baka a ƙasar Hausa, waɗanda Allah ya ba hikima da fasaha, da azanci wajen gudanar da waƙa. An kalli wasu daga cikin waƙoƙinsa, kuma aka yi ƙoƙari aka fito da kirari a ciki. Kamar kowane nazari akan sami tsari na musamman da ya kamata a gabatar kafin gudanar da shi, wannan maƙala  an dubi waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u ta hanyar nazarin kirarin da suke ɗauke da su da kuma kafa misalai daga ɗiyan waƙoƙinsa tare da yin sharhi dai-dai gwargwado. An kasa wannan aikin maƙala zuwa matakai guda huɗu kamar haka:- Mataki na farko kuwa shi ne gabatar wa ga aikin gaba ɗaya sai mataki na biyu inda aka yi waiwaye akan yadda masana da manazarta suke kai komo waje tattara bayani game da ma’nar kirari da kashe-kashensa. Mataki na uku ya ƙunshi bayanai a kan kirari da yadda Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai ke sarrafa shi a cikin waƙoƙinsa tare da kawo misalai daga cikin wasu ɗiyan waƙoƙinsa da kuma yin sharhi dai-dai gwagwado. Mataki na huɗu kuwa shi ne kammalawa.

Kirari

Kirari na nufin wasu zaɓaɓɓun kalmomi da ake furtawa a tsare don zuga ko kambamawa. (CNHN: 2006:466). A ra'ayin Gusau (1984:1) ya bayyana kirari da cewa "wata tsararriyar magana ce, 'yar doguwa ta hikima, da akan shirya musamman don kambama mutum ko wani abu, ko kuma mutum ya yi don kambama kansa da kansa". Shi kuwa Umar (1987:3) ya ce "kirari wasu kalmomi ne na kambamawa ko cicciɓawa da ake yi wa wani ko mutum ko shi yake yi wa kansa da ke zuwa ta sigar siffanta mutum ko wani kan shahararren ƙarfi ko alfarma ko daraja. Ya ƙara da zayyano abubuwan da ake kirari da su waɗanda suka haɗa da giwa da zaki ko aljani da gobara da baƙin kumurci da iyaye da sauransu". Har wa yau "kirari na nufin waɗansu irin maganganu ne da ake yi wa sarakuna ko muhimman mutane da take bayyana halayensu da kuma kamanninsu ta hanyar kambamawa". (Kafin Hausa, 1981:2). "Kirari wasu maganganu ne na zuga da kambamawa da suka shafi halaye da akan tsara cikin hikima da balagar harshe".(Garba 1998:21). Haka kuma "kirari wata tsararriyar maganar hikima ce da akan shirya ta don a yabi wani mutum ko a bayyana halayyar wani abu ko yanayinsa ko siffarsa". (Galadanci da wasu, 1993)

Ta la'akari da waɗannan ra'ayoyi na masana da suka gabata a kan wannan nau'in azanci za a iya cewa, kirari wasu maganganu ne na hikima da fasahar harshe da akan tsara don a yabi wani mutum ko a bayyana halayyar wani abu ko yanayinsa ko siffarsa ta hanyar zuga ko kambamawa ko cicciɓawa da nufin ɗaukaka darajarsa ko ƙimarsa ko ƙarfinsa ta nuna ƙauna ko ƙiyayya.

Wannan nau'in na daga cikin zantukan azanci da makaɗa ke amfani da shi don su zuga ko kambama wani ko koɗa kansu da kansu don nuna bajinta da faranta ran ubangidansu ko sanya shi yin kyautar da bai tashi yi ba ko don a razana abokan gaba. Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai na daga cikin makaɗan baka na Hausa da suke amfani da wannan nau'in kamar yadda misalai za su nuna haka daga cikin wasu waƙoƙinsa.

Kirari Mai Nasaba

Wannan kirari na nasaba ya danganci kirari da mawaƙa suke yi wa al'umma musamman uwayen gidansu ta dangantasu da kakanninsu ko iyayensu ko matansu ko 'ya'yansu ko iyayen gidansu da kuma aminansu da sauransu. Anan za muga yadda Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai ya yi amfani da kirarin nasaba a waƙoƙinsa kamar haka. A cikin waƙarsa ta Salihu Barade mai taken "Salihu baa jan ka ran yaƙi"

Gindin waƙa: Yara ku tashi za ni Wamakko,

'Yan’amshi: Don mu ishe Barade garkarsa,

  Salihu ba a jan ka ran yaƙi,

Jagora:  Kar ka sake Barade Wamakko,

  Kai ka halin Barade Jaɓɓi,

  Ka yi halin Ruwa Mai Sandare,

  Ka yi halin Barade Aliyu,

'Yan Amshi: Kai ka halin Barade Gainako. +2

Jagora:  Sarakunan ga da ni lissahwa,

  Dud martabarsu tana hannunka,

'Yan Amshi: Kai ka hwaɗi a yarda ko dole.

(Alhaji Musa Ɗanbau Gidan Buwai: waƙar "Salihu ba a jan ka ran yaƙi”)

A wannan ɗan waƙar Musa Ɗanba'u ya yi amfani da azancin magana na kirari da ya danganci nasaba inda ya kawo bayani mai nuna cewa gwarzonsa shi ne Barade, kuma ɗan Barade Jaɓɓi kuma jikan Barade Sandare da Barade Aliyu da kuma Barade Ganako. Duk wata martaba da daraja da nagarta da suke da ita yanzu, shi Barade Salihu shi ne yake riƙe da ita. Ya ƙara kambama shi ta nuna a yanzu ba wani mai faɗa aji kamarsa tun da shi ka riƙon Wamakko.

Haka kuma a waƙar Mukhtari Shehu Shagari mai take "Ɗan Marafa jikan Basharu" a wannan ɗan waƙa Alhaji Musa Ɗanba'u ya zo da misalin kirarin nasaba kamar haka:-

Jagora:  Ɗan Marafa jikan Basharu,

  Baba uban Abdullahi,

  Lahiya namijin zaune.

  Jarumi na Obasanjo,

'Yan Amshi: Na Atiku Turaki,

  Maza suna shakka ja nai.

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai: waƙar "Ɗan Marafa Jikan Basharu")

Wannan ɗan waƙar ya zo da kirarin nasaba ne ta danganta gwarzonsa da cewa shi ne jikan Basharu kuma uban Abdullahi. Haka kuma a layi na huɗu da na biyar ya yi amfani da kirarin nasaba amma ta haujin iyayen gida da aminai, inda ya ambaci gwarzonsa da dangatashi da iyayen gidansa wato shugaban ƙasa Obasanjo da Mataimakinsa Alhaji Atiku ta nuna zamantakewarsu a matsayinsa na minista a cikin gwamnati, wato ya yi masa kirari da cewa shi gwarzo ne maza suna saunarsa don ba ya ɗaukar raini.

Haka ma a wannan ɗan waƙar ya yi masa kirarin nasaba ta danganta shi da matansa kamar haka

Jagora:  Mijin Salamatu dottijo,

  Mijin Maryam mai bantsoro,

  Mijin Kuluwa 'yar Shehu,

  Mijin Sa'a mai sa'a,

'Yan Amshi: Ba a kai maka ganganci,

  Kuma bai ɗaukar wasa.

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai: waƙar "Ɗan Marafa Jikan Basharu")

A wannan ɗan waƙar Makaɗin ya bayyana nasabar zamantakewa ta miji da mata, inda ya bayyana dangantakar gwarzonsa da matansa ta yi masa kirari da ambaton sunayensu wato mijin Salamatu da Maryam da Kuluwa da kuma Sa'a.

Ita ma waƙar Yusuf Suleman mai taken: "Isuhun Sulemanu Minista" Makaɗin ya yi amfani da kirarin nasaba wajen fitowa da tarihin gwaninsa don ya nuna wa abokan adawa cewa fa ubangidansa mutunne sananne kuma mai asali mai kyau da kuma ɗaukaka a idon al'umma. Ga abin da ya ce:

Jagora:  Bari dai in ta da gwanina ni,

  Ina gwanin wani ga nawwa,

  Isuhu na Shehu na Tambari,

  Arzukinka ya fasa dutsi,

'Yan Amshi: Ka ƙara hattara Isuhu na Sada.

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai: waƙar "Isuhun Sulemanu Minista")

Wannan ɗan waƙa ya zo da kirarin nasaba inda mawaƙin ya yi kirari ga gwaninsa da danganta shi da yayanninsa wato ya nuna cewa gwarzonsa ƙane ne ga Shehu Suleman da kuma Tambari Suleman. A nan da Shehu da Tambari duk yayanni ne ga gwaninsa. Haka ma a layi na biyar ya ƙara danganta shi da Sarkin Musulmi Sada don nuna zumunci da soyayya da ke tsakanin gwaninsa da mai alfarma Sarkin Musulmi na ashirin, wato  Muhammad Sa'adu Abubakar na uku da ƙara nuna cewa shi gwarzonsa yana daga cikin Magada Sarautar.  

A waƙar Shugaban ƙasar Nijar Tanja mai taken "Shugaban Ƙasar Mai Sulken Yaƙi." Ɗanba'u ya zo da irin wannan azancin magana na kirarin nasaba kamar yadda zaa gan shi a cikin wannan ɗan waƙa:-

Jagora:  Dogo ɗan Lamiɗo,

'Yan Amshi: Gaba jikan Lamiɗo,

Jagora:  Ga ɗan HadiTanja,

'Yan Amshi: Baban Hadi Mamman,

Jagora:  Na Laraba mijin Faɗima,

  Giwa sha masu,

'Yan Amshi: Mai maganin walaƙanci,

  Tanja ɗan Mamman.

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwa: waƙar "Shugaban Ƙasar Mai Sulken Yaƙi")

A cikin wannan ɗan waƙar Alhaji Musa Ɗanba'u ya yi amfani da nau'in azancin magana na kirarin nasaba inda ya danganta Tanja da kakanninsa da uwayensa waɗanda suka haɗa da babansa Lamiɗo da kakansa Lamiɗo da kuma mahaifiyarsa Hadi, duk don nuna asalinsa ta danganta shi da su. Haka kuma a layi na uku ya ambaci nasabar ta danganta shi da 'ya'yansa da matansa "Na Laraba mijin Faɗima"tare da siffanta shi da wasu kalmomi na kambamawa da cicciɓawa kamar dogo da giwa.

Haka kuma Ɗanba'u ya zo da irin wannan kirari na nasaba a waƙar Sarkin Yamman Sakkwato Aliyu Magatakar daWamakko mai taken "Ƙi Sake Bajinin Gwarzon Maza Ali Sarkin Yamman Sakkwato".

Jagora:  Kai bari dai in tada gwanina,

  Bari dai in wasa ubana,

  Ɗan Barade jikan Umar,

  Baba gizago baka da sabo,

'Yan Amshi: Mai sassaƙa ya tsare hannunsa,

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai: waƙar "Ƙi sake bajinin gwarzon maza, Ali Sarkin yamman Sakkwato")

A wannan ɗan waƙa Musa Ɗanba'u ya yi amfani da dabarar azancin kirarin nasaba inda ya danganta gwarzonsa Aliyu Magatakarda Wamkko da cewa ɗa ne ga Barade Jaɓɓi shi kuwa Barade Jaɓɓi ɗa ne ga Baraden Wamakko Umaru, wato ya nuna nasabar gwarzonsa fitowa da alaƙanta shi da Ubansa da kakansa cewa duk sun yi Baraden Wamakko, musamman wannan nasaba ta fito ne a layi na uku.            

A cikin waƙa Mai taken "Janjunan Gidan Buwai, Arna Ba Su Ja Da Kai" Ɗanba'u ya yi amfani da irin wannan azanci na kirarin nasaba a lokacin da yake zuga ubangidansa da ya yunƙura ya karɓi Raɓa. Ga abin da ya ce

Jagora:  Ga maganar da niy yi ma,

  Janjunan Gidan Buwai,

  Jikan Audu Bayero,

  Shin wai mi ka kai da Rara,

  Kimtsa ka amshe Raɓa,

'Yan Amshi: Komai a kai ayi.

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai: waƙar "Janjunan Gidan Buwai, Arna Ba Su Ja Da Kai")

Wannan kirarin ya zo ne a layi na uku na ɗan waƙar inda ya zo da nasabar ta nuna cewa ubangidansa jika ne ga Audu Bayero. Wato Sarkin Raɓa da ya gabaci wanda ke kan karaga, shi kuwa Audu Bayero jika ne ga Mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo.

Kirari Mai Dangantawa

Wannan wani nau'in kirari ne da mawaƙi yake yi wa iyayen gidansa ko waɗanda suke yi wa waƙa don su samu fada ko don su yi musu wata kyauta ta musamman. Misali Alhaji Musa Ɗanba'u cikin waƙar Sarkin Musulmi Macciɗo mai taken"Gwauron Giwa Jikan Hasan Ɗan Amadu", ya yi masa kirari ta siffanta shi da waɗansu kalmomi masu nuna kwarjini ga idon jama'a kamar haka:-

Jagora:  Tauraron duniya

  Na Maisango

'Yan Amshi: Baba Zakin  na Mu'azu

  Hasken musulmin duniya

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai: waƙar "Gwauron Giwa, Jikan Hasan, Ɗan Amadu")

Wannan ɗan waƙa Ɗanba'u ya zo da kirarin wani inda ya yi wa gwarzonsa kirari ta fitowa da kalmomi masu nuna kwarjini da ƙarfi a tsakanin jama'a, wato nuna ɗaukaka kan abokan adawa. A layi na farko ya yi amfani da kalma mai nuna cewa gwarzosa kwarjininsa da farinjininsa ya game duniya kamar yadda taurari suke bice sama da haskake duniya. Haka ma a layi na uku ya kira shi da zaki don ya fayyace irin ƙarfinsa a tsakanin jama'a da 'yan sarki kamar yadda zaki yake taƙama ta nuna ƙarfi da kwajini adawa. A layi na huɗu ya ambace shi da hasken musulmin duniya wato alheri ne ga musulmin duniya, kuma ya zo da sigar kambamawa a wannan kirari domin nuna irin yadda ubangidansa yake yin ƙwazo wajen hidima ga al'umar musulmi na ganin adinnin musuluci ya sami ɗaukaka.    

A waƙar Attahiru Bafarawa mai taken "Bai San Tsoro Ba, Bafarawa Attahiru" Musa Ɗanba'u ya yi amfani da irin wannan kirarin a cikin waƙar kamar haka:-

Jagora:  Ga dai mulki gare shi,

  Ga nera ta tsaya,

  Ga jama'a nan gare shi,

  Ga ilimi ya yi yawa,

  Turanci,

'Yan Amshi: Ko Amerikan gogawa su kai.

Jagora:  Mijin Alhajiya Amina,

  Angon Murja,

  Uban Sagiru da Babangida,x2

'Yan Amshi: Shelto mai maganin ƙuda ko da sun yawa.

(Musa Ɗanba'u: waƙar "Bai San Tsoro Ba, Bafarawa Attahiru")

Wannan ɗan waƙar Ɗanba'u ya yi kirari ga gwarzonsa Alhaji Attahiru Bafarawa ta kambama shi da cewa shi ƙwararre ne wajen gudanar da mulki, haka kuma shi attajiri ne da ke tallafa wa jama'a don haka al'umma su ke ƙwaunarsa. Har wa yau makaɗin ya ci gaba da yi masa kirari ta danganta shi da matansa da kuma ‘ya’yansa da kuma mallakar dukiya da Allah ya hore masa, ga kuma jama'a da suke ƙaunarsa. Ya cigaba da yi masa kirari inda ya kambama shi ta nuna ƙwarewa a fannin ilimi da iya Turanci inda ya nuna ko daga Amerika ka fito albarka.

Haka kuma a ɗan waƙar da yake bi masa Ɗanba'u ya yi masa kirari ta siffanta shi da Shelto wato wani abu da ke maganin ƙuda komai yawansu da zaran an fesa shi za a ga sun mutu, to haka gwarzonsa yakan watse taron magabta komi yawansu.       

Ita ma waƙar Matawallen Sakkwato mai taken "Ɗan Waziri Ka Ƙara Shirawa, Aminu Yau Kai Am Matawalle", tana da irin wannan kirari, inda Ɗanba'u ya yi amfani da kalmomin siffantawa don ya yi kirari ga ɗaya daga cikin aminan Matawalle da suka yi masa kyauta kamar haka;     

Jagora:  Ga dogo mai halin kyauta, x2

  Kyautarka ta fi jarin yaro,

  Rai ya daɗe ma Kabiru Marahwa,

  Ɗan Uban ƙasar Alkammu,

  Kabiru rini kere itace.

(Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai: waƙar "Ɗan Waziri ka ƙara shirawa")

A wannan ɗan waƙa Musa Ɗanba'u ya yi wa gwarzonsa kiarari ta amfani da kalmomin siffantawa, inda daga farko ya ambace shi da dogo. A layi na biyar kuwa ya kira shi da rimi kere itace duk dai yana ƙoƙarin nuna cewa gwarzonsa kamar yadda rimi ke kere itace saboda tsayinsa haka ubangidansa Kabiru Marafa a duk inda ya shiga za a gan shi wato kamar yadda yake da tsawo haka kyautarsa da alherinsa yake. Ya ƙara da nuna irin yadda yake kyauta tamkar ya baka jari ne saboda yawanta, "kyautar ka ta fi jarin yaro". Haka kuma a wani wurin a cikin wannan ɗan waƙa mawaƙin ya yi masa kirarin nasaba ta nuna cewa ɗa ne ga uban ƙasar Akamu wato Marafan Alkamu mahaifinsa ne don haka gwazonsa Ɗangaladima ne a masarautar Alkamu ko a ce Yarima.

Kirarin Kwatantawa

Makaɗan Hausa na amfani da wannan dabara ta kirari ta amfani da salon kinaya ko alamci musamman lokacin da suke kambama gwarazansu, inda suke siffanta su da dabbobi ko ma wata halitta ta Ubangiji don su bayyana su ta yadda za su nuna fifiko tsakaninsu da abokan hamayya ko magabta. Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai yana amfani da wannan dabara ta kirarin kwatantawa a cikin waƙoƙinsa kamar yadda misalai za su nuna.

Wannan waƙa ta Alhaji Yusuf Suleman mai taken "Na Bello Ba A Ja Nai A Ci Riba, Isuhun Sulemanu Minista".Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai ya yi amfani da wannan azancin magana na kirari kamar haka:-     

Yaro:  Dutsin fashin tama jikan Ali,

  Gamji matattarar namun daji,

  Kowaj ji yunwa ya gangaro,

  Ya ɗauki abinci ya kai gida,

'Yan Amshi: Kowag ganai yana gyara gidansu.

(Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai: Waƙar "Na Bello Ba A Ja Nai A Ci Riba")

A wannan ɗan waƙar ya zo da kirarin kwatantawa ne ta amfani da salon jinsantarwa mai nuna abuntarwa, inda a layi na farko da na biyu ya zo da kalmomin abuntarwa ta ambatonsa da dutsin fashin tama wato ya nuna irin ƙarfin da ubangidansa yake da kamar yadda dutsin fashin tama yake a tsakanin duwatsu haka ubangidansa yake. Don haka maƙiya da mahassada su yi haƙuri ba su iyawa. A layi na biyu kuwa ya faɗi irin alheri da yawan kyauta da gwarzonsa ke yi ta yi masa kinaya da inuwar gamji wadda ke da faɗi da yalwa. Ta nuna hakan gwarzonsa yake biya wa al'umma buƙatunsu na yau da kullum, gwargwadon hali. 

Ita ma waƙar PDP mai taken " PDP Hasken Najeriya, Fati Mai Ƙarhi Da Martaba". Musa Ɗanba'u ya yi amfani da wannan kirari na kwatantawa kamar haka:-            

Jagora:   Hajji Modi na Yabo a gaishe ka,

 Zaki mai ƙarhin mutum dubu,

 Ka gama da 'yan kwakwar baya,

 Yanzu kwakwa ba ta da tasiri,

'Yan Amshi: Sai dai su yi bammi su sha giya.

(Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai: Waƙar "PDP Hasken Najeriya")

Wannan ɗan waƙa yana ɗauke da azancin magana a layi na biyu inda mawaƙin ya ambaci gwarzonsa ta siffanta shi da Zaki,wato ya yi masa kinaya ta nuna yadda Zaki yake da ƙarfi da kwarjini a tsakanin dabbobi haka ubangidansa yake a tsakanin jama'a kuma ya yi amfani da ƙarfin ya murƙushe abokan gaba ko adawa.

Haka ma a waƙar Alu Magatakarda Wamakko mai taken "Aliyu Zaɓaɓɓen Gwamna", a nan ma Ɗanba'u ya zo da irin wannan kirarin a ɗan waƙar da yake tafe kamar haka:

Jagora:  Tauraron gabas mijin Arziki,

 Gaishe ka na Murja,

 Ɗan Garba Farin wata Ali,

'YanAmshi: Ka iske mutanen birni,

  Har da mutanen ƙauyuka.

(Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai: "Aliyu Zaɓaɓɓen Gwamna")

Kirarin kwatantawa ya zo ne a farkon layi na ɗaya da kuma tsakiyar layi na biyu a wannan waƙa, inda mawaƙin ya yi amfani da salon kinaya wajen yin kirari ga gwarzonsa ta fuskar kiran sa tauraro, wato yadda tauraro yake haskewa haka ubangidansa yake. A layi na uku kuwa ya yi amfani da kalmar farin wata don nuna irin yadda farin wata ya zame game duniya, haka wanda ya yi wa waƙa yake. Haka shi ma ubagidansa alheri da kyautarsa ta game jama'a na birni da ƙauyuka.

Kirarin Koɗa Kai

A wannan kirari mutum ko mawaƙi kan yi wa kansa kirari don ya koɗa kansa ko kuma ya nuna fifikonsa da sauran abokan kiɗansa ko waƙa ko ma don firgita abokan gaba ya nuna ƙwarewarsa ta fi tasu da makamantan haka.  Alhaji Musa Ɗanba'u ya zo da irin wannan dabara ta azancin magana na koɗa kai a waɗansu ɗiyan waƙoƙinsa kamar haka.

A waƙar Sarkin Musulmi Macciɗo mai taken "Gwauron Giwa, Jikan Hasan Ɗan Amadu", Ɗanba'u ya zo da irin wannan dabara ta azancin magana na yi wa kansa kirari kamar haka:- 

Yaro:  Ɗanba'u mai kiɗa,

  Mamaki ɗai ni kai,

  Mamakin duniya,

  Ni ko duniya,

  Ina jin tsoron ki,

  Ka ga harakar 'yan Adam,

  Tana ban mamaki,

  Wasu sun ce,

  An hana ni waƙa nan Sakkwato,

  Ƙarya ƙaryar ƙasa,

  Zancen banza,

  Don ƙarya ba magana ba,

  Wasu sun ce,

  An hana ni waƙa,

  Nan Sakkwato,

  Ni ko na gaya masu,

  Kura ko bata ci,

  Kare na saunan ta,

  Yanzu ko da ba ni waƙa,

  Ƙafata ta tsaya,

  Tun da duk Nijeriya,

  Wani mai kyauta da naira,

  Ƙasar nan na sani,

  Wani mai kyauta da mota,

  Ƙasar nan na sani,

  Ko ba Nijeriya ba,

  Musa in tsallake,

  In tahi Nijar,

  Mu iskikke,

  Tanja Mammadu.

(Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai: Waƙar Gwauron Giwa, Jikan Hasan Ɗan Amadu")

A wannan ɗan waƙa kirarin koɗa kai ya fito ne tun daga layi na goma sha bakwai zuwa na ƙarshe inda ya nuna cewa ga yanzu fa ya wuce a yi mai raini don ya kai duk inda mawaƙi, ka son kaiwa ta amfani da karin magana mai nuni ga habaici don ya ƙara nunawa magabta da masu kushe, da cewa "Kura ko ba ta ci, kare na saunan ta" wato ga yanzu sai dai su yi haƙuri don na gaba ya yi gaba na baya ko sai labari, inda ya siffanta kansa da kura su ko magaba da kare ya siffansu wato akwai tazara mai yawa a tsakaninsu,sai su yi haƙuri da ikon Allah. Har wa yau dai ya kara nuna fifikonsa da su a layi na sha tara zuwa ƙarshen ɗan waƙar da cewa “'Yanzu ko da ba ni waƙa, ƙafata ta tsaya”.  Wato ya riga ya kai duk inda makaɗi yake buƙatar kaiwa don nuna gwaninta da samun karɓuwa ga jama’a na ciki da wajen ƙasar nan.

A waƙar Macciɗo Yarin Gandi, Ɗanba'u ya yi amfani da wannan dabara ta kirarin kai a wani ɗan waƙa kamar haka:-

Jagora:  A ni na sha wahala a Raɓa,

  Haji Ɗanba'u mai waƙa,

  Ni na sha wahala Raɓa,

  Ga siyasa wadda ta zarce,

  Mamaki ya kama ni,

  Ana yi man harakar ganganci,

  Tun da ƙarhina bai zo ba,

  Ɗanba'u ba zai magana ba,

  To yanzu kan ƙarhina ya kai,

  Mai auren matar mai waƙa,

  Tun da siyasa tai muku fancal,

  Don Allah ka sako akuyar nan,

 

'Yan Amshi: Ta sha ruwanta ta koma garge.

(Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai: Waƙar “Uban Aminu Sadaukin Sarki”)

A wannnan ɗan waƙar Ɗanba'u ya zo da kirarin koɗa kai, inda a layi na tara ya nuna cewa yanzu kan ƙarfinsa ya kai, don haka ba zai aminta da reni ba da harkar ganganci da ake masa a baya ba.  Ya yi amfani da salon dabbantarwa don ƙara fitowa da kirarin a layi na goma sha biyu inda ya yi amfani da akuya mai makon ya ambaci sunan matarsa da wani ɗan siyasa ke aure sai ya yi dabbantarwa da cewa to yanzu kan ƙarfinai ya kai kuma ga shi siyasarsu ta fanɗi wato tai musu facal, fancal na nufin harakarsu ta siyasa duk ta kwaɓe ba su da wata madogara. To a nan ne mawaƙin ya yi dabbantarwa da cewa 'Don Allah ka sako akuyar nan, ta sha ruwanta ta koma garge”,wato a sako masa matarsa da yake aure don ga yanzu mijin ba shi da ƙarfin riƙe ta, sanadiyar faɗuwa zaɓe da ya yi.

Kammalawa

A wannan takarda an fahinci yadda Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai ya yi amfani da dabaru da hikimomi daban-daban ya saka kirari a cikin waƙoƙinsa, mabambanta da ya yi saboda isar da saƙon da ke ciki. A takardar an ga yadda kirari ke ƙawata waƙoƙin baka na Hausa don yin armashi wajen rerawa da kuma samar da nishaɗi ga masu sauraro ba tare da gajiyawa ba ko ƙosawa. An kuma ga yadda yake nuna yabo da kambama uwayen gidansa ko kushewa da nakasa abokan adawar uwayen gidansu.

Manazarta

CNHN, (2006) Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria: Ahmadu Bello University Press.

Garba, M. (1998). "Azancin Magana A Waƙoƙin Makaɗan Baka". Kundin Digiri Na Biyu. Kano: Jami'ar Bayero

Galadanci, M. K. M. da wasu (1993), Hausa Don Ƙananan Makarantun Sakandare Longman Nigeria Plc.

Gusau S. M. (1984) ‘Nazarin Zaɓaɓɓun Waƙoƙin Baka na Hausa’. Cyclostyled Edition.

Gusau, S.M. (2002). Sarkin Taushi Salihu Jankiɗi. Nazari da Ratayen Wasu Waƙoƙinsa Baraka Publishers Limited, Kaduna.

Gusau, S.M. (2023). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S.M. (2015). Mazhabobin Ra'i da Tarke A Adabi Da Al'adu Na Hausa. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S.M. (2016). Makaɗa Da Mawaƙan Hausa, Littafi Na Biyu.Kano: Century Research and Publishing Limited.

Umar, M.B. (1987). Dangantakar Aadabin Baka da Al'adun Gargajiya.Kano, Nigeria: Trumph Publishing Company.

Torankawa, M.U (2006). "Adon Harshe A Waƙoƙin Sarauta Uku Na Makaɗa Rabo Ango Yabo" Kundin Difilomar gaba da Digirin Farko (PGDHS) A Fannin Hausa. Kano: Jami'ar Bayero.

Torankawa, M.U (2025) “Nazarin Azanci A cikin Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai” Kundin Digiri Na Biyu. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Danfodiyo.

Yahya, A.B. (2016). Salo Asirin Waƙa. Sokoto: Guaranty Printers.

Dundaye

Post a Comment

0 Comments