Ticker

6/recent/ticker-posts

Na Yi Mafarki Kanwata Da Ta Rasu Ta Ce Na Kusa Zuwa Garinsu

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum mlm ina yini Dftn kn lfy Allah yasa hk amin

Mlm ina so a taimaka mim da addua wlh mlm ina yawan yin mugayen mafarkai, sannan na yi wani mafarki daya tadamin hankali sosai nakasa samun natsuwa kwata kwata shi ne kamar haka naga kawanta datarasu taxo gidan mahaifiyata nikuma sai muka hadu da ita a kofar gidan lokacin za ta shiga sai na yi murnar ganinta a yana yi mai kyau saina ce daman kinanan sai ta ce eh yanzu ma gurin mahaifiyarmu na zo sai na ce mushigato amma mekika kawomim sai ta ce babu saidai naji an ce kema kinkusa zuwa garinmu saina ce a a ni ba zan zo garinku ba sai ta ce ai babu komai nima karama ai naje shi ne shiga gurin mahaifiyartamu, shi ne fa tunda na farka nakasa samun natsuwa mlm, sainajika nagode Allah yasaka da alkhairi

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh.

Mafarkin da kika yi cewa ga mamaci (kanwarki) tazo gidan ku ta ce kin kusa zuwa garinsu, yana sanya tsoro amma ba ya nufin mutuwar ki ta kusa ba. Wannan mafarki yana iya zuwa ne saboda tsananin tunani, ko damuwa, ko kuma saboda kin dade kina kewar marigayiyar a zuciyar ki ko kuma jan hankali zuwa ga tuba da tsoron Allah.

Abin da za ki riƙe don samun natsuwa yanzu shi ne; Kar ki sa a ranki cewa mutuwa za ki yi, domin rayuwa tana hannun Allah ne Shi kaɗai. Ki yawaita istigifari da neman tsarin Allah daga shaiɗan da mugayen mafarki. Kafin ki kwanta barci, ki rika karanta Ayatul Kursiyyi da suratul Ikhlas, Falak, da Nas, sannan ki tofa a jikinki. Idan kin tashi da mummunan mafarki, ki tofa a gefen hagu sau uku, ki nemi tsarin Allah daga Shaiɗan, sannan ki juya gefe ɗaya. Ki yi alwala kafin ki kwanta kuma ki kwanta a gefen dama. Sannan kiyi Sadaka, Sadaka tana kore bala'i kuma tana kawo kwanciyar hankali a zuciya. Ki Tuba da yawan Istigifari da yawan salati ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam).

Kada ki damu da wannan mafarki, domin ba zai cutar da ke ba, kuma ba yana nufin mutuwa ko wata mummunan abu. Mafarkin yana nuna tsoron rashin kanwarki da kike so, da kuma tunani mai tsanani a zuciyarki game da marigayiyar kanwar da ta rasu.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam   

Post a Comment

0 Comments